← Book details Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 88 OF 93

Sashe 88

Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*MAGANIN GYARAN NONO MAI TADA KOMADAR NONO DA DUK WATA TAMOWA TA* *JIKINKI NONUWA ZASU CIKO SOSAI ANMA BANCE ZASU TSAYABA WANNAN MAGANI ANGWADA ANDACE HANZARTA KI MALLAKI NAKI YAR UWA 8K* *TAREDA MAGANIN CIRE TUMBI DUK INDA KIKAI KAMAR KIN KUSA HAIHUWA AITA TAMBAYAR KI WATA NAWA IDAN KINSHIGA MATE KIZAMA KAMAR BABARSU DAN ALLAH KIZO KIJARABA 7k *INA AIKAYA KOWANI GARI DA YARDAR ALLAH INBAKI SHIRYA BA KIBARI KI SHIRYA SAI KUNZO NAGODE KAYAN* *AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA* *KI TUNTUBENI A WANNAN LAYIN* *08162859027*Wani lafiyayyen mari Abbu ya sauke Abraham a fuska yana huci tare da cewa "Who the hell do you think you are? Akan idanuna kake cewa a barka kaje ka sumbaci ƴar cikina? Sbd ka tabbatar mana kai mahaukaci ne baka san addini ba ko? Yanzu kai ko musulunci ne How do you think I will welcome you to marry my daughter, I will never let you marry Majeederh as long as I am alive in this world even if you are a Muslim, balle kuma ƙaton arne wanda babu ɗigon imani tunani a ransa" Uncle Isma'il ya ce "Alhaji Abdul'aziz wannan ba mafita bace, kamar kana ƙara tunzura shi ne wlh,This is not the way to solve this problem, take heart please" Abbu ya girgiza kai ya ce "Ba zan iya zama takaici ya tarwatsa mini zuciyata ba Isma'ila, Majeederh ta zame mini masifa da bala'i a cikin zuri'a kamar ita kaɗai na haifa? Ina sane fa time to time yake hauro mini gida kamar ɓaraho ya shigewa ɗakinta, tunaninta itama ban sani ba" Uncle Bello ya buɗe baki da mamaki bai ce komai ba ya juya ya kalli Abraham ya ce "Khalil, Majeederh kake so? Zaka iya kula da ita? Zaka iya musulunta?...," Abbu ya yanke maganar Uncle Bello da faɗin "Me ya sa kuke mini haka ne wai? To idan baku yarda ba, bari na ƙara maimaitawa wlh wlh wlh tallahi ko wannan shegen yaron zai musulunta ba zan taɓa lamumce masa auren Majeederh ba, kai na rantse da Allah da Majeederh ta auri yaron nan gwara ta zama duk abinda take son zama, gwara ta dauma babu aure har ƙarshen rayuwarta, gwara ta zubar mini da shegu na dinga ganinsu da dai ace wannan yaron ya aureta, i hate him for no reason, don Allah ku saka shi ya fice mini daga cikin parlour" A hankali Uncle Isma'il ya ce "Khalil" Abraham bai ɗago kai ba, balle ya kalli Uncle Isma'il bai ma san me suke tattaunawa ba tunda da Hausa suke magana, yadda yake jin ihun Abbu ya san faɗa yake, zuciyarsa kawai yake kaiwa nesa da tuna al'ƙawarin da ya yiwa Majeederh. Uncle Isma'il ya ƙara cewa "Khalil je waje ka jira ni" Ya ɗaga kansa ya kalle shi calmly ya ce "Na je gun je?" "A'a, ka je waje ka jirani itama tana can gidana ai" Miƙewa kawai ya yi jiki a sanyaye ya fice daga cikin parlourn ya jima tsaye yana kallon part ɗinta da yake a rufe yana jin kamar tana ciki musamman da ya ji zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, tuna Uncle Isma'il kuma ya ce bata nan yasa ya nufi compound na