Sashe 5
Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babban palon alfarma ne da kusan Babu abinda ya rasa na tsarin gidajen masu arziki,
Sanyin AC da qamshi tako Ina tashi yakeyi Dan haka sai jikin Zainab ya sakeyin sanyi Dan kwata kwata rayuwarta Bata taba zuwa irin guraren Nan ba.
Can hanyar kitchen aka nufa da ita matar tace ta jirata anan bara taje ta sanar da Haj maryamah din.
Saida Zainab tayi kusan mintuna ashirin agurin kafin Maryamah ta fito sanye cikin wata maroon jallabiya
Fuskarta da fatarta sai sheqi sukeyi tayi haske sosai taqara wani irin lafiyayyan kyau da kiba duk saita sauyawa Zainab din kwata kwata kaman wata balaraba.
Saurin sauke Kai Zainab tayi cikin girmamawa ta gaidata tareda yimata sannu da jiki na rashin lafiyar datai.
A kasalance cikeda mamaki maryamah ta amsa tareda kallon Karima tace ta wuce tabasu guri.
Maido kallonta tayi kan Zainab da kayanta cikin rashin son daga murya tace"
Keda waye kukazo?
Ina ummar?
Umma Tana gida
Itace tace nabiyo Wanda yakaita gida nazo nan.
Shiru maryamah tai Tana tunanin me umma ke nufi da hakan
Dan haka saita juya ta nufi palonta Dan Kiran umman taji meke faruwa.
Umma na daukar wayar Kai tsaye tace,
Me Zainab zatayi anan da kika aikota?
Ganin nayi masu aikin Nan idan aka biye halayensu haka zakiyita canjawa batareda kin samu yanda kikesoba gashi kina fama da laulayin Nan gwara ita din datake 'yar uwarki zata Miki duk yanda kikeso anhuta da neman kowace me Aiki Zainab zata iya duk wani aikin gidan..
Cikin tare zancen umman tace"
Umma kinsan aikin gidan Nan kuwa?
Ina zata iya sa,
Kina ganin girman gidan Nan ko shararsa zata iya,
Ga aikin abincin dare da ake fitarwa karatun Asad da malamansa,
Hakama umma zaginmu zaayi zaace na mun maidata 'yar aiki,
Duk ba bayan wannan Sam bana buqatarta kusa Dani umma kinsani banaso.
Cikin takaici umman tace"
Duk Wanda zaiyi magana yayi a bayana badai gabana ba Dan kuwa Babu mai iko da ita sai ni
Ni ubanta ya barwa amanarta hakama akwai wanda ya taba damuwa da ita ko kulawa da itane bayan mu din?
Idan bamu qaru da junaba to meye amfanin riqon nata danayi.
Rashin buqatarta a gidanki kuwa hakuri zakiyi ta zauna da itace kawai zatai Miki Aiki yanda kikeso ba qirsa koba komai ai mijinki ne me biyan kudin karatunta Dan haka Kuma kwa fanshe guminku anan.
"Umma to ke kuma wa zai dinga miki duk ayyukan da ta ke yi ɗin?"
Sai alokacin Umma ta sauke numfashi tana tausasa murya tace,
"Maryamah ko jiya da mu kai magana a asibiti na sake maimaita Miki cewan Cameron zan koma can gida cikin 'yan uwana tunda bani da kowa anan Kuma dai Tunda ba aure yanzu nakeyiba anan din gwara na koma can din cikin dangi shiyasama na sake yanke shawarar kawo Miki Zainab din Nan Dan Kinga bazan dauketa naje da itaba acan idan dangin mahaifiyarta sun sake zuwa ki miqa musu ita idanma basuzoba Tana samun miji ko wane iri ne aura mata taje nata gidan mijin kowa ya zauna lafiya shekenan.
