← Book details Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 95

Sashe 16

Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayani sukai Masa na cewan preterm labor ce maana haihuwa a wata bakwai din zata sbd matsalolin da cikin yasamu gashi bai kaiba.

Da sauri ya juya ya nufi gurin motarsa saikuma ya tsaya sbd yasan Babu inda zai samu shago a lokacin.

Dawowa yayi Yana jiran afito sallar asuba dasuke kokarin Shiga shima yai alwala ya Shiga masallacin.

Ana idarwa sama sama yayi adhkar ya fito ya ja mota ya nufi gidan tsohon driver din Dadynsa da yanzu shagone dashi na siyarda Kaya.

Aminu na masallaci Aqeel yazo nemansa Dole ya dauko mukalullan shagonsa suka nufi shagon ya bude ya basa kayanda yake buqata
Shima Dole transfer yayi Masa Dan Babu cash a jikinsa,
Allah Kuma sai yasa shagon nasa baa sakuwa yakeba da Babu Wanda zai bude musu kasuwar alokacin.

Koda ya dawo asibiti da siyayyar kayan baby masu yawa sosai har Allah yasa Zainab din ta haihu lafiya ta samu baby girl wato 'ya mace saidai babyn batada qwari ko kadan Dan Haka Yana kawo kayan aka Danyi Mata Shiri aka sakata cikin babys incubator da ake aje jarirai irinta.

Da farko tsoro yaji Jin babyn na cikin kwalba Amma Kuma sun Masa iya bayaninda zai gane yakuma ganar da mamarsa kamar yanda suke tunani.

Bacci Mamin tasamu bayan magani da allurai tareda tea Mai zafi datasha Dan Haka sai alokacin yasamu ya tafi gida guraren 9 na safe kenan.

Gidansu ya nufa direct sashen mahaifiyarsa ya nufa ya taddata zaune akan dining Tana breakfast a shirye cikin shigar dake nuni da fita zatayi.

Qarasowa yayi jiki a mace yana gaidata ya zauna kan dining din ya zuba ruwan zafi Yana hada tea.

Kallonsa tayi lokacinda yake Shan tea din ahankali cikin sanyi da nutsuwa tinaninsa nakan Maminsa.

Zatayi magana ya dago ya kalleta cikin nutsuwa yace"

Umma Mami ta haihu da asuba yau Amma babyn is not okay Tana incubator..

Kallonsa tayi cikeda mamakin Dama Zainab cikin da aka fada gaskia ne harya tsufa da haihuwa yanzu haka..
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
13
Cikin dan boye mamakinta tareda kokarin basar da tsananin fushi da bacin ranta akansa na tun jiya daya kasa ko daukan wayarta Sam yaqi lokacinta..,

Ahankali tace,

"Allah ya raya abinda tasamu din,
Jaime kuma yau ya kamata kazo kasan abinda duk Zakayi kasan dai zuwa Jibi zaka wuce.

Numfashi yadan sauke kadan yana cewa,

"Ummn insha Allah zan samu time naga yanda zan qarasa sauran shirin nawa.

Miqewa yayi daga zaman da yayi yabar gurin
Kai tsaye mai aikin gidan yakira ya bata umarnin hada breakfast lafiyayye a basket tukuna ya wuce bangarensa.

Tubewa yayi ya zari towel qarami ya rataya a wuyansa daga shi sai Qaramin boxers ya nufi toilet.

Wanka yayi yafito ya shirya Kansa na tsananin sarawa da alamarma idan ya kwanta zazzabi shigarsa zaiyi
Gaishi da komaima a gabansa yana neman rikice masa dan kuwa a yanzu da maminsa tayi irin wannan haihuwar bazai iya tafiya yabarta ba,

Ga rasuwar Mijinta,
Ga haihuwar bagatan,
Ga babyn na incubator
Tayaya zai tafi yabarta a wannan yanayin bayan yasan babu Wanda zai iya kular masa da ita.

