← Book details Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 93

Sashe 59

Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Who is he?" David ya tambaya, cikin mayen daya fara ɗaukar shi ya ce "I don't know, but i knw him na san muryar" David ya ce "Where?" Ya yi shiru... Ganin yana cikin maye kuma zai fi ɗaukar magana ya sa ya ce "Look Grandson, na ce ko da wasa bana son ganin jini a jikinka gwara ka fitarwa da wani jini da a fitar maka, ka ci mutuncin wanda ya ci naka, ka taka wanda ka ke so, kai ɗaya nake da shi a gefena You're my grandson exit? Babanka yabarka, baka da Mother baka da kowa a duniya sai ni, ni ne Grandfather naka, idan kuɗi na maganin komai a duniya to duk irin bala'in daka ɗauko zan ji da shi, ni ne shugaban church ni ne Pasto bayan haka kafi kowa sanin matsayina a ƙasar nan bana country ba, ina da kuɗi mai kuɗi shi ke da magana, a top 5 na masu kuɗin Nigeria zan shiga ciki, Mahaifinka Daniel zai shiga.....," "Stop calling his name, i hate him he's not my father" Abraham ya faɗi hakan idanunsa na lumshewa ya shiga surutan maye yana faɗin
"She left me, Mamina Grandpa, Mamina Mamina" Sai kuma jikinsa ya shiga jijjiga. Grandpa ya yi shiru kafin ya ce "Mamin nan taka maybe she's no more bata ra....," Tasss! Ya ji saukar Glasses ya miƙe da sauri yana riƙe Abraham ya ce "Am so sorry Dear, Maminka na nan I'll find out where she's hiding to" Da ƙyar bacci ya ɗauke Abraham bakinsa ɗauke da sunan “Mamin, JEENA" Ganin ya yi bacci yasa Grandpa kiran Taj a waya ta prvt line nasa yana ɗagawa ya ce "What's happened?" In brief Taj ya faɗa masa komai Ya ce "Ka nemi mai Zane ya yi drawing na mutumin ka kawo mini nan gida" Taj ya ce "Bad boy fa? Ai zai fi yin zanen yadda ake so" Grandpa ya ce "It's secret"....
Saudiya. Majeederh na zaune saman kujera gabanta ɗauke da laptop tana duba abubuwan da zatai a B.u.k idan ta koma Nigeria, komai nata maturel ne nutsuwa ga wani irin jan aji da kamon kai bata sakewa kowa fuska, har office ya buɗe wanda za a dinga samunta kai tsaye a ranakun weekend, ba ruwanta da batun tama sakawa ranta ba zatai ba tunda babu wanda ya ƙara tunkararta tana jin surutai na yawo a unguwa harda Social media ba ga family taƙi yin aure sai yawo... Door bell ta ji ta yi ƙara a hankali ta ɗan zame hannunta daga keyboard ɗin laptop ɗin, tare da ɗan yi shiru tana tunanin who is there by this time? Bata da appointment da kowa amma waye kuma? A hankali ta miƙe tana saka sunglasses ɗin ta na medical kana ta ƙarasa jikin ƙofar ta ce "Who's there?" Aka amsa da "Messenger" "Ok came in" Ta faɗa a gajarce, tana kowa tayi saurin saka hijabi da liƙab kana ta buɗe ƙofar, da mamaki ta dinga kallon mutumin ganin uniform ɗin masarauta a jikinsa da alamar Bafade ne shi yana ganinta ya zube a ƙasa yana kwarara mata gaisuwa, ita dai bata ce komai ba ya miƙe mata wata envelope ya ce "Saƙo ne daga Palace ranki ya daɗe Gwarzuwar Nigeria" Da hannu ta nuna masa ya ajjiye nan ƙasa ya ajjiye bayan ya tafi ta durƙosa ta ɗauka envelope ɗin tana komawa cikin bedroom ɗin, a hankali ta ware iya haɗuwa Envelope ta haɗu wani irin zaibar rubutu ne manne a jiki an rubuta.