Shiru kawai maryamah tayi sbd batasan abinda zataceba Kuma Dan haka sukai sallama kawai ta fito Kai tsaye tasa Inna Karima takai zainab Dan madaicin dakin dake hanyar kitchen Wanda masu Aiki yakamata su zauna anan Amma maryamah dayake batason qazantar masu Aiki dakin yanan sabonsa Babu me aikin data Taba zama acikinsa komai nasa na Nan sabo
masu aikin Kuma dakin boys quarters take kaisu Dan ko Inna Karima acan take yanzu hakan.
Dakin da aka bawa zainab qatuwar katifa ce aciki sabuwa da wardrobe sai madubi da toilet me girma sai Kuma zanin gado har biyu da daddumar sallah da fanka qarama ta tsaye sbd gidan koina pop ne Dan haka AC ne ako Ina Banda dakunan masu Aiki.
Inna Karima ta nuna mata ta saka kayanta cikin wardrobe
Inna Kariman ce ta shimfida mata bedsheet a katifar da kanta takuma share mata dakin tai mopping tareda wankin toilet din dayake tamkar dakin wani basarake sbd kyansa da girmansa.
Duk aikin da Inna Karima tayi mata tayi mata ne dan taga yanda akeyi ta koya tun yanzu din Dan a daukarta sabuwa me aikice aka kawo wadda zata karba ragamar tsaftace koina ita Kuma taji da aikin girki.
Duk aikinda Inna ta nunawa zainab din tagane Tunda Dama aikin wahala shine rayuwarta ba Wai sabon Abu bane.
Kitchen takuma janta can ma ta nuna mata yanda zatai wanke wanke a kitchen din tareda tsaftacesa.
A taqaice dai Tunda zainab ta iso gidan a ranar Bata zaunaba sai dare sbd aikin da aka fara tarbarta dashi gashi Bata Kuma ganin maryamah ba sai dare data fito tace zainab din ta dafa mata ruwan shayin datake dafo musu da suna asibiti.
Inna Karima ce ta kunnawa zainab din gas ta dafa mata aka Bata inda ta juye mata takai mata kafin suka kashe komai tareda rufewa itada Inna Karima kowa ya nufa makwancinsa.
Sallar ishai tayi ta kwanta take bacci ya dauketa Dan Dama ita data kwanta sai bacci sbd aikin datake wuni yi jikinta a gajiye yake Koda yaushe.
A gida akan tabarma take kwana saida maryamah tayi aure umma ta saida katifar maryamah babba ta siya mata wata Yar yololuwar katifa data gama sidewa Amma dadinta takeji ko ahakan ita,.
Ganin wannan babbar katifar baisa ta hau akai ta kwanta ba sbd gudun laifi ko zaqewa dakuma shakkar yiwa maryamah laifi da haka a kan tiles ta shimfida daddumar sallah tayi kwanciyarta har safe.
Qarfe 7 Inna Karima Tazo ta tadata suka fito Dan fara aikin gidan.
Shara tafara mai kyau
Ya goge komai cikin tsoro tsoron kada ta fasa ga jikinta dake faman Yar rawar fargabar kada tayiwa maryamah laifi da yanayin aikin.
Fes tayiwa koina saidai Kam yau saida bayanta ya amsa wahalar aikin daya bambamta Dana gidansu data saba,
Palo uku manya Manya da dakuna biyu da kitchen da corridors biyu da toilets ta share tai mopping takuma wanke Bayan goge gogen datai.
Kowanne gurin datai aikin girmane dashi Babu qaramin guri,.
Jin tayi bayanta ya riqe qyam kamar bazata iya miqewa daidaiba Amma haka ta miqe ta share babbar harabar gidan da kusan mota hudu yake dauka.
Ko data gama ayyukan tas bayanta da qugunta sun mata nauyi daqyar take iya miqewa tsaye daidai haka ta zauna kitchen taci abincinta da Inna Karima ta Bata Tana gamawa tayi wanke wanke tasake tsaftace kitchen din ta nufi dakinta.
Daqyar tayi wanka ta saka kaya tazo ta Dan kwanta take baccin wahala yafara daukan kenan saiga Kiran Inna Karima akan taje ta tattaro kayan dining idan su masu gidan sun gama breakfast.