Cikin black qananun kaya yafito yasa samira takai masa basket din mota ya fice daga gidan Kai tsaye batareda yaje gurin ummansaba tasan da fitar tasa dan zata iya kawo masa wani uzurin dazai hanasa fitar.

Koda yakoma asibiti Maminsa ta tashi tana zauna fes cikin wasu kayan da alama sun taimaka mata tayi wanka ta sake shiryawa

Fuskarta ya kalla yaga babu walwala ko farin ciki saima sake shiga damuwa da tsoron babynta kada itama ta rasata,

Tea ya hada mata dakansa ya zauna gefenta yana kallonta cikin tsananin kulawa da bata tabbaci yace,

"Mami kada ki taba yankewa kanki rahama dan rahamar ubangiji bata yankewa,
Ina nan,matuqar ina raye mami dake da babyn nan bazaku taba rasa gatanku ba insha Allah,
Wannan babyn zan zama gatanta,
Zan bata farin cikin da kowanne dan yake fatar samu wannan alqawarina ne idan Allah yabani tsawon rai da lafiya to tabbas nine babban yayanta kuma ubanta dazai tsaye mata a komai dan haka mami kada kisa damuwa kiyi mata adduar samun lafiya baba Malam kuma adduar samun rahamar ubangiji.

Da yake kukanta ya qafe qyam baya zuwa tun jiya dan haka bata iya cewa komaiba saima Jin nauyin zuciyarta daya qaru duk da alqawarin da Aqeel din yayi mata akan future din 'yarta sai hakan ya sata shiga fargaba idan aqeel din ya tafi kafin yadawo waye sukedashi.

"Allah",zuciyarta ta tinatar da ita

Daqyar ta iya cin abincin daya tilasta mata ci dan daga bakinta har maqoshinta zuwa cikinta abincima kamar yankar matasu yakeyi a halinda take ciki.

Bayan tagama akace zaa kawo mata abubuwan da zata ja Nono zaa je abawa babyn.

Aqeel ne yakuma bada kudi aka siya komai aka kawo mata nurses biyu suka taimaka mata aka dan samu nono shima daqyar da wahala.

Neman alfarmar ganin babyn Aqeel yayi suka tafi tare harda Mamin wadda take tafiya a hankali sbd rashin karfi da damuwar data gama ci da mamaye kuzarinta.

Suna isa saida aka dauki mintina kafin nurse ta fito da babyn kointa a rufe dunqule cikin tattausan bargo mai tsada da kyau pink ta miqawa Aqeel din ita.

Nauyi yaji zuciyarsa tayi lokacinda aka miqo masa babyn saida ya sauke numfashi boyayye kafin ya miqa hannayensa ya Karbeta cikeda tsananin so da Kaunarta tun baiga fuskartaba.

Gefen mamin ya dawo ya zauna tareda dan bude musu babyn suna zubawa 'yar qaramar fuskarta idanuwansu kowanne cikeda Kauna da tausayin tazo duniya a marainiya.

Wani numfashi mai zafi da qunci Zainab ta sake tareda  Dagowa ta kalli Aqeel daya kasa dauke idonsa akan babyn Ahankali ta iya furta,

"Aqeel kai kadai takeda kayi mata huduba da suna..

Dama abinda yake shirin yi kenan saidai sunan dayake Ransa yana fatar idan ya saka hakan yasa kaunar babyn yashiga ran mai sunan...

Ahankali ya dagota sama yakawo daidai fusktarsa yayi mata huduba tareda kiranta da sunan MARYAMAH..

Kallon maminsa yayi alokacinda ya furta sunan daya sakawa babyn a fili...

Batace komaiba kamar yanda har cikin ranta bataji komaiba na damuwa ko rashin jin dadin sunan,
Har a ranta sunan yayi tunda shine ya zaba sunan,
Kuma sunan yar uwarta ne Jininta da bata da kowa sai ita da yayanta da suka zama biyu yanzu wato AQEEL da MARYAMAH.

Hannu nurse ta miqa masa Akan ya bada babyn a maida ya maida kallonsa kan babyn yana kallon fuskarta cikeda kulawa da kauna,
Hakanan yakejin kamar idan ya bada MARYAMAH din ya Rabu da ita kenan.

