Sashe 10
Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_KUNSAN DUK INDA ABUBUWAN ARZUKA SUKE MUNA SHIGA MU KURDA MU NEMO MUKU SU DOMIN JIN DADIN KU..🥰💕SABODA KU DIN NA GABAN GOSHINAN MU NE._
_TAMKAR KO DA YAUSHE.. YAU MA MUNZO MUKU DA WATA TSARABAR.. TSARABAR DUNIYAR KAYAN KITCHEN, DECORATIONS DA SAURAN SU… KU MARMATSO KU JI…_
*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*
_KUN GANI KO? TO INA AMAREN? INA UWAYEN GIDAH INA YAMMATAN DA KE SHIRYE SHIRYEN SHIGA DAGA CIKI? INDA ZAKU JE KU KANKARO MUTUNCI KU DANDALO ARZIKI NA KECE RAINI.. INDA ZAKU WUCE RENI DA GANIN KASKANCI..INA MAZAN DA KE BURIN FARANTAWA MATAN SU DA ‘YAYAN SU DA KANNEN SU? _
_MAAB LUXURY HOME: RIGIJI GABJIN KENAN! WOHOHO WANI KAYA SAI AMALE KAN DAUKA.. MAAB LUXURY HOME : ALJANNAR KAYAN KITCHEN KENAN, INDE AKACE KAT TOH KARSHEN MAGANA TA KARE KENAN.. MAAB LUXURY HOME ; A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY KITCHEN UTENSILS, HOME DECORATIONS AND MUCH MORE_
_ADIRESHIN MU: MUNA KAN TITIN AHMADU BELLO WAY, KANO STATE. ZAKUGA TAMBARIN DA MAAB LUXURY HOME.._
_DAN SAUKAKA MAKU FITA ZUWA SHAGON MU. ZAKU IYA ORDER AKAWO MUKU DUKKANIN INDA KUKE A FADIN NIJERIYA DA KETARE. _
_INSTAGRAM: @maabluxuryhome._
_FACEBOOK: @maabluxuryhome._
_KO KU NEME MU TA LAMBAR TARHON MU: 08034631010_
_KYAU! INGANCI! RAHUSA! ADADE ANA AMFANI DA SHI SAI KAYAN: MAAB LUXURY HOME_
_100% TESTED AND TRUSTED😍☑️_
______
********
Tun Haj maryamah na tafiyenta da basa wuce kwanaki zuwa satittika yanzu wasu lokutan takanyi doguwar tafiya qasashe Wanda suna share wata daya,biyu,uku,har fiye Basu gantaba,.
Ana cikin hakan Wani aminin Alh Asad dayake babban Justice dake Abuja ya fito neman auren,
Da farko Bata aminta ba Amma ummanta da hajiyar su Alh Asad suka tilastata tareda nasihu tukuna ta amince akai auren Amma shi Yana can Abuja da iyalinsa itama yabata ware Mata nata gidan Amma Bata wani zama sai can can idan taje abujar ta Dan zauna tayi kwana biyu kokuma idan shi yazo Mata
Haka dai aure yake kamar Wadda akaiwa Dole a auren
Shima Justice Ayub Nasir din bai wani damuba sbd sanin uzurirrikanta da Kuma dama shima baya wani som zama.
Ita Kuma Zainab Hakan yasa ta sake dagewa sosai gurin tarbiyantar da Aqeel Wanda yaketa qara girma Yana cigaba da karatunsa Tunda yazama dai itace tamkar uwa Kuma ubansa.
Aqeel Kyakykyawar Yaro ne Mai nutsuwa da rashin son shiga cikin mutane sosai bare Wasa cikin yara 'yan uwansa,
Kasancewar yanayin yanda rayuwar tasa ta taso yasa yake shiru shiru mara son hayaniya,
Baida mahaifin dazai tsaya masa ya zama jagorarsa,
Wadda itace ta haifesa Sam batada lokacinsa bare nuna Masa kauna da shakuwa,
Wadda yakewa kallon uwa Kuma mahaifiya agaresa Tana cikin wani irin qunci da rashin yancin Kai dazasu sake suyi rayuwarsu,
Duk gata da daular da ake kashewa gidan kamar baasan zafin nemansuba bai saka Aqeel din ya taso cikin Jin cewar ba Maminsa ce mahaifiyarsa ba shiyasa maimakon yayi rayuwar Jin dadi saima yake rayuwar kadaici kaman Maminsa suna rayuwarsu da Jin basa buqatar komai
Ita Zainab batada wani buri ko kwadayi bare shaawar wata rayuwar,
Ko Aqeel dinta aka Barta dashi baa rabasuba batada doguwar damuwa.