Haka ta tashi taje tattara gurin tasake gyarawa Takoma kitchen tayi Wani wanke wanken tafara Taya Inna Karima aikin abincin Rana.
Wunin ranar ma Kam Bata sake samun zama ba sallah kawai ake barin taje tayi tadawo
Da yamma ma saida takuma sharar harabar gidan sbd karatun daren da akeyi.
Da daddare data kwanta tsamin da jikinta yayi ko bacci mai dadi data saba samu Bata samuba ranar.
Washe garima duk aikin datai a jiyan haka ta maimaitashi Dan haka ranar jikinta har kasa daka yayi da zazzabi ta kwana.
Haka aikin yakasa karban jikinta kusan kwanaki hudu kullum da zazzabi take kwana Amma harta Dan fara sabo da aikin jikin ne dai bai sababa sbd aikin yafi karfin shekarunta ga makaranta har lokacin maryamah batace mata komaiba akai ita Kuma Bata cika ganintaba kota ganta bazata iya Mata magana ba sbd shakka da tsoron Mata laifi.
Idan tace tana Bata gaji da zaman gidan matuqa ba ta yi ƙarya,
don kuwa duk aikin da ta ke yi a gidan Umma bai kai nan ba sbd ko gyaran ɗakunan da take yi a can girman falukan wannan gidan na Maryamah shi ne matsayin girman ɗakunan gidan Umma kaf ɗinsu
Duka gidan dakin Alh Asad ne kawai ba itace take sharewaba Amma kaf gidan itace mai share koina ta gyara
Har aikin kitchen da Inna Karima yakamata tayi kusan duk itace take Rabi sbd Maryamah wasu lokutan tafison aikin zainab na abinci hardai na marmari.
Sati biyu da zuwanta gidan ta fara sabawa da duk wasu bautan da ta ke yi
Umma kuma a satin ta haɗa komi nata ta ɗaga zuwa Cameron bayan ta zo har gidan Maryamah sun yi sallama da juna tayiwa zainab nasihar biyayya ga Yar uwarta tareda tunatar da ita batada kowa sai su Dan haka ta zauna ta Taya Yar uwarta aikin gidanta Tunda idanma batayiba batada gurin zuwa.
Zainab ta sha kuka sosai duk da cewa babu shaƙuwa tsakaninta da Umman amma sai tafiyar nata ya ɗaga hankalinta sosai sbd koba komai tafi Jin sanyi agurin umman tun rasuwar Abbansu sbd lokuta da Dama umman na Mata wasu abubuwan kulawa sabanin maryamah dako kallon fuskar juna basayi sosai,
Kwata kwata Babu shaquwa ko kusanci ko wata qauna a tsakaninsu Dan haka takejin da umman zata taimaketa da ta tafi da ita ko bautarce ta yarda acan tayiya yi Mata har tsufa yafi Mata zaman Nan din.
Bayan tafiyar umma da sati uku maryamah tayi barin cikinta Dan haka gidan duk suka shiga damuwa musamman maigidan gabaki dayama dauketa yayi sukai tafiya wata qasar aka bar su zainab masu aiki.
Bayan tafiyarsu ne zainab tasamu Takoma makaranta shima saida aka Kira Alhaji Asad din daga makarantar Yana can suka sanar Masa ta Dena zuwa shinefa yayi waya drivern gidan na kaita wata Rana Kuma da qafa take zuwa tadawo da qafa duk nisan kuwa sbd driver ganin yakeyi Mai aikice ita Amma tasamu shigar da ake kaita makaranta da mota Dan haka Wani lokacin yake shareta ya dauki motar ya tafiyarsa nasa sabgogin.
Karatunta da aikin gidan ya taru ya hade mata gabaki daya rayuwarta Aiki ya firgitata ga kadaici,
Sam bayan aikin wahalar hidimar gidan maryamah da hidmar maryamah din batada aboki Dan haka duk Takoma kaman wata nakasasshiya karatun ma yanzu sai ahankali Bata Wani ganewa zuwa kawai takeyi.