Miqata yayi bayan ya sake rufeta koina kamar yanda aka kawo musu ita.

Dakin da maminsa take suka koma ko zama baiyiba ya fito yaje ya biya kudin komai da komai harna sallama dan haka babu abinda zasu Nema har ayi sallamarsu insha Allah.

Daga can gida yakoma sbd kiranda ummansa ke masa.

Yana isa ta rufesa da fada amma dai bayan hakura baice mata komaiba saima maganar data daga hankalinta dan saura kiris ta some.

Cikin tashin hankali sabo
Da mamakinsa mai tsanani tace,

"Aqeel kace bazaka tafi UK ba ka fasa???
Sbd Zainab ne ko????

Sam rayuwarsa bai iya qaryaba da wani kwana kwana dan haka cikin nutsuwarsa kai tsaye yace,

"Umma bazan iya Barin mami da Little MARYAMAH ba natafi,
Kona tafi wlh hankalina zai rabu
Inaga gwara na tsaya nan din kawai zaifi mun nutsuwa........

Tsabar baqin ciki da takaici bata tsaya tambayar sauran zantukan nasaba sai sunan daya ambata
A qule tace,

"Wace sabuwar shigowar aka samu little MARYAMAH kuma?

Bata buqatan yace mata yar Zainab yasawa sunanta dan haka Ta zuba masa idanuwanta tana jiran amsar dazai bata dan bacin ranta qaruwa yakeyi da komaima ayanzu idan har Aqeel yafasa tafiya Akan zainab wlh wannan karon ba qaramin fushi da bacin ranta zaa ganiba.

"Umma yar maminace da wannan sunan
Bakuma lafiyayya bace tayaya zan barsu natafi waye zai kula dasu?
Maganar tafiyata kuyi hakuri umma abarta sbd bazan iyaba.....

Kofa ta nuna masa da hannu Tana kokarin danne zuciyarta daga furta kalamanda basu daceba ga 'danta.

Yana fitowa bangarensa ya nufa ko zama baiyiba kiran Haj kaka yashigo wayarsa dan haka ya juya ya fice zuwa gidan haj kakan,
Yana isa haj maryamah na isowa nan take sabon rikici ya tashi qannan babansa ma su uku maza duka sun saka bakinsu a maganar amma Aqeel din ya tsaya cak akan bazai bar zainab da MARYAMAH su tagayyara.

Duk yanda ake tunanin kusanci,shaquwa da girman kaunar dayakewa Zainab wannan karon sun tabbatarda abin ya wuce tinaninsu dan haka hankali ya tashi cikin kwana daya lamarin ya zama babba dan kuwa su dangin mahaifinsa duka tsananin laifin  haj maryamah suke gani Dan itace tayi watsi da 'dan ta Barwa zainab din har Aqeel din yazo gashinan idanba zainab da baya Jin kowa a ransa,

Umma tayita kiran wayar Zainab din yafi so dari da dori amma bata samu dan haka takejin kamar ta zama tsuntsuwa tazo ta samu zainab tayi mata duka,

Sun rabu da ita kowa ya kama rayuwarsa amma takasa barin yar uwarta taji dadin rayuwarta da 'danta
Yanzu gashinan itama ai ta Haifa tata yar tabarsa da tasa uwar taqi.

Hannuwansu su haj kaka suka cire sbd duk yanda sukeson tafiyarsa karatu sunfison farin cikinsa akan nasu dan haka suka hakura Akan yanda yakeso din kuma suka amince da yaci gaba da kulawa da zainab da MARYAMAH..

Jin hakan yasa zuciyar haj Maryamah bugawa qarshe dai saida aka hada da Kaita asibiti dan kuwa jininta yayi mugun hawan data kusa samun matsala.

Umma dataga zasuyi biyu babu sai gata ta iso ba shiri gashi da a ranar zai wuce Abuja Gobe su wuce UK din.
Chapter 16 · 0% Book details