← Book details Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 95

Sashe 12

Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsananin tausayi da sabuwar kaunar Maminsa ne ya shigesa Wanda a gabansu saida ya zubda qwallar wani irin 'daci da raunin da zuciyarsa ta samu na Jin wannan babban lamarin.

Kai tsaye ya amince da barin qasar zuwa UK Dan kuwa bazai taba barin sbd shi Mamin tabar gidanba Dan kuwa yasan batada gurin zuwa.... Amma a gabansu ya shimfida wani kyakkyawan alqawari Mai girma na cewa duk ya dawo zai dauki Maminsa har abada nauyinta zai dawo kansa yadauke musu nauyinta tun daga na jini harna jiki.

Da farko Haj maryamah Bata fahimtaba saida umma tasake nuna Mata illar Hakan da gaba zaa samu Dan haka tace Bata yardaba
Zainab qanwarta ce a hannunta zata zauna sai aure idan tanada rabon yinsa kenan.

Kalmar ta Sosa zuciyar Aqeel yakalli Mamin wadda take zaune batada abin cewa sai yanda akai da ita.

Take wani ciwo da daci yakuma mamaye zuciyarsa Dan haka baice komaiba aka bar zancen ahakan.

Umma sai datai kusan wata daya kafin ta tattara ta koma Cameroon tabarsu Bayan tayi musu Yan nasihu Amma dai kusan kowa yanzu zuciyarsa ta cire Rai daga Dan uwansa.

Zainab gabaki daya yanzu tasake zama wata iri tayi sanyi sosai fiyeda baya Dan an ankarar da ita ko zaman datakeyi gidan alfarma ce akeyi Mata
Batada wani amfanin da zaa mutunta Dan shi saima tunatar da ita da akai ita din ba kowa bace face Yar Aiki a gidan wadda zaa kora aduk lokacin da akaso.

A yanzu gidan Bayan Aiki da abinda aka sakata Yi Babu abinda takeyi
Data Gama take komawa inda dakinta yake ta zauna ta kame kanta.

Shi Kansa Aqeel yanzu tsakaninta dashi sai idan yazo dakinta da safe gaidata kamar yanda ya saba Amma duk wani alaqarta dashi ta Dan ja baya dashi.

Wannan sabon halin data shiga ya sakasa damuwa shima Amma Kuma shima cikin nasa yanayin na damuwar yake Dan haka kowa dai yazama sai ahankali gidan.

Ta bangare daya karatunsa na addini da malaminsa Kuma ubansa malam Sanda yayi zurfi,

Malam Sanda A yanda yakejin Aqeel shima tamkar shine ya haifesa musamman Dama baida da ko daya ba taba haihuwaba,

Asalinsa Dan Billiri dake gombe karatun almajiranci ne ya kawosa cikin gombe daga Nan aka ringa kaisu garuruwa almajirancin qarshe ya tsaya anan Jigawa harya girma yafara Dan sirkawa Dana Biko kadan kadan haryayi karatun secondary Amma daga Nan bai Dora ba saiya Dan ringa kasuwanci Yana karatun addinin sosai har Allah yasa ya Dan Yi suna a karatun Addininsa.

Tunda iyayensa suka rasu ya rage zuwa gida haryazo Yana jimawa sosai baijeba Dan kusan dangin kowa tayita kansa.

Anan yayi aurensa na farko kusa shekararsa bakwai da matar Allah bai Basu haihuwaba qarshe ta rasu sanadin breast cancer batareda ta haihuba..
Tun daga lokacin bai Kuma aureba haka yake zaune Yana cigaba da yiwa addini hidima.

Alh Asad shine kusan komai na malam Sanda Dan kuwa ko dawainiyar jinyar matar malam din shine ya dauki nauyi har qasar India sukaje Amma Hakan dai Allah yayi bamai warkewa bace.

Tsakanin malam Sanda da Alhaji Asad akwai kauna da shakuwa tareda mutunci sosai kamar Yan uwan jini haka suka dauki juna...