#MAMUH#
#SISTERS#LIFE#LOVE#AQEEL#AMAL IDON NERA#
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
Sanyin AC da qamshi tako Ina tashi yakeyi Dan haka sai jikin Zainab ya sakeyin sanyi Dan kwata kwata rayuwarta Bata taba zuwa irin guraren Nan ba.
Can hanyar kitchen aka nufa da ita matar tace ta jirata anan bara taje ta sanar da Haj maryamah din.
Saida Zainab tayi kusan mintuna ashirin agurin kafin Maryamah ta fito sanye cikin wata maroon jallabiya
Fuskarta da fatarta sai sheqi sukeyi tayi haske sosai taqara wani irin lafiyayyan kyau da kiba duk saita sauyawa Zainab din kwata kwata kaman wata balaraba.
Saurin sauke Kai Zainab tayi cikin girmamawa ta gaidata tareda yimata sannu da jiki na rashin lafiyar datai.
A kasalance cikeda mamaki maryamah ta amsa tareda kallon Karima tace ta wuce tabasu guri.
Maido kallonta tayi kan Zainab da kayanta cikin rashin son daga murya tace"
Keda waye kukazo?
Ina ummar?
Umma Tana gida
Itace tace nabiyo Wanda yakaita gida nazo nan.
Shiru maryamah tai Tana tunanin me umma ke nufi da hakan
Dan haka saita juya ta nufi palonta Dan Kiran umman taji meke faruwa.
Umma na daukar wayar Kai tsaye tace,
Me Zainab zatayi anan da kika aikota?
Ganin nayi masu aikin Nan idan aka biye halayensu haka zakiyita canjawa batareda kin samu yanda kikesoba gashi kina fama da laulayin Nan gwara ita din datake 'yar uwarki zata Miki duk yanda kikeso anhuta da neman kowace me Aiki Zainab zata iya duk wani aikin gidan..
Cikin tare zancen umman tace"
Umma kinsan aikin gidan Nan kuwa?
Ina zata iya sa,
Kina ganin girman gidan Nan ko shararsa zata iya,
Ga aikin abincin dare da ake fitarwa karatun Asad da malamansa,
Hakama umma zaginmu zaayi zaace na mun maidata 'yar aiki,
Duk ba bayan wannan Sam bana buqatarta kusa Dani umma kinsani banaso.
Cikin takaici umman tace"
Duk Wanda zaiyi magana yayi a bayana badai gabana ba Dan kuwa Babu mai iko da ita sai ni
Ni ubanta ya barwa amanarta hakama akwai wanda ya taba damuwa da ita ko kulawa da itane bayan mu din?
Idan bamu qaru da junaba to meye amfanin riqon nata danayi.
Rashin buqatarta a gidanki kuwa hakuri zakiyi ta zauna da itace kawai zatai Miki Aiki yanda kikeso ba qirsa koba komai ai mijinki ne me biyan kudin karatunta Dan haka Kuma kwa fanshe guminku anan.
"Umma to ke kuma wa zai dinga miki duk ayyukan da ta ke yi ɗin?"
Sai alokacin Umma ta sauke numfashi tana tausasa murya tace,
"Maryamah ko jiya da mu kai magana a asibiti na sake maimaita Miki cewan Cameron zan koma can gida cikin 'yan uwana tunda bani da kowa anan Kuma dai Tunda ba aure yanzu nakeyiba anan din gwara na koma can din cikin dangi shiyasama na sake yanke shawarar kawo Miki Zainab din Nan Dan Kinga bazan dauketa naje da itaba acan idan dangin mahaifiyarta sun sake zuwa ki miqa musu ita idanma basuzoba Tana samun miji ko wane iri ne aura mata taje nata gidan mijin kowa ya zauna lafiya shekenan.
Shiru kawai maryamah tayi sbd batasan abinda zataceba Kuma Dan haka sukai sallama kawai ta fito Kai tsaye tasa Inna Karima takai zainab Dan madaicin dakin dake hanyar kitchen Wanda masu Aiki yakamata su zauna anan Amma maryamah dayake batason qazantar masu Aiki dakin yanan sabonsa Babu me aikin data Taba zama acikinsa komai nasa na Nan sabo
masu aikin Kuma dakin boys quarters take kaisu Dan ko Inna Karima acan take yanzu hakan.