Dukkanin wahalar da ta sha tun yana ƙarami har kawo yanzu da ya fara zama babba bata taɓa jin daidai da rana ɗaya ta gaza ko ta gaji da hidimarsa ba,
Shi AQEEL Yaro ne me tsananin son a kula dashi tareda lallabasa,
Hakan wata dabi'arsa ce data lura ta fahimta tun Yana qanqani shiyasa tafi basa mahimmanci da kulawa fiyeda komai a gidan.
Duk masu aikin da ake kawowa gidan basa wani zama tafiyarsu sukeyi sbd dagasu sai Zainab
Aikin kawai akeyi Babu Mai gidar gashi duk da batanan aikin Babu Wanda aka Dena saima qaruwa Dan kuwa har kullum baa Dena karatu a gidanba saima qaruwa da jamaa sukai kusan duk manya Yan anguwar dake karatun da 'yayansu manya a gidan Malam Sanda ke basu karatun kullum tsakanin magriba zuwa ishai,
Hakama dangin Alh Asad maza kusan dukkaninsu anan gidan ake karatun dasu kullum Wanda sbd sakawa rayuwar gidan ido yasa suka maida sallar magriba dinsu zuwa ishai anan suma suna qaruwa da karatun.
Duka wannan lamarin dayake faruwa a rayuwar gidan har tsawon wannan lokacin babu Wanda yasan Zainab jinin Haj maryamah dince
A matsayin me Aiki suka santa tun kuruciya har kawo yanzu data girma zama mace shiyasa Babu Wanda yake ganin girma ko wani mutuncinta saima mayyar kwadayayya dasuke kallonta Dan uwar wahalar datakesha suna ganin kwadayi kawai zaisa ka zauna irin wannan rayuwar.
Shi Kansa Aqeel baisan qanwar mahaifiyarsa bace,
A taqaice baisan sun hada jini da itaba saninsa Mai aikin gidance
Shikuma uwace agaresa.
Qarin abinda yasa wasu masu aikin da Dama dasuke tafiyarsu shine duk wahala da biyayyar Zainab Haj maryama Bata yabawa bare nuna wani Jin dadi sai jikinsu na mutuwa da tsoron Hakan,
Wasu Babbar sata suke zubawa su gudu wasu Kuma salin alin suke tafiyarsu Dan Zainab dasuke karkashinta meta zama duk shekarun bare suda abin duniya suka fito nema ba Wai zaman bautar banza ba.
Babban abinda yaqara saka Haj maryamah yiwa Zainab tsanani akan rashin barinta fita shine gudun tasamu mijin aure a lokacin tayi aure tabar Aqeel Wanda tasan bazai taba zamaba Zainab ta tafi tabarsa
Tasani Sarai bin Zainab din zaiyi Koda zata hauka ne akan bataso tasan saiyabi Zainab
Itakuma bazata iya Bari danta yayi rayuwa a qazamtaccen guriba.
Sabuwar dabia Mai karfi data shigeta shine tsanar duk wani Abu daya shafi gwagwarmaya da mutanen daba nagartattuba...
Ta tsani zuwa ko irin guraren dasuka shafi irin Hakan shiyasa ma gidanta yasake samun tsaro da dokoki
Ko masu aikin da ake kawowa batason wadda Alama ta nuna tagama lalacewa da sanin maza,
Sam Bata kaunar irinsu
Qyanqyaminsu takeyi tareda musu fatar shiriya daga nesa shiyasa duk tsanani idan Tana gida batacin abincin kowa saina Zainab itama sbd tanada tabbacin tsarkinta da tsaftar rayuwarta da Bata gurbata tako Ina.
Rayuwarsu tafara sauyawa ne lokacinda haj Maryamah ta nemawa Aqeel wata tsadaddiyar makarantar boarding Amma Kai tsaye yaqi yarda da makarantar bakuma sbd kowa yaqi makarantarba sai Dan Maminsa wadda yasan wanu gata da sanyin datake ji duk sbd shine Dan haka akai akai Amma yaqi yarda.
Kiran Zainab Haj maryamah din tayi tai fada sosai tareda cewa lallai saita rarrashesa tasa ya amince ya tafi makarantar Dan tariga ta kashe maqudan kudi sosai akan karatun nasa.
