Sashe 52
Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Da daddare bayan Majeederh ta gama dinner tayi sallar Magriba tana zaune tana azkar wayarta ya yi ringing ganin sunan Alpha yasa gabanta faɗuwa har kiran ya katse bata ɗauka ba, wani kiran ya sake shigowa ta yi bismillah ta ɗauka a hankali ta ji ya sauke ajjiyar zuciya ya ce "Me kike?" A hankali ta ce "Azkar" Ya yi jim ya ce "Shi ne baki picking kiran farko?" Ta ɗan marairaice ta ce "Kayi haƙuri" Ya share maganar ya ce "Majeederh" Ya kira sunanta ta kasa amsawa ya ce "Wannan shi ne hukuncin dana yanke mana, ina fatan banwa rayuwarki Shisshigi ba, idan kuma baki so na baki son aure let me know first" Ta yi shiru Ya ce "Kina son Aurena? Majee?" Da sauri ta kashe wayar tana rufe Idanunta kamar yana gabanta, daga can ɓangaren murmushi Alpha ya yi kana ya kashe wayar ya shiga Parlourn Mahaifiyarsa zaune ya sameta ya ce "Sannu da dare Mama" ta ɗaga masa hannu ta ce "Ya isa" Tana faɗin hakan ta miƙe tare da ficewa daga parlourn...... Ciki sati gudu wata muguwar shaƙuwa ta wanzu tsakanin General Alpha Bello da Malama Majeederh Abdul'aziz Khan! Tana jinsa har cikin zuciyarta gashi da masifaffen kishi, Anti ta kira mai gyara aka shiga yiwa Amarya Majeederh wani mahaukacin gyara, sosai Alpha yake kashe kuɗi har kawo lokacin ko hannu Majeederh ta hana ya riƙe mata..... Ana saura kwana ɗaya ɗaurin aure tun safe aka haɗa Family meeting gidan Uncle Isma'il an cika sosai yara da manya maza da mata, Alpha ne kawai babu a wajan can Uncle Bello ya ɗakko wayarsa ya kira shi yana ɗagawa ya ce "Wanne irin iskanci ne haka? Mu zamu zauna zaman jiranka?" Muryarsa can ƙasa Ya ce "Am sorry" Uncle Bello ya kashe kiran babu jimawa ya shigo kansa a ƙasa ya zauna can kujera, aka buɗe taro da addu'a Uncle Isma'il ya ce "Ma sha Allah, a gobe In sha Allah muna da ɗaurin auren da zai kafa tarihi a Khan family" Cikin sauri Alpha ya ce "Auren wa za'a ɗaura Uncle?" Gabaɗaya aka kallesa cike da mamaki Uncle Isma'il ya kasa bashi amsa, Alpha ya ce "Me ya sa kowa ke kallona? Why are you staring at the?" Anti ta ce "Gidanku General Aurenka mana" Ya ware idanu ya ce "Aurena kuma Anti? Dawa?" Ta ce "Da Majeederh" Ya ƙara waro idanu ya ce "Wacce Majeederh? Ni zan yi aure kuma Majeederh zan aura?" Innati ta ce "Ji wawa dilla kuyi abinda ya kawo ku" Uncle Isma'il ya kwaso katin ɗaurin auren ya ce "Gashi nan It's too late ka bawa friends ɗinka" Alpha ya kwashi katin da Shock ya dinga bin sunansa da idanu da kuma na Majeederh ya ɗago kansa ya ce "Ke ni na ce zan aureki? Wai meke faruwa ne?" Uncle Bello ya miƙe ya zabgawa Alpha ya ƙara zabga masa ya ce "Bana son hauka, lokacin da kazo da maganar aurenta kwana bakwai daga shige uban waye ya yi maganar ba kai ba?" Alpha ya girgiza kai ya ce "Wallahi Abba ni ban taɓa cewa ina sonta ba, ni me zai saka na aureta ƙanwata ce fa?" Innati ta ce "To da sauƙi tunda ba nono ɗaya kuka sha ba" Alpha ya ce "Uncle,Abba this is misunderstanding wlh ni bance zan auri Majeederh ba infact ina da wacce nake so kuma gobe zan kawota ku ganta don Allah kada ku aura mini Majeederh.......
*BOOK 1 PAGE 32*
*MIJIN MALAMA*
_littafina na kuɗi idan kina so ki biya ki karanta.... 08119237616 ko yayane kada ki karanta free without my permission please siyan littafinmu shi ne nuna soyayya a garemu🫂_
*BOOK 1 PAGE 32*
*MIJIN MALAMA*
_littafina na kuɗi idan kina so ki biya ki karanta.... 08119237616 ko yayane kada ki karanta free without my permission please siyan littafinmu shi ne nuna soyayya a garemu🫂_