Alaqarsu tasaka malam Sanda cusawa Alh Asad kaunar addini Mai tsanani gashi Hakan yazo har Dan sa Aqeel Wanda kusan ayanzu yafi mahaifinsa daya rasu akidar karatun na addini gashi shi yanada kuruciya Kansa a bude yake sai ya zama har yanafin malam din riqe wasu abubuwa idan malam din ya Dan tsaya.

Farko Kai tsaye sha'awar aurarda Maminsa ga malaminsa Yashigesa Amma Kuma lura da su dukan kamar iyayensa ne sai bai fidda maganar kai tsaye ba sbd yanason fara Jin raayin Maminsa Dan bazai iya Mata abinda batasoba.
##MAMUH#
#LOVE
#AQEEL ASAD
#IDON NERA

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*

9
Duk da Maminsa ce bayajin zai tsaya boyon zancen dake ransa gameda shawarar tasa,

Qari Kuma Daman zuciyarsa Bata kwanta da barinta gidanba sai ga wannan lamarin daya faru harya sakata cikin damuwa,

Sosai ta canja a kwanakin kwata kwata ta sake kame kanta sosai ta maida kanta a matsayinta na 'yar Aiki Mara gata ko mutuncin dayafi na Hakan,

Ta yarda cewan 'dan wani Baya taba zama 'danka duk da tanajin radadin raba kanta da tayi da Aqeel Amma Hakan shine kwanciyar hankali da mutuncin kowa duk da tasan bawa mutuncin take dashiba a gidan..

Tsakaninta dashi share Masa sashensa ta gyara takai Masa abincin ta jere saita komawarta cikin masu aikin gidan Yan uwanta.

Hakan Yana tsananin cizon ransa Dan hakama yake sake Jin nutsuwar shawartarta akan auren idan har zata aminta sbd rayuwarta ta inganta dan kuwa Allah bazai barsuba dagashi har mahaifiyarsa harma da umma Idan har suka Bari rayuwarta ta qare ahakan batareda sun Bata damar aure ta samu daidai iya nata farin cikinba.

Bai tuntubi Mamin da zancenba saida safe guraren 10 zuwa 11 haka Bayan tagama gyare koina na bangarensa zata fice ya fito daga bedroom dinsa sanye cikin casual wears qafafunsa sanyeda black footwears marasa nauyi na yawo cikin Palo da daki.

"Mami" Kai tsaye yakira sunanta Yana qarasowa tsakiyar palon inda ta tsaya tareda waiwayowa ahankali ta kellesa cikin yanayi na alamar akwai wani aikin ne?

Qarasowa yayi gabanta Yana kallon kyakkyawar fuskarta da sai yanzu yake ganin diban kamanninta da ummansa
Ahankali ya Kai hannunwan duka biyu ya kamo nata hannuwan Yana sake kallonta cikin kulawa da kauna irin ta uwa da 'da yace"

Mami Ni meye nawa da laifin maganar umma zai shafeni?
Tafiya fa zanyi zuwa farkon nxt year
Idan kina shareni haka bazan iya tafiyar nanba gaskia.

Kallonsa tayi Jin yanda Yar shagwaba take cikin sautin muryarsa
Duk saiya tuna Mata lokacinda yake yaronsa...

Sanyi jikinta yayi duk da tanajinsa cikin ranta fiyeda kowa Amma kuma kusancin nasu Yana neman zama damuwa ga kowa Dan haka har cikin ranta ta dangana zata danne zuciyarta akansa bawai Dan Bata son 'dan nata ba sai Dan mahaifiyarsa dake ganin kamar ta rabata da danta data Haifa abinda.

Janta yayi ahankali ya zaunar kan kujera cikin kulawa tareda zaunawa gefenta hannunta daya yasake riqewa ya Dan sauke numfashi tareda nutsuwa ya kalleta.

Take tagane maganar dazaiyi Mai mahimmanci ce Dan haka ta dauke kallonta daga Kansa Tana sauraron abinda zai fada.

Mami aure nakeson kiyi kamar umma..

A bazata taji sakar zancen cikin kunnuwanta.

Kasa kallonsa tayi sbd Bata Kama zancenba Tunda dai yafi kowa sanin Hakan kamar abinda bazai yiyu bane gareta,

Ina mijin?
Waye zai aureta tagama fita layin budurwai?
Waye zai Bata gatan yin auren? Sbd tasan Haj maryamah ba lallai ta Bari ba,
Ina ita Ina wannan gata da rufin asirin..