gidan. Yana tsaye jingine da motarshi idanunsa rufe ya ji ance "Aa yau Little ne a gidan namu?" Jin muryar Aaliyyah ya sanya ya buɗe idanunsa tare da zuba mata a hankali ya ce "Baki iya gaisuwa ba?" Aaliyyah ta zare ido tana riƙe haɓa ta ce "Wa zan gaisar? Kai? Tab ka tuna sanda muke goyaka ne a baya muke maka wanka" Ya haɗe fuska tamau idanunsa ya ƙara yin ja kamar ba zai magana ba sai kuma ya ce "Kee!" Aaliyyah ta ce "A'a ba wani batun kee, sbd kaga ka zama ƙato kamar samudawan farko? Daga yau Anti zaka dinga ce mini" Bai kulata ba sai kuma da sauri ya ce "Ko jee ba taɓa ganin jikina ba, balle ke yarinya" Ta riƙe haɓa ta ce "Yarinya?" Ya yi mata banza yana kallon motar Uncle Isma'il ta ce "Bari na ƙarasa na gaji sosai" Ya jinjina kai ta ce "Ka gama secondary school?" Ya wani irin kallonta sai kuma ya ce "A'a" Ta yi Murmushi ta ce "Ka dage ka gama sai ka fara zuwa University school ɗin da nake Yusuf Mai tama" Silently ya ce "Ohk" Sbd at this time bai ma san me zai ce mata ba, kuma darajar jinin Majeederh dake yawo a jikinta ya sanya yake conversing da ita. Yana kallo ta shige ciki. Uncle Bello ya kalli Abbu ya ce "Amma har ranka baka ji kunya da ka ce wai kana kallo Khalil yake shigewa part ɗin Majeederh? Ba tare da taking any action ba, kuma kana ji a ranka kai uba na gari ne ko? Ka bada gudunmawa mai tarin yawa a rayuwar Majeederh yanzu kuma kana son bawa ƴar cikinka laifi?" Ya girgiza kai Uncle Isma'il ya ce "Alhji Abdul'aziz Please faɗa mini tun daga kan haihuwar Majeederh kawo yanzu da tayi growing up ta mallaki tunaninta sau nawa cikin dare ka taɓa tashi ka duba ɗakinta kaga yadda take kwana, ka duba kaga akwai problem da zamanta ita ɗaya a ɗaki ko babu? To mace bata taɓa girma a gaban iyayenta muddin ba aure tayi ta nufi gidan mijinta ba, yadda duniya ta lalace Majeederh ko maza take kawowa cikin gidanka take kwana da su ba zaka taɓa sani ba, tunda baka bincike yanzu ma da Khalil ke zuwa dalili ne ya sanya ka fahimci yana zuwa sbd ka saka idanunka akan shi, haka son shi. Yadda zamani ya lalace da waya ma kadai zai iya sawa yarinya ta lalace ta dinga aikata ba daidai ba a ɗakinta tunda tana ganin ita kaɗai take kwana take tashi, waya kuma babu mai binka mata balle asan me take, Alhj Abdul'aziz till now da kake wannan harbin iskar baka taɓa zama ka ji mene problem ɗin ƴarka ba, baka taɓa zama ka ji wanne hali take ciki ba, babu mai bata shawara akan rayuwarta kama gdy Allah ya baka yarinya ta gari wlh, amma ka iya zama ka buɗe baki kace wai yaro yana shiga cikin bedroom ɗin Majeederh bayan baka taɓa tsawatar masa ba, idan zaka tashi ka kula da rayuwar yaranka fine" Uncle Bello ya sauke numfashi ya ce "Muma fata muke mu rabu da Abraham lafiya a samu Majeederh tayi aure shikenan dole ya haƙura, amma kana surutun banza da iska kasan kaifin bakin uba akan yaransa? Baka gudun bakinka ya kamata haka kurum kaja mata masifa? Bama wannan ba kana da wanda zaka bawa aurenta ne?" Calmly Abbu ya ce "Still searching" Ya ce "Allah ya kyauta ni zan shige" Uncle