← Book details Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 93

Sashe 43

Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read

*5 Month later..... The day*
Ranar Musabaƙar Alkur'ani ta ƙasa ya tashi ranar watan tafiyar alhazzai, watan zul-hajj. Tun ana sati ɗaya gabaɗaya Ɗaliban ko wacce ƙasa ta Muslunci suka sauka a ƙasar Misira, daga nan kuma manyan mutane, shugaban ƙasar ko wacce ƙasa, da gwamnoni, hatta Sarkin Saudiyya Sarki Sultaan ya halaccin Misira ana kwana ɗaya da shi da Mahaifiyarsa Zaytoon, hadda. Babban hall ɗin ya cika da jama'a fal, ƙabila da yare daban daban farar fata da ɓaka, jami'an tsaro kamar me. Saura minti ashirin a fara Ɗaliban duk suka shigo ko wanne da tambarin ƙasar shi a jikinsa, kowa aka nuna masa wajan zama kana zama computer zata nuna sunanka da kuma ƙasar da kake, gabaɗaya kuma ya kasance mata ke namiji ɗaya ne daga Qatar. Majeederh kanta a ƙasa sbd jiri da faɗuwar gaban dake riskarta na rashin sanin su waye a wajan. Zagaye biyar ne masu zafi, da kayi kuskure Computer zata tsayar da kai. Aka fara da ƙasar Saudiyya ta tayi karatu yadda ya kamata, a zagaye na huɗu dana biyar ta samu matsala. Abun kamar abin mamaki Majeederh ce ta zamo ta ƙarshe ma'ana Nigeria, Computer ta nuna mata farkon shafin suratul Yusuf, kana malamin ya ja.
Kanta a ƙasa ba tayi kuskuren ɗago kan ba, lokacin da tayi Basmala shiru wajan ya ɗauka ya zamana kamar ba a ji ƙira'ar kowa ba sai nata, sbd zaƙi da sautin muryarta daya zaga ko'ina na hall ɗin, a tare Sarki Sultaan da Zaytoon suka ɗago kan su, tare da kallon inda Majeederh take zaune fuska rufe, Zaytoon ya dubi computer gaban Majeed taga ansa. _“Majeederh Abdul'aziz Khan, from Nigeria”_ Karatu take mai ɗauke da zallar ƙa'idoji na Kur'ani. Tunda ta fara karatun idanunsa akanta ya kafeta da wani irin rikitaccen kallo yana mamakin yadda a ƙasar su Nigeria aka samu mai daɗin murya da ilimi kamar Majeederh. Tunda ta fara karatun babu gyara ko tuni, waƙafi, aya ko wasali har zuwa zagayen ƙarshe. Computer ta nuna mata Suratul Maryam tsakiyar surah. Cikin rashin sa a ta ɗago kanta da nufin sauke numfashi nan take komai nata ya kunce dalilin ganin dubban jama'ar da suke gabanta tare da kallonta suna kuma saurarenta. Ai gabaɗaya neman duk haddar Alkur'anin dake kanta tayi ta rasa kaf, a tare kuma Aliyu-haydar, Captain Alpha, Prince Ajlaal Sultaan da wani matashi dake kusa da Gwamnan jihar Kano suka ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!....

MIJIN MALAMA
Paid book
08119237616
Chapter 43 · 0% Book details