_Your Highness Ajlaal Sultaan_
Invite
_Malama Majeederh Abdul'aziz Khan_

Ta duba date yau kenan sai kuma time 4 na yamma, ta dinga juya Envelope ɗin Ajlaal mijin Ƙhulud Arzaan kenan? za taga Ƙhulud farin ciki ya wanzu a zuciyarta duk da fargabar kiran ya ɗarso a zuciyarta.... 3:45 Daidai ta fito cikin wata Abaya dark blue tayi rolling kanta da vail sai liƙab da wani sirrin Glasses a Idanunta hannunta riƙe da hand bag da wayarta, tafiya take cikin tarin nutsuwarta kamala da sanin ya kamata, harta isa motar da ake jiranta tana zuwa driver ya buɗe zata shiga gaba ya ce "Ranki ya daɗe baya, ni driver ne" Ta ɗan girgiza masa kai kamar ba za tayi magana ba sai ta ce "Ina so gaban" Ta shiga ta zauna cikin sauri taja motar sai Palace.... Ƙhulud Arzaan na tsaye cikin shigar larabawa ga tsohon ciki a jikinta wanda shi ne karo na farko da zata haihu, fuskarta ɗauke da murmushi Majeederh na yin sallamawa Ƙhulud ta fasa ihu tare da nufar Majeederh, cak ta tsaya idanunta na gizo mata wani abu sai kuma ta nufeta suka rungume juna sosai sukai farin ciki bayan shekaru nawa sun sake haɗuwa, Ƙhulud ta ce "Ina mijinki fa?" Majeederh ta ɗan yi shiru sai kuma ta ce "Ban yi aure ba" Cikin wasa Ƙhulud ta ce "Kina jiran haɗaɗɗan namiji ko?" Murmushi kawai ta yi sai kuma ta ce "Kamar labari littafi? Kawai Allah bai kawo ba" Ƙhulud ta ce "Ubangiji ya kawo na gaban kwatance amma na yi mamaki na ɗauka ma kin haihu wlh" Majeederh ta yi shiru Ƙhulud ta ce "Mu je wajan Granny Zaytoon" Suka miƙe wani plat suka nufa mai kyau da tsari. Zaytoon na zaune saman ladduma gabanta cike da kayan itatuwa ana mata firfita suna shiga Zaytoon ta sauke wani irin kyakkyawan murmushi tana tafa hannu ta ce "Lale lale da babbar Malama" Gabaɗaya Hadiman suka fita Majeederh ta zube gaban Granny tana gaisheta ta amsa da "Ma sha Allah, Allahamdulillah Sannu kin ji ina sake tayaki murna" Ita dai kanta a ƙasa, Granny ta dinga kallonta ko zata cire liƙab ɗin fuskarta amma taƙi itama kuma bata ce ta cire ba sbd she don't want interfere a rayuwar Majeederh. Majeederh ta ɗago kai idanunta ya sauka akan wata matashiyar mata mai wani kyau kamar ba mutum ba, ta dinga kallon matar sai kuma ta ce "Ina yini?" Granny ta juya ta kalli matar da Majeederh ke gaisarwa wacce take zaune saman wheelchair Granny ta ce "Wai Gimbiya kike gaidawa? Allah sarki Hawwa'u ai bata da lafiya bata magana bata tafiya hannunta kawai ke motsawa" Cikin tausayawa Majeederh ta ce "Allah sarki, Allah ya bata lafiya" Granny ta ce "Ƙarasa wajanta mana, takwararki ce sunanta Hawwa'u yadda take kallon naki kamar ta sanki bayan ko Nigeria bata taɓa zuwa ba" Majeederh ta ƙarasa gaban matar ta durƙosa ta ce "Sannu Allah ya baki lafiya" Ga mamakinsu sai su kaga tayi murmushi harda hawaye ta riƙe hannun Majeederh ƙam! Sun jima kafin ta ce "Naga saƙon kira" Ƙhulud ta ce "Ohh Takawa ke kiranki" Gabanta ya faɗi ta ce "Mai martaba Sultaan?" Ƙhulud ta ce "Tsohon zance tuni muka ture shi mijina ke kan karaga ai, Mai martaba Ajlaal Sultaan ke kiranki" Ta yi shiru bata ce komai ba Granny ta ce "Fulani rakata mana, yana part ɗinsa ai ya bar fada tuni sai miskilanci yake ji jiya da yau" Ƙhulud ta ce "A'a jinin sarauta ke yawo a jikinsa fa, ba wani miskilanci" Tana faɗin hakan ta miƙe tsaye Majeederh ta miƙe ƙirjinta sai bugawa yake a haka suka ƙarasa wani irin ƙyakƙyawan plat mai ɗaukar kyau ga matso tsaran ƙofa nan birjik suna ganin Fulani suka zube Ƙhulud ta yi murmushi tare shigewa Majeederh ta bi bayanta, suna shiga Ƙhulud ta yi sallamawa yana zaune hakimce idanunsa rufe yana cikin wata Jallabiya mai kama da Alkyabba, ya ɗora hirami a saman kansa ga gefensa fuskarsa suma ta sakko kamar ka taɓa shi jini ya fito, bai amsa gaisuwar Ƙhulud ba, bai kuma buɗe idanunsa ba, Ƙhulud ta miƙe ta ce "Ina zuwa Majeederh" Majeederh kamar ta saka kuka ta cikin liƙab ɗin, amma ta kasa ko motsi. Wajan ya yi shiru ita ba tayi magana ba shi ma bai ce komai ba, bashi da niyyar cewa komai ɗin, shafewar seconds kafin Majeederh ta ce "Barka da hutawa Takawa" muryarta na rawa domin ba ƙaramin kwarjini ya yi mata ba, tana jin kanta Uncomfortable a gabansa musamman da taga kamar bai taɓa sanin wani Abu Annuri ba a saman fuskarsa. Ta ɗauka bai ji ba ta ƙara maimaita gaisuwar nan ma shiru tana ɗago idanunta da niyyar ganin ko baya wajan cikin rashin sa a idanunsu ya sarke cikin na juna, Ajlaal Sultaan ya kafeta da narkakkun idanunsa can kuma ya taɓe baki kana ya janye idanunsa a hankali ta ce "Gani" Ya jima kafin ya ce "Ke wa?" Tama ɗauka ba zai magana ba sai ta ji ya ce hakan. "Ance kana kirana" Bai ce komai ba ganin tana ƙoƙarin wulaƙanta kanta gabansa duk da tarin nata kimar ya sa ta miƙe tare nufar hanyar fita, sai da ta je bakin ƙofa ta ji an ce "Wait" Bata ɗauka da ita yake ba duka jikinta rawa yake Allah ya gani bata taɓa ganin mutum nai haibar Ajlaal ba zata fita ta ji an ɗora hannu akan hannunta dake jikin Handle da sauri ta juya ta ganshi tsaye kamar ya haɗiyeta gabaɗaya ya yi mata rumfa da ƙaton jikinsa rawar jikinta ya tsananta haka ma bakinta ƙirjinta na ɗagawa tunda uwarta ta haifeta bata taɓa yin kusanci da namiji kamar yadda sukai da Ajlaal ba, hannunsa ya murza akan nata kana jata zuwa cikin bedroom ɗinsa ba parlour ba......
Chapter 59 · 0% Book details