Da farko Zainab rarrashinsa tayi tareda nasihu da Jan hankali iri iri Amma Sam yaqi yarda
Duk da bai fadaba itama tasan sbd itane
Qarshe dabai yardaba hakura tayi ta qyalesa Dan Bata son takura Masa Tunda baya gardama da duk abinda ta sakasa sai wannan karon
Dan haka bazata takurasaba Dan Jin take kamar tace a qyalesa karsu takura Masa Amma Kuma ba Dama Tunda uwar data haifesa ce take magana akansa.
Issue din makarantar yasa ran haj Maryamah baci sosai qarshe ta dorawa Zainab din lefin Bata basa tarbiya Mai kyauba tunda har zai iya qin abinda tace ita data haifesa.
Fada da bacin rai sosai akai akan maganar makarantar tasa Wanda dukanin laifin akan Zainab aka dorasa karshe kukan datake dadewa bataiba sbd bushewar da idanuwanta da zuciyarta sukayi Amma wannan karon saida ta kwana Tana kukan bacin ran da lamarin ya kawo Dan kuwa ko umma ta Kira wayarta Babu kalar fada da gorin da baayi Mata ba Hakan ta Basu hakuri Dan batada komai na fada.
Aqeel kuwa abinda sukaiwa Mamin yasa yace bazai taba zuwa makarantar ba Dan farko harya fara sauka akan zaije din ganin Maminsa nata lallabasa.
Tunda akai wannan tashin hankalin sai haj Maryamah tafara Jin buqatar raba danta da Zainab tun kafin lokaci ya qure Mata Dan kuwa da Alama 'danta tanaji Tana gani zai bijire Mata
Wato dai kamar Zainab ta haifawa Dan kenan.
Ita kanta Zainab sake kame kanta tayi tareda shiga taka tsan tsan sbd ganin ran su umman da Haj maryamah ya baci sosai.
Aqeel baije boarding school dinba Amma Hakan daya faru yasa Haj maryamah yanke shawarar daukesa daga qasar kwata kwata zuwa wata qasar yayi karatunsa acan sbd da gaske take buqatar rabasa da Zainab yanzu sbd zuwa yanzuma tsoron irin kaunar dayakewa Zainab din takeyi Dan kuwa yafara maganar abawa Zainab qananun abubuwa zuwa gaba yayi girmanda zai karba dukiyarsa ta tabbatarda zai iya mallakawa Zainab komai nasa data Gama yawo da wahalar kular Masa da kare Masa.
Ta bangare daya malam Sanda ne ya zama malami na musamman ga Aqeel tareda cusa Masa akidu na so da kaunar karatun addnini sosai sbd harda shi acikin burikan mahaifinsa akansa,
Mahaifinsa yanada tsananin shaawa da buqatan 'dan nasa yasan Addininsa sosai yayi zurfi acikinsa Dan haka ahankali sai shima Aqeel din Hakan ya shigesa yafara zama Mai tsananin son addini da karatunsa sosai.
Yana karatun bokonsa Kuma Yana na addinin sosai,
Kokarinsa da nutsuwarsa akan Hakan yasa malam Sanda maida hankali gabaki daya akan Aqeel din Dan cika burin Alh Asad dakuma Dan samun qarin Wanda addnini zai qaru dashi.
Ahankali shaquwarsa da malam Sanda tayi zurfi sosai har yake Masa kallon mahaifi sbd shima ya manyanta yazama dattijo mai nutsuwa sbd ilimin addini daya ratsasa,
Sam baya tsallake maganar malam Sanda sbd ba qaramin girmansa yake ganiba musammam daya kasance ta wani bangaren kamar shi kadaine Bayan Maminsa Wanda yake fahimtarsa.
Yazama matashi Mai cikakkiyar nutsuwa da kamun Kai Kuma har lokacin Babu Abu daya rage na shaquwa da girman kaunarsa da Maminsa saima abinda yayi gaba,
MUHAMMAD AQEEL ASADULLAH yazama wani irin saurayi da kallo daya zakai Masa kasan 'dan gatane daya taso cikin gata da nitsatsiyar rayuwa,
Kyakkyawane Wanda ya dauko kamannin mahaifiyarsa sak wacce itama kyakkyawar tun asalinta.
Zainab Kuma zuwa wannan lokacin sosai ta fita a sahun matasa masu 'yan shekaru Dan kuwa tazama mace sosai gashi har Haj Maryamah data girmeta nesa sosai ta fita kyan gani da jikin kuruciya sbd Hutu da Jin dadi
Itakuma wahala duk ta sauyata tasa manyancin zuwar Mata da wuri.
