← Book details Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 95

Sashe 13

Idon Nera Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Malam Sanda yasa Aqeel matashi ne Mai nutsuwa da hangen nesa tareda tunani na masu ilimi Dan haka baiyi wani dogon Jan lokaciba yace idan Zainab din ta Aminta da aurensa shikenan Allah yabasu hakuri da zaman lafiya.

Take ya sanar masa ta Aminta Dan haka a washe gari ya karbi sadakin Maminsa a hannun baba Malam Sanda ya shigo dasu sai alokacin ya tunkari Haj maryamah da zancen sbd kamar aikin Gama ya riga ya Gama
Dan Idan ba Hakan yayiba tun farko ya tunkareta bazata aminceba da wuri zatai watsi da zancen.

Malam Sanda kuwa da baisan cewar Zainab din qanwar Haj maryamah bace baiyi tunanin Zainab nada dangiba Dan kuwa Dama kusan kowa sanin marainiya Mai Aiki ake Mata wadda aka dauko tun Tana yarinya har girman yanzu shiyasa ma ya amince da auren Dan shima ya bada tasa gudunmawar gurin inganta rayuwarta.

***
Tsit palon Haj maryamah ya dauka sbd wutar da itama ta Dan dauke ta wucin gadi,

Kudin sadakin Zainab da Aqeel din yake nuna Mata take kallon agabanta zuciyarta na neman toshewa da rashin iska na zallan mamaki da firgici.

Maida kallonta tayi kan Aqeel ahankali Tana nazarin yanda yariga yayi nisa aduk wani lamarin daya shafi Zainab baya shakkar kowa bare tsoron bacin ranta.

Daqyar ta iya bude bakinta tace"

Zainab tasan ta zancen??

"Tasani Amma nine na tilasa Mata amincewar......

Sbd Kaine ka haifeta ko?

To meye amfanin samuna da zancen yanzu Bayan kun riga kunyi shawara har Kai ubanta ka karba sadakinta.

Dan rintse idanuwa yayi ahankali Yana sauke Kai daga kallonta Dan a kala manta Yana iya jiyo tsananin fushinta da bacin ranta.

Kasa cewa komai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta tabarsa a palon sbd wani tiriri da zafi zuciyarta ta dauka.

Sosai taji zuciyarta tayi zafi da Zainab,

Tafara gajiya da yanda take baa matsayin kowaba agurin Dan data dauka cikinsa ta haifa akan Zainab,

Ya maidata kwata kwata a Bayan Zainab,
Zainab itace first priority dinsa kafin ita,
To meye amfanin Zainab a rayuwarsa da zata fi Masa uwar data haifesa.

Sbd yanda ranta yayi tsananin baci daga shi har Zainab Babu Wanda takuma magana dashi ta dauki fushi Sosai.

Zainab kuwa batasan meyake faruwa ba Dan batamasan cewa harya karba sadakinba.

A bangaren Aqeel kuwa ganin yanda Haj maryamah tadauki zafi matuqa akan zancen yasashi sanarda Baba malam Sanda a daura auren zuwa jumaa Tunda saura kwana biyar juma'ar tayi.

Sai alokacin ya sanarda Mamin tasa yakuma Bata sadakinta a hannunta.

Shiru tayi tsawon mintuna tareda shiga tunani kafin ta tambayasa Haj maryamah Bata kirata tayi Mata maganar ba Bayan Dole saida izininsu da saka hannunsu zaayi duk wani lamarin.

Haka ya share zancenta Dan yasan Maminsa bazata amincewa aurenba kamar yanda yasan bazata taba aurar da ita dinba
Shikuwa bazai iya barin rayuwarta ta qare a Hakan ba tinda ba baiwarsu bace itama uwarsa ce,

Idan a baya batada gata ayanzu daya San Kansa shine zai zama gatanta daga Nan har lokacinda zai bar duniya inshallah.

Hankalin Haj maryamah bai Gama tashina da tsananin bacin rai saida Malam Sanda da Kansa yayi magana da ita ya sanar Mata yanda sukai da Aqeel tareda Bata tabbacin jumaa zaa daura auren.

