← Book details Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 95

Sashe 35

Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Batason Jan zance da batawa juna da zaman sulhun lokaci Dan Haka Kai tsaye Babu boyo ko shakka ta zayyano abubuwan da ake aikatawa da sunanta wainda tasan batada alaqa ko hulda dasu ko bayanansu Bata kawoba sbd Bama yarda zaayiba dan Haka atafi ahakan..

Lauyanta ne ya karba zancen da fara bada hakuri dakuma godiyar yarda da sulhun da akai,

Kallon Haj Zainab din yayi wadda itama ta dago lokacin zatayi magana idanuwanta suka sauka akan Fuskar data sakata sarqewa da yawun bakin da zatayi magana dashi...

Tari Mai qarfi ne ya rufeta hannuwanta na daukan rawa a hankali..

Cikin kulawa da mamakin abinda ya sametan uncle Lulu ya kalleta Yana Dan tasowa da bayansa dake jingine jikin kujerar dayake kai ahankali yace,

"Yar uwa Yaya dai?
Are you ok??

Kasa magana tayi sbd tsananin da tarin ya qara sosai
Take idanuwanta suka fara ja ta dafe kirjinta tanayi..

Da sauri Barr Salahudeen ya leqa waje yace Salis yakawo Mata ruwa da sauri...

Ko awane masifaffen Hali take na dimuwa ko ciwo ko hauka
Bazata taba kasa gane AQEEL ASADULLAH ba,
Kamai girma da manyanta da zaiyi da sauyawar da zaiyi kuwa bzata taba kasa ganesaba..

To Amma meya kawo hardashi a wannan zaman?

Koma menene batada alaqa ko wani hadi dasu Dan Haka Babu amfanin tabari ya ganta,..

Rawa zuciyarta da jikinta ke dauka tareda wani irin sanyi na shekaru data Dade batajiba,

Rintse idanuwanta tayi cikin wani irin nauyi da zuciyarta ke sauka Mai qarfi,

Bata so ko buqatan sake kallonsa a yanda takeji zuciyarta na bubbugawa da da sauri da karfi.....

Tsanananta tarinta yayi Wanda ya Hadu da bugun zuciyarta dayake qarfi da sauri....take tafara neman fita hayyacinta.

Da sauri uncle Lulu ya Kamata suka miqe sbd Dole zaman ya wargaje sbd gabaki daya ta fara fita hayyacinta idanuwanta tini sukai jajir hannuwanta sai rawa sukeyi.

Kai tsaye aka miqawa lauyoyinta bayanan matsayar zancen da aka Kai Wanda akaso karantawa gaban kowa a zaman Wanda take nuqatar saka hannun amincewa Dan Haka tunda zaman ya lalace sbd zuwan tsautsayin sai aka bawa lauyoyinta daga baya ta karanta su saka hannu itada Lulu lauyyinsu su dawo dashi a miqa kotun shikenan.

AQEEL ASAD Wanda ya kasa dagowa ya kallesu sbd ba halayyarsa bace yawan kallon bare Kuma ga mace irin wannan dayaji Ana fada,

Yanada kiyaye ganinsa akan abubuwan da kallonsu zasu damu Kansa da zuciyarsa shiyasa duk abinda yasan baida mahummanci kokuma zai taba Masa nutsuwar Kansa baya kalla sbd kaucewa damuwa da ciwon kai.

Koda IDON NERA tayi nata bayanin kwata kwata Bai dagoba hakama jinsa ba sosai yake akantaba...

Miqewa sukai Lulu na gefenta Barr Salahudeen na dayan gefen da handbag dinta a hannunsa sai sannu suke jera Mata tana dafe da kirjinta dake zafi da nauyi matuqar gaske kamar zai fado...

Tana gap da kaiwa kofar ficewa data matsu tabar dakin sbd suffocating takeji....

"MAMI"

Taji Nutsatsiyar muryarsa ta sauka akan kunnuwan duka Wanda yake dakin..

Babu Wanda yajuya ya kallesa sbd tunanin waya yakeyi
Itakuma datasan menene Bata juyoba ta wucewarta Kai tsaye batareda ta nuna alamar Jin sunan ba..

Motarta ta nufa har lokacin hannuwanta da kirjinta rawa sukeyi Kuma tarin ya sarqi makoshinta sosai ta yanda ko magana Bazata iyaba.

