Sashe 31
Mijin Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
zuciyarta cike da tunanin wannan wani irin zama ne zasuyi. 50/ruwan tea ta sha sai farfesun kayan ciki data gani yana tiriri a kula ta zuba taci,tana gamawa ta kwashe kayan ta kai kicin,baba na ganinta tace,haba amarya da kin barsu a can ma zanzo in kwashe in wanke ai aiki nane aneesa tace ko aikinki ne ai wani lkcn kina bukatar taimako,kici gaba da goge gogen da kikeyi ni zan wanke wadannan kayan da zakiyi, don idan na koma daki kwanciya kawai zanyi.tace wlh da knje kin kwanta abinki duk aikin nan babu wanda ke gagarata, na riga na sba,kada alhaji ya dawo ya ganki a kicin yace nasa amarya aiki.aneesa tayi murmushi,babu abin zaice shima zai so hakan.ranar yini sukayi a kicin suna girke girke abubuwan da safeena ta barwa baba sallahu ta girka,har mada ba aneesa sunyi shi.karfe dayan rana direba yaje ya daukosu suhail a makaranta,dama idan an dauko su baba ke canza masu kayan a dakinsu tabasu abinci kafin karfe biyu safeena ta dawo,shi kuma odan uku yake dawowa idan yana garin kenan. yara na shigowa suka makalkale aneesa suna murna,ita ta canja baba ta canja musu kaya ta basu abinci sukace zasuyi bacci amma wai sai adakinta,ta debe su ta kaisu gadonta suka kwanta,basu dade ba sai bacci dukkansu.wanka aneesa tayo ta sallaci azahar sannan ta sake yin sabuwar shiga,wannan karon doguwar riga ta saka ta kamata daga saman kirji zuwa kwankwaso daga kasa aka saki rigar tayi fadi,anyi aiki a saman rigar da ahannu da kasanta;shadda mai ruwan malmo(dark purple)ssai ta yane kanta da gyale(light purple)kalar flat silifars din kafarta. 51) Tana zaune a falo tana kallo ne taji shigowar mota gidan, da kamar 5mins sai ta nufi dakin safeena tayi sallama ta amsa mata suka gaisa, sai aneesa ke ce mta, da safe na tashi da nafito baba tace kun tafi gurin aiki, wlh barci ne ya dauke ni da nayi sallah. Sannu ya aiki? Tace lfy, tace su Yusra suna gurinki sunyi barci hala? Tace eh sunyi, sama2 suka danyi hira Aneesa ta koma daki. Tym da Ishaq ya dawo tana daki ta dauka zai nemeta ko ya leko dakinta, sai taji shiru dole ta tashi ta nufi falon, suna bisa table da gimbiyar tasa ita tayi wanka, ta yi kwaliyya ta zuba wasu ubansu riga da wando sai da kiba ta kwafsa ta hana kwaliyyar yin kyau sai dai duk da haka tayi. Aneesa sai ta sami kanta da faduwar gaba tunda sukayi ido hudu da Ishaq taga yana mata wani irin kallo da bata gano na meye ba, ta isa gefensa tace sannu da zuwa, ya office, yace lfy lau ya zaman kadaici? Tayi murmushi kawai, ta juya zata koma daki yace dawo ki ci abinci ko kinci ne, eh naci duk da dai bata cin ba, gani tai gwara tace taci din ko ya kyaleta ta bar wurin, dan gimbiyarsa ta tsare gida, watau indai ita da ita ne zata sakar mata fuska, amma idan yana wurin bata son ya kula kowa sai ita. Yace to dawo ki zauna ki jira zanyi magana da ku. Ta dawo ya nuna mata kujera daga can gefensa yace ta zauna ta nan zaune suka cigaba da cin abincinsu tana ta dan satar kallonsu abaki suke bawa junansu, suna ta zuba soyayyarsu kila ma sun manta da ita a falon. 52) Suna Gamawa safeena ta kwalawa baba kira tace ta kwashe kayan. Sai suka dawo falo suka zauna. Ishaq ya dan fara yi musu nasiha dangane da zaman da Allah ya hada su tare, cewa safeena yayi ta rike girmanta ita ma aneesa ta rike kankanktarta, sannan yara ba banbanci na kowa ne, haka nan masu aikin gida ma na kowa ne, da ya gama yace inda mai magana tayi, safeena tace bata da magana haka ma aneesa batai magana ba. Sai yace yauwa maganar girki sai kuyi kwana 2 wadda taga zata shiga kicin tana iya shiga ga dai baba nan tana yin komai na girki, sannan ni bana zuwa dakin kowa kwana a dakina kowacce zata zo. Ga safeena nan zata gaya miki tsarin zamanmu. Ya kare maganar yana kallon aneesa, ita dai shiru tayi idanunta akasa, ita kam! Daga zuwanta ba zata iya kai kanta gurin miji ba. Indai ba shi ya zo ya gayyace ta ba, wannan ai bada kai ne a matsayinta na wadda ta bata san kan lamarin ba, ina laifin ya bita dakinta ya gayyato ta, ko kuma yayi mata kwana bakwai dinta in yaso daga baya ta dinga zuwa dakinsa, amma yanzun kam bazata iya ba. A dare ranar Aneesa da tayi wanka tayi shirin baccinta, batayi wani tunanin zuwa dkin miji ba, ko don ganin yadda uwargidan ke kaf2 da mijinta ne, amma tasha alwashin duk ranar da ya kirata ba zaki amsa kiransa ba. Da ta idar da sallah subahi bata koma bacci ba, a ganinta gwara ta shiga kicin ta taya safeena yin abin kari don bai kamata ba ta sakar mata ragamar komai ba. A