Kudi ya fidda ya ajiye Mata daidai qarfinsa akan asiyawa Zainab din sitira.

Haj maryamah harsuka Gama magana ya tafi batasan haqiqanin me take cewaba Dan kuwa Aqeel yagama kasheta da mamaki wato har dangin mahaifinsa yasa malam Sanda yayi magana dasu akan auren Zainab din acan akai neman aure na manya aka sake bawa Aqeel qwarin gwiwar wannan aikin alkhairin daya hada tareda saka Masa albarka.

Kasa danne tsananin bacin ranta tai Dan bazata iyaba,
Duk wani rashin mahimmancinta ga danta ya nunawa duniya Tunda ya yanke wanan hukuncin shi kadai ya zartar.

Umma takira Tana hawayen qunci ta sanar Mata komai Tana jaddada laifin akan Zainab da zata iya yarda da buqatar Aqeel ta aure batareda saninsu ba.

Ita kanta umma mamaki Mai girma tashiga Jin Zainab dince zatai aure bada saninsuba,

Kenan duk kokarin dasukeyi akanta Bata ganiba shine ta zabi 'dan da aka Haifa a gabanta ya aurar da ita ga tafaffen malaminsa da baa San asalinsaba,baasan danginsaba baida kowa.

Wannan karon ummar da kanta ta Kira Zainab tayi Mata fadanda Bata taba yimata irinsaba...

Sai alokacin Zainab tasan da basusan da zancenba ashe

Hankalinta tashi yayi da fadan umma Dan kuwa maganganu marasa dadi da raunana zuciya ta fada Mata Wanda yasata kuka sosai.

Haj maryamah ta nufa dan Bata hakuri akan lamarin Amma Kuma bacin ran Haj maryamah din yafi na Umma Dan kuwa Kai tsaye ko wannan karon tabata zabi akan idan hartayi auren Wanda baasan asalinsaba Babu ruwansu da ita sun rabu kenan har abada.

Hankalin Zainab ya tashi Dan haka Bata tsaya shawara ko tunaniba tace ta hakura da auren ta fasa.

Hakan ya daki ran Aqeel sosai tareda Jin bacin rai da kunyar halayen mahaifiyarsa...

Daga umma har Haj maryamah Babu Wanda yayiwa Zainab sassaucin bayyanarda bacin ransa Dan haka tashiga wani mummanan Hali na damuwa da qunci tareda 'dacin zuciya Mai tsanani.

Halinda tashiga yasa Aqeel akaro na farko tsayawa da raayinsa akan na ummansa da ummarta.

Dukkanin harkar tafiyarsa karatu ya sokesu da Kansa tareda sanarda mahaifiyarsa ya fasa tafiya koina.

Babbar sabuwar rigima lamarin ya koma Wanda ya haddasa bacin rayuka tareda koke kokenda yawanci Zainab ce tafi Yi Dan ita aka yabawa laifin wannan karon har dangin mahaifin Aqeel din ita suka dorawa aka ringa tofa Mata maganganun gori marasa dadi.

Karshe dai da rigima taqi qarewa har saida umma tazo da nata bacin ran hakama haj Maryamah har gadon asibiti sbd jininta daya hau sosai Dan kuwa tashin hankalin da bacin ran Aqeel babu wanda bai ganiba qarshe dai kusan Zainab din yakeda niyar zaba akan kowa Dan haka tashin hankalin Zainab da baqin jininta saiya qaru.

Dangin mahaifin Aqeel dinma sai suka maida zancen Kuma akan Haj maryamah suna sukar tarbiyarta da wadda tabawa Aqeel din tako Ina duk sai komai ya qara lalacewa.