Dakin da aka bawa zainab qatuwar katifa ce aciki sabuwa da wardrobe sai madubi da toilet me girma sai Kuma zanin gado har biyu da daddumar sallah da fanka qarama ta tsaye sbd gidan koina pop ne Dan haka AC ne ako Ina Banda dakunan masu Aiki.
Inna Karima ta nuna mata ta saka kayanta cikin wardrobe
Inna Kariman ce ta shimfida mata bedsheet a katifar da kanta takuma share mata dakin tai mopping tareda wankin toilet din dayake tamkar dakin wani basarake sbd kyansa da girmansa.
Duk aikin da Inna Karima tayi mata tayi mata ne dan taga yanda akeyi ta koya tun yanzu din Dan a daukarta sabuwa me aikice aka kawo wadda zata karba ragamar tsaftace koina ita Kuma taji da aikin girki.
Duk aikinda Inna ta nunawa zainab din tagane Tunda Dama aikin wahala shine rayuwarta ba Wai sabon Abu bane.
Kitchen takuma janta can ma ta nuna mata yanda zatai wanke wanke a kitchen din tareda tsaftacesa.
A taqaice dai Tunda zainab ta iso gidan a ranar Bata zaunaba sai dare sbd aikin da aka fara tarbarta dashi gashi Bata Kuma ganin maryamah ba sai dare data fito tace zainab din ta dafa mata ruwan shayin datake dafo musu da suna asibiti.
Inna Karima ce ta kunnawa zainab din gas ta dafa mata aka Bata inda ta juye mata takai mata kafin suka kashe komai tareda rufewa itada Inna Karima kowa ya nufa makwancinsa.
Sallar ishai tayi ta kwanta take bacci ya dauketa Dan Dama ita data kwanta sai bacci sbd aikin datake wuni yi jikinta a gajiye yake Koda yaushe.
A gida akan tabarma take kwana saida maryamah tayi aure umma ta saida katifar maryamah babba ta siya mata wata Yar yololuwar katifa data gama sidewa Amma dadinta takeji ko ahakan ita,.
Ganin wannan babbar katifar baisa ta hau akai ta kwanta ba sbd gudun laifi ko zaqewa dakuma shakkar yiwa maryamah laifi da haka a kan tiles ta shimfida daddumar sallah tayi kwanciyarta har safe.
Qarfe 7 Inna Karima Tazo ta tadata suka fito Dan fara aikin gidan.
Shara tafara mai kyau
Ya goge komai cikin tsoro tsoron kada ta fasa ga jikinta dake faman Yar rawar fargabar kada tayiwa maryamah laifi da yanayin aikin.
Fes tayiwa koina saidai Kam yau saida bayanta ya amsa wahalar aikin daya bambamta Dana gidansu data saba,
Palo uku manya Manya da dakuna biyu da kitchen da corridors biyu da toilets ta share tai mopping takuma wanke Bayan goge gogen datai.
Kowanne gurin datai aikin girmane dashi Babu qaramin guri,.
Jin tayi bayanta ya riqe qyam kamar bazata iya miqewa daidaiba Amma haka ta miqe ta share babbar harabar gidan da kusan mota hudu yake dauka.
Ko data gama ayyukan tas bayanta da qugunta sun mata nauyi daqyar take iya miqewa tsaye daidai haka ta zauna kitchen taci abincinta da Inna Karima ta Bata Tana gamawa tayi wanke wanke tasake tsaftace kitchen din ta nufi dakinta.
Daqyar tayi wanka ta saka kaya tazo ta Dan kwanta take baccin wahala yafara daukan kenan saiga Kiran Inna Karima akan taje ta tattaro kayan dining idan su masu gidan sun gama breakfast.
Haka ta tashi taje tattara gurin tasake gyarawa Takoma kitchen tayi Wani wanke wanken tafara Taya Inna Karima aikin abincin Rana.