Har wannan lokaci Babu wani Wanda yataba sanin matsayin Zainab agun Haj maryamah acikin gidan
_TAMKAR KO DA YAUSHE.. YAU MA MUNZO MUKU DA WATA TSARABAR.. TSARABAR DUNIYAR KAYAN KITCHEN, DECORATIONS DA SAURAN SU… KU MARMATSO KU JI…_
*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*
_KUN GANI KO? TO INA AMAREN? INA UWAYEN GIDAH INA YAMMATAN DA KE SHIRYE SHIRYEN SHIGA DAGA CIKI? INDA ZAKU JE KU KANKARO MUTUNCI KU DANDALO ARZIKI NA KECE RAINI.. INDA ZAKU WUCE RENI DA GANIN KASKANCI..INA MAZAN DA KE BURIN FARANTAWA MATAN SU DA ‘YAYAN SU DA KANNEN SU? _
_MAAB LUXURY HOME: RIGIJI GABJIN KENAN! WOHOHO WANI KAYA SAI AMALE KAN DAUKA.. MAAB LUXURY HOME : ALJANNAR KAYAN KITCHEN KENAN, INDE AKACE KAT TOH KARSHEN MAGANA TA KARE KENAN.. MAAB LUXURY HOME ; A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY KITCHEN UTENSILS, HOME DECORATIONS AND MUCH MORE_
_ADIRESHIN MU: MUNA KAN TITIN AHMADU BELLO WAY, KANO STATE. ZAKUGA TAMBARIN DA MAAB LUXURY HOME.._
_DAN SAUKAKA MAKU FITA ZUWA SHAGON MU. ZAKU IYA ORDER AKAWO MUKU DUKKANIN INDA KUKE A FADIN NIJERIYA DA KETARE. _
_INSTAGRAM: @maabluxuryhome._
_FACEBOOK: @maabluxuryhome._
_KO KU NEME MU TA LAMBAR TARHON MU: 08034631010_
_KYAU! INGANCI! RAHUSA! ADADE ANA AMFANI DA SHI SAI KAYAN: MAAB LUXURY HOME_
_100% TESTED AND TRUSTED😍☑️_
______
********
Tun Haj maryamah na tafiyenta da basa wuce kwanaki zuwa satittika yanzu wasu lokutan takanyi doguwar tafiya qasashe Wanda suna share wata daya,biyu,uku,har fiye Basu gantaba,.
Ana cikin hakan Wani aminin Alh Asad dayake babban Justice dake Abuja ya fito neman auren,
Da farko Bata aminta ba Amma ummanta da hajiyar su Alh Asad suka tilastata tareda nasihu tukuna ta amince akai auren Amma shi Yana can Abuja da iyalinsa itama yabata ware Mata nata gidan Amma Bata wani zama sai can can idan taje abujar ta Dan zauna tayi kwana biyu kokuma idan shi yazo Mata
Haka dai aure yake kamar Wadda akaiwa Dole a auren
Shima Justice Ayub Nasir din bai wani damuba sbd sanin uzurirrikanta da Kuma dama shima baya wani som zama.
Ita Kuma Zainab Hakan yasa ta sake dagewa sosai gurin tarbiyantar da Aqeel Wanda yaketa qara girma Yana cigaba da karatunsa Tunda yazama dai itace tamkar uwa Kuma ubansa.
Aqeel Kyakykyawar Yaro ne Mai nutsuwa da rashin son shiga cikin mutane sosai bare Wasa cikin yara 'yan uwansa,
Kasancewar yanayin yanda rayuwar tasa ta taso yasa yake shiru shiru mara son hayaniya,
Baida mahaifin dazai tsaya masa ya zama jagorarsa,
Wadda itace ta haifesa Sam batada lokacinsa bare nuna Masa kauna da shakuwa,
Wadda yakewa kallon uwa Kuma mahaifiya agaresa Tana cikin wani irin qunci da rashin yancin Kai dazasu sake suyi rayuwarsu,
Duk gata da daular da ake kashewa gidan kamar baasan zafin nemansuba bai saka Aqeel din ya taso cikin Jin cewar ba Maminsa ce mahaifiyarsa ba shiyasa maimakon yayi rayuwar Jin dadi saima yake rayuwar kadaici kaman Maminsa suna rayuwarsu da Jin basa buqatar komai
Ita Zainab batada wani buri ko kwadayi bare shaawar wata rayuwar,
Ko Aqeel dinta aka Barta dashi baa rabasuba batada doguwar damuwa.