A ranarda taga yanda Haj maryamah ke zubda hawaye akan Aqeel zai jikinta yayi sanyi Dan kuwa tasan zubar hawayen uwa ga danta fitinace garesa Dan haka ta yanke shawarar dakatar da duka tashin hankalin dayake gudana....Dan haka ta amince da auren Malam Sanda tabar gidan har abada kamar yanda Haj maryamah tace..
Amincewarta zata sakata nesa da Aqeel Wanda Hakan zai basa damar jituwa da shakuwar kauna da mahaifiyarsa dake ganin itace ta zama sanadin da Babu kauna Mai tsanani tsakaninta da danta.
##MAMUH#
#DR SHAYKH AQEEL ASAD
#AMAL IDON NERA
#LOVE/ROMANCE
#LIFE#SISTERS

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
11

*_ASSALAMU ALAIKUM_*

_Barkanmu da dare da fatan kowa yana cikin qoshin lafiya_

_Akwai abinda muka turo tallansa na WOMEN EMPOWERMENT PROGRAM(KUDI KE KIRA),so please duk wadda batayi pyment ba ta jira tukunna kada tayi,akwai wani CONFIRMATION da mukeso mu samu a kansu_

*Idan komai ya daidaita zamu sanar muku*

*_idan kikaci gaba da pyment kuma bada yawunmu ba_*

*Muna godiya sosai*

**********
Rayuwar auren tasu farko yanayin yazo musu a Dan takure sbd nauyin juna da rashin sabo da rashin sanin juna ko kadan tun farko,

Ga kunya da nauyinsa dake tsananin dawainiya da Zainab sbd zamansa babba sosai gareta ya Isa haihuwarta sosai gashi kwata kwata basu San komai na raayi ko halayen juna ba.

Abu daya ne yafara sakawa zaman nasu dadi da kwanciyar hankali shine nutsuwa da biyayyar Zainab tareda taka tsantsan dan kaucewa laifi da Bata Masa Rai.

Da farko shi Kansa malam Sanda din ya dauka biyayyartace sai daga baya ya fahimci harda rashin sakewa da sabon datai da aikin bauta da biyayya batada raayin kanta kwata kwata sai Wanda akace tayi shiyasa anan din ma sai yazama kamar zaman bautar takeyi bana yanci da kwanciyar hankali ba, Dan haka yafara kokarin janta ajiki sosai tareda nuna Mata ba wannan zaman zasuyiba,

Zaman nutsuwa da kwanciyar hankali yakeso harma da kaunar juna.

Duk da Hakan dai Bata wani sakeba ta Sabu dashi saida sukai kusan wata uku zuwa na hudu tukuna tafara sakewa har Tana dariya da farin ciki a tareda mijin nata Wanda shikam har cikin tsakiyar zuciyarsa tuni ya kamu da so da kaunar matarsa sosai.

Zainab tasamu kyakkyawar rayuwa a hannun mijinta yanzu,

Batada damuwa,

Batada abinda ta rasa face Yar uwarta da umma Wanda takewa kallon mahaifiya agareta,

Har tsawon wannan lokacin su umman fushi sukeyi da ita Mai tsanani musamman Antynta Haj maryamah da kusan har lokacin Bata dawoba Tana gidan mijinta Abuja.

Kusan Babu ranarda Zainab Bata kiransu Amma basa daga wayarta 
Amma takasa gajiya kullum sake Kira takeyi.

Aqeel yakoma gidan kakarsa Haj Kaka mahaifiyar Dadynsa Dan Sam baida raayin komawa Abuja gidan ummansa ya zauna acan
Dan haka ya zauna a gidan kakarsa kafin lokacin tafiyarsa dayake qaratowa.

Aqeel kusan Babu ranar da baya zuwa gidan Mamin tasa sbd anan suke karatu da baba malam din nasa yanzu Dan haka kusan abincin darensa a gidan yakeci kwata kwata
Har na Rana ma wataran duk anan yakeci sbd sabo da abincin Mamin.

Babban abinda yake taqaita damuwar Zainab akan Yar uwarta da umma shine Aqeel daya cike Mata gurbinsu ya hanata Shiga damuwarsu sosai duk da abin na cikin ranta takasa cirewa sbd fushinsu akanta Tana ganin illarsa Tunda dukkaninsu iyayenta ne.

Shi Kansa Aqeel yasan fushi sun umman sukeyi dashi sosai musamman ummansa Dan haka yake kwantarwa da Maminsa hankali akan komai zai wuce.

*****Lokaci ya Dan ja tun daga kwanaki har satittika da watanni,
Chapter 13 · 0% Book details