Wunin ranar ma Kam Bata sake samun zama ba sallah kawai ake barin taje tayi tadawo
Da yamma ma saida takuma sharar harabar gidan sbd karatun daren da akeyi.
Da daddare data kwanta tsamin da jikinta yayi ko bacci mai dadi data saba samu Bata samuba ranar.
Washe garima duk aikin datai a jiyan haka ta maimaitashi Dan haka ranar jikinta har kasa daka yayi da zazzabi ta kwana.
Haka aikin yakasa karban jikinta kusan kwanaki hudu kullum da zazzabi take kwana Amma harta Dan fara sabo da aikin jikin ne dai bai sababa sbd aikin yafi karfin shekarunta ga makaranta har lokacin maryamah batace mata komaiba akai ita Kuma Bata cika ganintaba kota ganta bazata iya Mata magana ba sbd shakka da tsoron Mata laifi.
Idan tace tana Bata gaji da zaman gidan matuqa ba ta yi ƙarya,
don kuwa duk aikin da ta ke yi a gidan Umma bai kai nan ba sbd ko gyaran ɗakunan da take yi a can girman falukan wannan gidan na Maryamah shi ne matsayin girman ɗakunan gidan Umma kaf ɗinsu
Duka gidan dakin Alh Asad ne kawai ba itace take sharewaba Amma kaf gidan itace mai share koina ta gyara
Har aikin kitchen da Inna Karima yakamata tayi kusan duk itace take Rabi sbd Maryamah wasu lokutan tafison aikin zainab na abinci hardai na marmari.
Sati biyu da zuwanta gidan ta fara sabawa da duk wasu bautan da ta ke yi
Umma kuma a satin ta haɗa komi nata ta ɗaga zuwa Cameron bayan ta zo har gidan Maryamah sun yi sallama da juna tayiwa zainab nasihar biyayya ga Yar uwarta tareda tunatar da ita batada kowa sai su Dan haka ta zauna ta Taya Yar uwarta aikin gidanta Tunda idanma batayiba batada gurin zuwa.
Zainab ta sha kuka sosai duk da cewa babu shaƙuwa tsakaninta da Umman amma sai tafiyar nata ya ɗaga hankalinta sosai sbd koba komai tafi Jin sanyi agurin umman tun rasuwar Abbansu sbd lokuta da Dama umman na Mata wasu abubuwan kulawa sabanin maryamah dako kallon fuskar juna basayi sosai,
Kwata kwata Babu shaquwa ko kusanci ko wata qauna a tsakaninsu Dan haka takejin da umman zata taimaketa da ta tafi da ita ko bautarce ta yarda acan tayiya yi Mata har tsufa yafi Mata zaman Nan din.
Bayan tafiyar umma da sati uku maryamah tayi barin cikinta Dan haka gidan duk suka shiga damuwa musamman maigidan gabaki dayama dauketa yayi sukai tafiya wata qasar aka bar su zainab masu aiki.
Bayan tafiyarsu ne zainab tasamu Takoma makaranta shima saida aka Kira Alhaji Asad din daga makarantar Yana can suka sanar Masa ta Dena zuwa shinefa yayi waya drivern gidan na kaita wata Rana Kuma da qafa take zuwa tadawo da qafa duk nisan kuwa sbd driver ganin yakeyi Mai aikice ita Amma tasamu shigar da ake kaita makaranta da mota Dan haka Wani lokacin yake shareta ya dauki motar ya tafiyarsa nasa sabgogin.
Karatunta da aikin gidan ya taru ya hade mata gabaki daya rayuwarta Aiki ya firgitata ga kadaici,
Sam bayan aikin wahalar hidimar gidan maryamah da hidmar maryamah din batada aboki Dan haka duk Takoma kaman wata nakasasshiya karatun ma yanzu sai ahankali Bata Wani ganewa zuwa kawai takeyi.
#MAMUH#
#SISTERS#LIFE#LOVE#AQEEL#AMAL IDON NERA#
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200