Ganin zancen bai shigetaba yasashi sake fuskantarta yakuma Kiran sunanta'

"Mami da gaske nakeyi Aure nakeson kiyi,.

Juyowa tayi wannan karon Tana kallonsa da alama kosawa da zancen Dan tasan ana maganar aure ne a inda akeda miji Kuma Idan har zaka auru kenan.

Kai tsaye yace'

" Mami Zaki yarda babana Malam Sanda ya aureki?

Nine waliyinki Kuma na aminta da Hakan idan kin yarda.

Kasa magana tayi sbd maganar tasa tafara girmama da Bata tsoro,

Aure Kuma?
Ita din ce zatayi aure?
Dama akwai ranarda sunanta Dana aure zai Hadu Koda da raha ne?

Duk da tasan Hakan ba lallai Abu Mai yiyuwa bane saidai kuma yanda Aqeel din ya tattara nutsuwarsa akan maganar yasata kasa cewa komai.

Tabbas da tanada ikon kanta a gidan dakuma gurin tafiya da tafiyarta zatayi sbd tasan fitinar da zaayi idan wannan zancen na Aqeel ya bayyana,..

Haj maryamah ba qaramin bacin rai zata shigaba Amma Kuma a yanzu da Aqeel din yake maganar tareda magiya sosai yasa takasa cewa komai bare ta musa masa,

Wannan Wace irin sabuwar qaddarar ce Kuma?

Zamewa tayi ta tafi tabar Aqeel din Yana sake binta da magiya qarshe dai dakinta Takoma ta zauna tareda rafka taguma Tana tunanin abubuwa da Dama.

Shi Kansa malam Sanda din dayakeson aura Mata kamar yafi qarfinta sbd yanada rufin asirinsa,
Tsaftataccen malami kyakkyawan bafulatani Mai haiba shine zai bige da aurenta ita data Gama rasa kanta a mace,

Wahala da aikin wuta duk yagama dafar da fatarta ta rasa kyanta na mace,
Duk wani adon da mace ke buqata Babu daya data samu Bayan kitso wadda shima matar Maigadin gidan Dan majalisar dake kusa dasu itace take Mata wanda shima sbd tsaftar abincinsu yasa Haj maryamah ta lamunce Mata zuwa.

Da gaggawa ta kori tunanin zancen Auren dayake neman shigarta sbd kaucewa fada da gorin da zatasha dagasu umma da Haj maryamah sbd zaa ce itace ta kitsawa Aqeel din zancen.

Tattara zuciyarta tayi guri daya ta dangana ta dauki qaddarar da Allah yariga ya qaddaro Mata Dan haka kwana biyu tayita kaucewa Aqeel kadaicewarsu sbd kada yasake tayar Mata da zancen Amma kamar a banza sbd Hakanan yanzu daya riga ya furta tareda qudurta zancen sai yakejin idan ba auren sukaiba hankalinsa bazai kwantaba....

Ganin Mamin tasa batada niyar amincewa hankalinsa ya tashi sosai ya dage tareda hanata sukuni da magiyarsa Wanda yasata shiga mamaki da tsoron ganin yanda ya qwallafawa ransa maganar auren Dan harkomawa yayi kamar zai zauna yayi Mata kuka Dan kuwa har cikin tsakiyar ransa yakejin so da buqatan auren nata da Malam Sanda.

Batada zabi ko qwarin gwiwar hanawa Aqeel dinta abinda yakeso Dan haka ta amince Bayan tashiga tsoro da fargaban abinda zai biyo baya sosai.

Kafin ta amince sharadin sai idan mahaifiyarsa ta amince tukuna zatai auren idan Haj maryamah Bata amince bazataiba.

Baibi takan shawartar Haj maryamah ba Kai tsaye yayiwa malam Sanda tayin auren Mamin tasa tareda rokonsa akan amincewarsa bawai Dan komaiba sai Dan kamar Yana rokonsa ne ya zama gatan Maminsa alokacinda baya Nan.
Chapter 12 · 0% Book details