Isma'il ya miƙe ya ce tafiya zan ni ma. Fitowa sukai a tare suka bar Abbu zaune dafe da kansa dake juya masa. Suna fitowa Compound Raihana na shigowa ita da wani yaƙunannen mutum jikinsa duk dauɗa talakan ƙarshe mai fama da halin rayuwa. Bayan ta gaishe su Uncle Bello ya ce "Wannan fa?" Ta ɗan shafa kanta ta ce "Tasi'u sunansa" Ya ƙara cewa "Who's he?" Ta ce "Shi ne wanda mukai magana ya amince zai auri Majeederh, na kawo shi Abbu ya gansa" Uncle's ɗin suka dinga kallon Tasi'u kafin Uncle B ya ce "Ok neman kai aka ce miki ake da ita?" Ta ɗan shafa kai ta ce "Daman naga har yanzu ba tayi aure bane, kuma tana ta yawo a gari har ana mana gori wai iskanci take....," Wani ba hangon mari ta ji an sauke mata nan take hancinta ya fashe, aka ƙara sauke mata wani. Da sauri Uncle Isma'il ya ce "Khalil mene haka?" Huci kawai Abraham yake bai ma san akan me ake magana ba, sunan Majeederh kawai ya fahimta. Ya juya kan Tasi'u sai gashi ya saki fitsari a wando yana cewa "Wallahi ƙarya take ni Mahaukaci ne ba wani aure da za a mini" Sai kuma ya kwasa da gudu ya fice daga cikin gidan. Raihana ma ta miƙe tai waje da gudu tuni gefen fuskarta ya kumbura bata taɓa jin zafin mari irin wannan ba wanda ya gigita ta lokaci ɗaya. Abraham ya shiga motarshi ya fice da gudu tare da nufar gidan Grandpa. "Wannan yaron zuciya ne dashi" Uncle Bello ya ce "I like him, da musulmi ne babu abinda zai hana ni aura masa Majeederh wlh, ko zata dinga goya shi a baya dan ƙanƙantar shekarunsa" Uncle Isma'il ya ce "Ko waye ya faɗa mata namiji na yin kaɗan? Kuma ma age is just a number sanda zata fara ƙaunar mijinta ba wanda ya sani" Murmushi kawai Uncle Bello ya yi ya ce "Exlty, kaga a 9mnts ka samu jika" Ya ce "Ko shakka babu a wannan zafin naman na shi".... Bayan kwana biyar Majeederh na zaune duk ta rame ta kalli Latifa sai ta ji kamar ta faɗa mata Abraham na shigo mata bedroom cikin dare amma ta ji tsoron kada tayi mata wata fassarar Kullum abin na damunta ta rasa yadda za ta yi, bata da ƙarfin qiwwar tunkarar Abbu da wannan maganar hakan ya sanya bata da wani mafita kullum addu'a take Ubangiji ya ɗauki ranta ta huta da wannan halin da take ciki. "Ni laifinki nake gani, ga Aliyu ki aura wlh da tuni kin haihu da shi a sanda na yi miki wannan maganar amma kin ƙi" Majeederh ta girgiza kai ta ce "Ina jin kamar bani da rabon farin ciki a wannan duniyar Latifa, bani da gata na ko wacce mace na sare banda na san hukuncin wanda ya kashe kansa wlh da rataye kai na zan yi na huta, an kasa fahimta ba babu wanda ya gane halin da nake ciki, Abraham ya takura ni duk inda zani ya sani da ace na san ina ne dangin mahaifiyata wlh da can zan tafi maybe su za su iya fahimtar yadda nake ji a zuciyata, akwai mutanen da Ubangiji yake ƙaddara musu abubuwa wanda basu da rabo a duniya sai a lahira jikina yana bani ina ɗaya daga cikinsu" Hawaye ne ya kawo a idanun Latifa ta ce "Stop saying that dear, Ubangiji ya fi kowa sanin halin da kike ciki, In sha Allah watarana sai labari zaki zama
Chapter 88 · 0% Book details