Dukkanin wahalar da ta sha tun yana ƙarami har kawo yanzu da ya fara zama babba bata taɓa jin daidai da rana ɗaya ta gaza ko ta gaji da hidimarsa ba,
Shi AQEEL Yaro ne me tsananin son a kula dashi tareda lallabasa,
Hakan wata dabi'arsa ce data lura ta fahimta tun Yana qanqani shiyasa tafi basa mahimmanci da kulawa fiyeda komai a gidan.
Duk masu aikin da ake kawowa gidan basa wani zama tafiyarsu sukeyi sbd dagasu sai Zainab
Aikin kawai akeyi Babu Mai gidar gashi duk da batanan aikin Babu Wanda aka Dena saima qaruwa Dan kuwa har kullum baa Dena karatu a gidanba saima qaruwa da jamaa sukai kusan duk manya Yan anguwar dake karatun da 'yayansu manya a gidan Malam Sanda ke basu karatun kullum tsakanin magriba zuwa ishai,
Hakama dangin Alh Asad maza kusan dukkaninsu anan gidan ake karatun dasu kullum Wanda sbd sakawa rayuwar gidan ido yasa suka maida sallar magriba dinsu zuwa ishai anan suma suna qaruwa da karatun.
Duka wannan lamarin dayake faruwa a rayuwar gidan har tsawon wannan lokacin babu Wanda yasan Zainab jinin Haj maryamah dince
A matsayin me Aiki suka santa tun kuruciya har kawo yanzu data girma zama mace shiyasa Babu Wanda yake ganin girma ko wani mutuncinta saima mayyar kwadayayya dasuke kallonta Dan uwar wahalar datakesha suna ganin kwadayi kawai zaisa ka zauna irin wannan rayuwar.
Shi Kansa Aqeel baisan qanwar mahaifiyarsa bace,
A taqaice baisan sun hada jini da itaba saninsa Mai aikin gidance
Shikuma uwace agaresa.
Qarin abinda yasa wasu masu aikin da Dama dasuke tafiyarsu shine duk wahala da biyayyar Zainab Haj maryama Bata yabawa bare nuna wani Jin dadi sai jikinsu na mutuwa da tsoron Hakan,
Wasu Babbar sata suke zubawa su gudu wasu Kuma salin alin suke tafiyarsu Dan Zainab dasuke karkashinta meta zama duk shekarun bare suda abin duniya suka fito nema ba Wai zaman bautar banza ba.
Babban abinda yaqara saka Haj maryamah yiwa Zainab tsanani akan rashin barinta fita shine gudun tasamu mijin aure a lokacin tayi aure tabar Aqeel Wanda tasan bazai taba zamaba Zainab ta tafi tabarsa
Tasani Sarai bin Zainab din zaiyi Koda zata hauka ne akan bataso tasan saiyabi Zainab
Itakuma bazata iya Bari danta yayi rayuwa a qazamtaccen guriba.
Sabuwar dabia Mai karfi data shigeta shine tsanar duk wani Abu daya shafi gwagwarmaya da mutanen daba nagartattuba...
Ta tsani zuwa ko irin guraren dasuka shafi irin Hakan shiyasa ma gidanta yasake samun tsaro da dokoki
Ko masu aikin da ake kawowa batason wadda Alama ta nuna tagama lalacewa da sanin maza,
Sam Bata kaunar irinsu
Qyanqyaminsu takeyi tareda musu fatar shiriya daga nesa shiyasa duk tsanani idan Tana gida batacin abincin kowa saina Zainab itama sbd tanada tabbacin tsarkinta da tsaftar rayuwarta da Bata gurbata tako Ina.
Rayuwarsu tafara sauyawa ne lokacinda haj Maryamah ta nemawa Aqeel wata tsadaddiyar makarantar boarding Amma Kai tsaye yaqi yarda da makarantar bakuma sbd kowa yaqi makarantarba sai Dan Maminsa wadda yasan wanu gata da sanyin datake ji duk sbd shine Dan haka akai akai Amma yaqi yarda.
Kiran Zainab Haj maryamah din tayi tai fada sosai tareda cewa lallai saita rarrashesa tasa ya amince ya tafi makarantar Dan tariga ta kashe maqudan kudi sosai akan karatun nasa.