kicin din ta sami safeena ta gaisheta ta tambayeta ta yara basu tashi ba, tace basu tashi ba. Aneesa ta kara cewa dama cewa nayi bari in zo in tayaki wani aikin, kada yau ma barci ya kwasheni. Safeena ta dan yatsina fuska tace ki barshi kin riga kinsa tuntuni idan ina hadawa mijina abinci bana son wani ya sami hannu, ki bari idan naki girkin ya zo saiki yadda kike so. Aneesa tace haba aunty ni dake ai duk daya ne, yadda kikace haka za'ayi. 53) Ta tabe baki tace, hum! Haka kike gani ni dake daya ne? To bari kiji in gaya miki, ki bar ganin kin auri mijina, wlh ni dake muna da banbance sosai, sannan bari in gargade ki banson shisshigi a al'amurana bana son katsalandan sannan ki bar ganin kamar na sake miki mijina kina wani shisshige masa, to wlh ki kiyayeni akn captain in dai kina neman zamanki cikin lfy da kwanciyar hankali to kada ki rabar mini mijina ki nisance shi shine zaman lfyarki, in kuma ba haka ba zaki ga abinda bakiyi zato ba, shi ma na lura sai rawar kai yake shiga mai amarya har yana hada matsiyana da naki to zan gyara wannan kuskuren da ya tafka idan yayi mantuwa ne zan tuna masa. Aneesa sarkin tsoro da saurin kuka nan da nan ta tsorata hawaye na zuba mata shar2 tace, don Allah kiyi hkr bazan sake miki shisshiga ba, zan iya barin miki mijinki wlh zan iya.... Ni dama ban dauka da zafi ba alamarinsa. Tace yo miji ko kibarmin ko kada ki barmin ai nawa ne sainaga dama zan bari yayi mu'amula da ke, ai na riga nagaya miki kin tafka babban kuskure da kika yarda kika aka aura miki mijin wata, in baki sani ba min wata MIJIN ARO NE! Kawai ke yanzon yar kararo ce a gidan ko in ce miki er kallon ce tsakanina da mijina kin gane? Aneesa ta share hawayen batace komai ba kawai sai ta juya ta koma dakinta tacigaba da aikin kuka, saboda tana ganin bata da wata mita yanzun tunda ta lura shima maigidan yana shakkar safeena, lallabata yake tamkar kwai ita kam, zata zubawa sarautar Allah ido ne, taga yadda taga yadda maigidan zai sarrafa yanayin zamansu, idan ya iya yin adalci to shikenan idan bai iya ba bashi ya sani, ita dai zata xuba idanu. MIJIN ARO 2***6 54) Da tayi wanka kwanciyarta tayi a falo tana jin hayaniyar yaran suna falo suna karyawa, taji fitowar Ishaq kamar taje ta gaisheshi sai wata zuciyar ta kwabeta. Tana na tana jinsu har duk suka fice kowa ya kama gabansa, sannan ne ta fito suka gaisa da baba mai aiki, yauma kamar jiya tare sukayi aikin girki har suka gama. Da dare ma taki fitowa duk da cewa taji dawowarsu tun da yamma, shima bai nemeta ba. Tana kwance ne suhail ya kwankwasa kofar falonta ya shigo yace, aunty daddy yace kizo kici abinci. Ta shafa kan suhail tace kaje kave na riga naci abincin. Ya juya yana waige2 ko zai ga kulolin abin a dakin bai gani ba, yace aunty Allah baki ci ba, tace naci dazun a kicin baka nan. Kace naci dazun. Ba don ya yarda ba ya juya ya fita, can ya dawo yace wai daddy yace ki fito kiyi hira ko kallo. Ta lura shidai ba zai shigo dakinta ba sai dai ya aiko ta fito, ta fito kuma idan ta fito babu anfanin fitowarta nata. Don mantawa zaiyi da ita suyi ta zuba hirarsu da matarsa, sannan ga matarsa sarkin iya luv bata jin kunyar yi masa komai agabanta, ko an haya mata kowa bai iya son miji da nuna masa lu ba ne sai ita oho? Ta dubi suhail tace muje, taja hannunsa suka nufi falon, suna cin abinci ta gaishesu dukkansu yace, me ya hanaki fitowa cin abinci? Tace na riga nacine, yace kin fi son ki dinga ci ke kadai ne bakya son ci tare da mu? Tace babu komai, yace ok indai kinfison hakan ne shikenan ki dinga ci, dama kada kice mun ware ki ne. Amma ki dinga fitowa cikin mutane tace to! Ta juya zata koma dakin yace, ba zakiyi hira bane? Tace bacci nakeji kuma banyi sallar isha'I ba. Yace to shikenan mu kwana lfy. Ta juya ta tafi duk wannan zancen da sukyi safeena tana zaune tana cin abincinta, tamkar bata ma gun, har aneesa ta wuce daki sannan ta bita da kallon a ranta tace yarinya kadan ma kika gani sai kin zamo abar tausayi tunda kika auri mijin safeena MIJIN ARO kenan. 55) Haka zaman Aneesa ya kasance a gidan Ishaq, yana zaune ne kurum tamkar bakuwa ko er kallo, don duk wasu al'amura na gidan safeena ce ke gudanarswa, ita tsakaninta da shi sai gaisuwa sai kuma idan ya dawi tazo tayi masa sannu da dawowa, yara kuma indai ba sch ba sukaje ba to suna nan makale gurin aneesa don wata rana ma agurinta suke kwana, hakan bai sa uwarsu ta sassauta mata ba, sh kuma maigidan bai bi ta kanta ba, sabgar gabansa kawai yakeyi, saboda shi aganinsa safeena ta tsare masa komai bai da sauran