← Book details Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 93

Sashe 18

Mijin Malama Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

End of free pages
In sha Allah a nan na tsaya da free pages mu haÉ—u a paid grp. Yanzu zamu je asalin labari nan tsakiya ne, book1 shi ne asalin tashin hankalin littafin duk wani abu daya faru a nan ya faru. Book2 anan zamu ji yadda jaruman namu za su yi faÉ—a akan Majeederh.

ÆŠan waye?
Ya akai sai bayan shekara biyu ta haihu?
Dashe akai mata?
Cikin Aljanu ne?
Ko Abraham, ko Abu-turab ko kuma Zakin Hajia? Wa zai ci riba.

Book1 500
Book2 500
Gabaɗaya har mu kammala littafin 1k ne. Zaka iya fara biyan kuɗin book1 kafin mu fara book2.... 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank... Evidence of payment 08119237616. Zamu fara posting as soon as kun kammala payment. THANK YOU💋❤️🥰

Kafin kammalawa Wannan page ɗin gabaɗaya sadaukarwa ne ga HASEENATOU AUTAR MANYA. ELEGANT ONLINE WRITER'S, MIJIN MALAMA GRP 1,2. ALLAH YA SAKA MUKU DA ALHERI☺️🥰.

TALLAH👇🏾
Shin kuna bibiyar littafin *DAUƊAR GORA!* Wanda *HAWA__B__KUMO (REAL-SMASHER)* ke kawo maku? Wai³ this is an emotional story ever,idan ba kya bi maza ki nema ki fara kada ayi babu ke,*DAUƊAR GORA!* Labari ne dake ƙunshe da sarƙaƙiya akan ƙaddarar wata baiwar Allah *AYSHATOU AYATULLAH* wacce tayi fama da matsalar yoyon fitsari at a very young age,she really went through tsananin rayuwa,ƙiyayyar Family'n uba,kowa yana ƙyamar zama da ita,saboda larurar data sameta lokaci ɗaya,ba kuma wai dan haifeta da shi ba,ku nema ku karanta kada ayi babu ku..

*DANÆŠANO*

Kallon ƙyama Inna Tabawa matar ƙanin Babanta data kama baki kamar an yi pausing ɗinta ta bita da shi dawani murya take cewa "toh! Yau muke ganin tsiya da wasali.. Ke yanzu da girmanki gotai² sai ki saki fitsari a jikin kayanki? O'ohh! Ikon Allah.. Ni Tabawa na ga abunda ya isheni bai ishi Allah ba" ta riƙe haɓa tana sake jinjina al'amarin,kamar an cillota kuma kamar me jiran ayi da ita,Inna Larai tai wuff ta fito daga ɗaki jin maganganun da Tabawa ke faɗa ta ɗora da faɗin "ai Tabawa in faɗa maki iskanci ne da kuma ganin ta samu masu ɗaure mata,amma babu wani rashin lafiyar dake damun yarinyar nan,samun guri ne kawai.. Allah na tuba yau aka fara yin ciki? Kou a kanta aka fara haihuwa da za'a raina ma mutane hankali ace ta gamu da wani larurar dake hanata riƙe fitsari.. Zallar taɓara ce dai ke damunta,tou kuma kin san abunki da goyon kaka,babu abunda baza tayi ba da sunan larura" hawayen da suka ciko idonta tai saurin sa hannu ta goge,da sauri ta wuce za ta bar gurin,Inna Larai ta kalli yara²n gidan tace "Kaiii! Kui mata ihu kou za ta ji haushi ta dena abunda take,kui mata waƙar me fitsarin kwance ni na saku,duk wanda yayi kuma zan bashi Nera 5-5,manya kuma zan baku 20-20" ihu da tafi suka hau yi,kafin kace me ƙananan yaran gidan sun ɗauko murafen languna da ƙananun gallon suka fara kiɗa. Kamar cikin watan ramadhan lokacin tashe,haka muryoyin yara da manyan gidan masu jin haushinta babu gaira ba dalili suke tashi cikin waƙe suna faɗin "me fitsarin kwance,amalaala! Wace ce? Me fitsarin kwance.. Amalala.. Me fitsarin zaune.. Amalala.. Me fitsarin kwance!" Inna Larai tace "baku kama sunanta ba,ku faɗa ku ɗaga murya kowa yaji,idan tai zuciya gobe ta daina" kamar Inna Larai ta zugasu kuwa suka ci gaba da kiɗa suna waƙa "wace ce? Aya me fitsarin kwance,amalaala! Aya me fitsarin kwance.. Amalala.. Aya me fitsarin zaune.. Amalala.. Aya me fitsarin kwance!!" Ba waƙar da suke yi ne yafi taɓa mata zuciya ba,yanda wasu ciki ke zagayeta har suna kama mata zani suna janta,wasu na dungure mata kai shi ne abunda yafi komai sawa taji ta muzanta a idanun duniya,da wani irin sauri ta durƙushe bakin ƙofar ɗakinta,banda kuka babu abunda take kamar ranta zai fita,bata taɓa jin ta yi loosing hope ba irin yau,zuwa yanzu kam gaba ɗaya rayuwar ma ya fice mata a rai,musamman irin tozarci da wulaƙancin da take kan fuskanta daga danginta,abun yai mata yawan da ciwon zuciya yake neman kamata nan take,daga jiya zuwa yau sosai take cikin barazana/walaƙanci da tsokanarsu,har tunanin fita take kou wani uzuri ya kamata da dole zaisa ta haɗuwa da wani cikin mutanen gidan ba Baba Wada kou su Inna Asama'u ba,wani lokaci har ƙofar ɗakin ake zuwa ai mata ɗan kira...
Chapter 18 · 0% Book details