Kasa yarda da idanuwansa yayi alokacinda ya dago yaga matar da batada bambamcin kamanni da Maminsa,

Baisan lokacinda bakinsa ya furta kalmar Mamin ba,
To Amma meyasa ta dakata alokacinda ya Kira sunan kafin daga baya ta wucewarta Bata juyoba....

Miqewa yayi da sauri ya nufi kofar yabi bayanta da sauri Kansa na daukan wani irin zafi da juyawa,

Yana gap da Ida jikin motarta Yana kallo tace aja motar awuce.

Maminah ce wannan da gaske?
Maminah ce nake gani?
Am i hallucinating?

Dafe Kansa yayi daya Wani irin sarawa Yana sake daukan zafi...

Morarsa ya nufa kai tsaye da drivernsa harya bude Masa.

Yana Shiga cikin wata shaqaqqiyar murya yace,

"Muje office yanzu Nan.

Jan motar Rabiu driver yayi cikin Dan speed sbd ganin yanda Mai gidan nasa yake kamar a zafafe.

Wayarsa ya daga ya saka Kiran PA dinsa Kuma na hannun damarsa Al-Amin tajudden.

Al-Amin na daukan wayar Kai tsaye yace,

"Ina son bayanan komai da hoton Idon Nera yanzu Nan..

Ok done Sir" Al-Amin din yace Yana janyo Apple tab dinsa dake gefensa yafara dubawa kafin ya saka Kiran Wanda zai Basu sauran bayanan komai da bazai samu a internet ba.

AQEEL ASAD da yagama fita gabaki daya tinaninsa akan lamarin dayake kamar kyaftawar ido a mafarki ace yaga Maminsa,

Maminsa fa yake tunanin yagani...

Shi gabaki daya bayama kawo a matsayin datake din idanma mamin tasa ce,
Sam zancen wata karuwa ko karuwai ya fita Kansa shidai fata da buqatan sanin itace 'dince kokuwa.

Motarsa na parking cikin harabar babban gidansa ya fito ya nufi sashen mahaifiyarsa Kai tsaye kaman yanda ya Saba duk ya dawo saiya fara zuwa ya gaidata yake Isa nasa sashen sbd ba lallai ta sake ganinsaba sai gobe Kuma Daman a wuni kafin ya fita yake zuwa su gaisa sai Kuma idan ya dawo.

Wayarsa ce tayi ringing Yana gap da Isa palon ummansa
Ya daga wayar cikin nutsuwa..,

"Sir I just forwarded you all the informations.

Kashe wayar yayi tareda bude sakon,

Hotonta yakeson gani kawai kafin sauran informations din..

Yana saka qafarsa ta dama a palon Haj Maryamah dake zaune ta zuba Masa ido tana jiran shigowarsa adaidai lokacin hoton Zainab ya bude fes akan screen din tsadaddiyar wayarsa..cak ya tsaya batareda ya qarasa saka qafarsa cikin palon ba.

Wayar ya zubawa fararen idanuwansa dasuka sauya atake,

Komai nasa tsayawa yayi cak idanuwansa suna qara sauyawa,

Kasa motsawa yai sbd gabobinsa da zuciyarsa da suka tsaya cak na wucin gadi...

Kallonsa Haj Maryamah takeyi cikeda mamaki tana ambatar sunanta ganin yanda yayi kamar Wanda yaga matacce yadawo duniya...

Bayajin komai bare yaji sunansa da umman ke Kira...

Miqewa tsaye tayi cikeda tsoron daya cika zuciyarta itama na ganinsa a wannan halin zuciyarta da jikinta na sanyi ta nufosa....

Bata qarasaba ya juya ya koma hanyar daya shigo ta fita idanuwansa na kadawa jajir..

Cak ta tsaya itama daga inda take batareda ta qarasa inda ya Bari dinba jikinta na wani irin sanyi zuciyarta na Shiga tsoro Haka kawai.

Jamilu driver na kokarin Isa gate gurin securities yana juyowa ya hango Mai gidan nasa tafe
da sauri ya juya ya Isa motar ya bude Masa Yana bude Baki zaiyi magana AQEEL ASAD ya katsesa Kai tsaye da cewa,

"Ikeja GRA right now..

Ok Shaykh.

Rufe kofar yayi ya zagaya da sauri ya shiga tareda tayarwa ba Bata lokaci da ribas ya fita gidan suka hau titi da wani irin gudu suka Kama hanyar ikeja GRA Kamar yanda Al-Amin ya turo Masa address din.