Da farko Zainab rarrashinsa tayi tareda nasihu da Jan hankali iri iri Amma Sam yaqi yarda
Duk da bai fadaba itama tasan sbd itane
Qarshe dabai yardaba hakura tayi ta qyalesa Dan Bata son takura Masa Tunda baya gardama da duk abinda ta sakasa sai wannan karon
Dan haka bazata takurasaba Dan Jin take kamar tace a qyalesa karsu takura Masa Amma Kuma ba Dama Tunda uwar data haifesa ce take magana akansa.
Issue din makarantar yasa ran haj Maryamah baci sosai qarshe ta dorawa Zainab din lefin Bata basa tarbiya Mai kyauba tunda har zai iya qin abinda tace ita data haifesa.
Fada da bacin rai sosai akai akan maganar makarantar tasa Wanda dukanin laifin akan Zainab aka dorasa karshe kukan datake dadewa bataiba sbd bushewar da idanuwanta da zuciyarta sukayi Amma wannan karon saida ta kwana Tana kukan bacin ran da lamarin ya kawo Dan kuwa ko umma ta Kira wayarta Babu kalar fada da gorin da baayi Mata ba Hakan ta Basu hakuri Dan batada komai na fada.
Aqeel kuwa abinda sukaiwa Mamin yasa yace bazai taba zuwa makarantar ba Dan farko harya fara sauka akan zaije din ganin Maminsa nata lallabasa.
Tunda akai wannan tashin hankalin sai haj Maryamah tafara Jin buqatar raba danta da Zainab tun kafin lokaci ya qure Mata Dan kuwa da Alama 'danta tanaji Tana gani zai bijire Mata
Wato dai kamar Zainab ta haifawa Dan kenan.
Ita kanta Zainab sake kame kanta tayi tareda shiga taka tsan tsan sbd ganin ran su umman da Haj maryamah ya baci sosai.
Aqeel baije boarding school dinba Amma Hakan daya faru yasa Haj maryamah yanke shawarar daukesa daga qasar kwata kwata zuwa wata qasar yayi karatunsa acan sbd da gaske take buqatar rabasa da Zainab yanzu sbd zuwa yanzuma tsoron irin kaunar dayakewa Zainab din takeyi Dan kuwa yafara maganar abawa Zainab qananun abubuwa zuwa gaba yayi girmanda zai karba dukiyarsa ta tabbatarda zai iya mallakawa Zainab komai nasa data Gama yawo da wahalar kular Masa da kare Masa.
Ta bangare daya malam Sanda ne ya zama malami na musamman ga Aqeel tareda cusa Masa akidu na so da kaunar karatun addnini sosai sbd harda shi acikin burikan mahaifinsa akansa,
Mahaifinsa yanada tsananin shaawa da buqatan 'dan nasa yasan Addininsa sosai yayi zurfi acikinsa Dan haka ahankali sai shima Aqeel din Hakan ya shigesa yafara zama Mai tsananin son addini da karatunsa sosai.
Yana karatun bokonsa Kuma Yana na addinin sosai,
Kokarinsa da nutsuwarsa akan Hakan yasa malam Sanda maida hankali gabaki daya akan Aqeel din Dan cika burin Alh Asad dakuma Dan samun qarin Wanda addnini zai qaru dashi.
Ahankali shaquwarsa da malam Sanda tayi zurfi sosai har yake Masa kallon mahaifi sbd shima ya manyanta yazama dattijo mai nutsuwa sbd ilimin addini daya ratsasa,
Sam baya tsallake maganar malam Sanda sbd ba qaramin girmansa yake ganiba musammam daya kasance ta wani bangaren kamar shi kadaine Bayan Maminsa Wanda yake fahimtarsa.
Yazama matashi Mai cikakkiyar nutsuwa da kamun Kai Kuma har lokacin Babu Abu daya rage na shaquwa da girman kaunarsa da Maminsa saima abinda yayi gaba,
MUHAMMAD AQEEL ASADULLAH yazama wani irin saurayi da kallo daya zakai Masa kasan 'dan gatane daya taso cikin gata da nitsatsiyar rayuwa,
Kyakkyawane Wanda ya dauko kamannin mahaifiyarsa sak wacce itama kyakkyawar tun asalinta.
Zainab Kuma zuwa wannan lokacin sosai ta fita a sahun matasa masu 'yan shekaru Dan kuwa tazama mace sosai gashi har Haj Maryamah data girmeta nesa sosai ta fita kyan gani da jikin kuruciya sbd Hutu da Jin dadi
Itakuma wahala duk ta sauyata tasa manyancin zuwar Mata da wuri.
Har wannan lokaci Babu wani Wanda yataba sanin matsayin Zainab agun Haj maryamah acikin gidan