Hotonta ne yake yawo cikin Kansa da idanuwansa,

Rintse kyawawan idanuwansa dasukai jajir yai wani daci dake zuciyarsa Yana gauraya bakinsa tareda qafar da yawunsa dasukai daci.

Babu yanda Maminsa zata koma a duniya ya kasa ganeta,
Shekarun da sukai a rabe bazasu taba goge masa asalin kamannintaba dasuke Zane a zuciyarsa da rayuwarsa duk canji da sauyawar da zatayi.

****Haj Zainab kuwa suna baro gurin Kai tsaye gida suka nufa zuciyarta na sake daukan nauyi da wani irin 'daci data manta yanda yake a zuciya.

Lulu daya shiga damuwar halinda ta Shiga din ya kalleta Yana sake tambayarta ko zasu tafi asibitin ne.

Ahankali ta girgiza Masa Kai tana kokarin dawowa hayyacinta sbd ganin yanda ya damu saidai Amon muryar AQEEL ASAD ya daki zuciyarta mugun dukanda takasa daidaita kanta.

Suna Isa gida tayi bedroom dinta da sauri ta rufe kanta tana dafe zuciyarta dake zafi da radadi.

Siddi ce dake zaune palon ta miqe tabita tana Kiran sunanta cikeda so da kulawa tana cewa,

"Mommy are you ok??
Mommy meya sameki?
Mommy please meyake faruwa?
Bakida lafiya ne?

Kasa magana Haj Zainab tayi sai kokarin hana kanta shiga shock takeyi.

Amal ce tashigo dakin itama tana kallon mommyn sbd tana shigowa Bilkisu ta sanar da ita kamar mommyn ba lafiya taji siddi na daga murya.

Qarasowa tayi ta zauna gefen mommyn ta riqo hannayenta biyu tana kallon siddi tace,

"Meya sameta?
Mommyn menene?
Wani abin ya faru ne?

Rintse idanuwanta dasuka fara kokarin sauyawa tayi tana tunanin Meye hadinta dasu AQEEL din da zata damu Kuma?
Ai rayuwarta batada wani Hadi Koda amafarkine bare a zahiri,

'yayanta da 'dan uwanta Lulu sune kadai jininta Kuma abinda ya Kamata ta damu akansa...

Ta manta tayi alqawarin rufe babin rayuwar Zainab Yar malam adamu,
Yanzu Haj Zainab IDON NERA ce wannan.

Bude idanuwanta tayi tareda sauke numfashi Mai sanyi ta dafe goshinsa tareda kallon 'yayan nata dasuka daga hankalinsu gabaki daya.

Wani kyakkyawan murmushi tasaki tana kallon idanuwansu musamman AMAL datake jiran bayanin komai..

Zame hannunta tayi daga na AMAL ta shafa Fuskar Siddi da tafi AMAL rauni tace,

"Babyna ahakan Zaki zama uwar da muketa fata da burin ki zama
Kina komawa kamar baby daga Kinga mommynki cikin ciwo.

Dawo da kallonta tayi kan kyakkwar Fuskar AMAL mai daukan hankali tana murmushi tace,

"Am ok sweetie and everything is fine karki damu,

Wani case mukaje da uncle dinku suka Bata Mana Rai Amma ankai karshen matsalar komai yazama tarihi Babu abinda zai taba sauya Mana rayuwar farin cikinmu da kwanciyar hankalinmu.

Ajiyar zuciya suka sauke dukkaninsu Amal na cewa,

"I love you Mom.

Kallonsu tayi itama tana dariya tace,

"I love you both.

Uncle Lulu ne yashigo tareda Dr tayo daya Kira Dan yakasa nutsuwa da yanayin Zainab din.

Ganinsu ahakan yasashi sauke numfashin samun nutsuwa suka dawo palon dukkaninsu Dr tayo ya dubata yace jininta ne kawai ya Dan hau shima ba wani abin damuwa bane.

Dr tayo na tafiya AMAL ta miqe ta nufi bedroom dinta ta tube ta Shiga toilet.

Wanka tai ta fito ta Sanya doguwar Riga Mara hannu Kamar yanda ta Saba ire irensu ne kayan datafi sakawa idan tana gida.

Qaramar hula ce da Bata Gama rufe kanta ba a kanta sai slippers data saka ta fito taci abinci tana miqewa tsaye zata nufi sama inda su mommyn suke Bilkisu ta tareta da cewa,

"Anty AMAL Pelo yakira wai mommy tayi baqo.

Bata tsayaba tace,

Zan fada Mata.
Chapter 35 · 0% Book details