Sashe 25
Galadima Family Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
tace"lafiya lou munjiku shiru ga events da zamu fara gudanar wa tun jiya amma baku iso ba sai yau. "Aikam kinsan ogan be gama wattaakewa da tafiya ba so munjira ya huta sai mu shigo agaisa, Akeela tace"eyya babu komai,duban Sauban tayi tare da langabar dakai tace"Baby inata magana amma kayi shiru, dagowa Sauban yayi tare da Kura mata ido duk da bata ganin eye ball nashi amma sai da kallon yasata taji babu dadi,agogon hannun sa ya kalla tare da duban su yace"please Taufeeq kuyi abinda yakawo mu cuz time yana tafiya, Taufeeq yace"Ok. Dagowa yayi cike da basarwa yadubi Akeela yace"amarya nawa kuke da bukata ne?na hidima nd everything? "10 millions naira! Sukaji ambasu amsa,duk cikansu suka dubi inda maganar yafito har shi gogan sai da yadago. Xahratty CE Lallai Alqalami yafi takobi [5/28, 11:27] Xahratty (OUM AJMAL): *_GALADIMA FAMILY_* Story&Written By *FATEEMA ZAHRA LAWAL* Marubuciyar A DALILIN'YAR TSINTUWA. MIJIN ZAHRA. DIAMOND LADIES ( Daukar fansa)paid book. RUHIN AMRITA (FATALWA CE). Now *_GALADIMA FAMILY_* Page 39/40 ______Sosai maganganun hajiya Aliya suka tsaya ma Adda zainab a ranta domin tashiga fargaba tare da tsananin tashin hankali,lallai tasan wacece hajiya Aliya duk abinda ta sama gaba to tabbas sai ta cimma nasara,hankalinta a tashe yake sosai take safa da marwa a cikin dakin nata,a gefe guda kuma damuwar ta daya shine haryanzu bataji sakamako akan bilkisou ba,a koda yaushe cikin jiran tsammanin kira take amma shiru ga biki ya gabato saura kwana biyar kuma can maidugrin zasu nufa don acan ne ake taron biki,sosai hankalinta yakasu gida biyu,wani tunani ne yafado mata cikin rai don haka da sauri tadauki wayarta tafara laluban layin hajiya Aliya,sai dai kash!sanar da ita ake wayan fa haryanzu a kashe take alamu ya nuna tabbas bata dawo daga kasar nijar dinba. ****** Sanye takeda doguwar riga mai hannun armless,roba ce tasamu waje ta lafe a jikinta wanda har tayi sanadin bayyanan duk wani halittun ta saboda shape duk ya bayyana,musamman kugunta wanda yake a tsuke sai hips daya nemi waje ya baje ga tudun bom bom,hankalinta a kwance take tafiya da alamu video call takeyi don murmushi takeyi da surutai.Kallo daya ya mata tare da kauda fuskan shi cikin basarwa,idanunshi ne suka sauka akan wani security dake bakin gate ya kurawa mata idanuwa ko kiftawa bayayi like maye,maida dubanshi yayi gareta yaga tabbas ita yaron yake kallo,ranshi ne yayi kololuwan baci wanda har sai da yakasa control din kansa,idanuwan sa sun kankanci cikin bacin rai yanufo inda take gadan ,babu zato taji an fusgota tare da yarfa mata mari. Lokaci guda tanemi jinta da ganinta tarasa don sun dauki batasan sanda tasaki wani ihu ba tare da dafe kunci don rabon da ayi mata irin wannan marin ta manta,da sauri Ammi ta futo daga apartment dinta don yafi kusa saisu Mashahuda da suka fito daga apartment din Mom suma a guje saboda karar ihun nata,nunata yashiga yi da hannu bakinsa har wani rawa yake amma yakasa furta komai."Menene haka Son?me ta maka lafiyan ka lau kuwa?gabadaya yakasa magana,da sauri yajuya kai tsaye gate din yanufa,koda yaje beyi wata ba ya zabga ma security dinnan mari,a gigice ya dafe kuncin jikinsa babu inda baya rawa,cakumo kwalar rigansa yayi tare da diddilo masa idanuwa yace"idan nasake kama ka kana ma wata mace a gidannan irin kallon da kama wannan yarinyar yau,wallahi sai kabar aiki a gidan nan tare da tsarabar nakasa ka don sai na nakasa naga uban da ya tsaya maka,stupid son of a bitch!! Yakarasa maganar tare da hankada sa baya,a gigice security dinnan yanufi kofan gate yafice jikinsa na wani irin rawa,juyowa yayi kaitsaye yanufi parking space, Ammi ce tayi saurin isa garesa"Son wai ba magana nake maka ba kana jina meta maka da zaka mata irin wannan marin?kaga yanda shatin yatsunka suka fito a kumatun ta kuwa?bakinsa na rawa yace"Saboda rashin kamun kai na yarinyar nan haka taga sauran 'yan uwanta ke dressing a cikin gidan?ta fito tana karkada ma security jiki tana shaking body?ko kunya bataji?wallahi daga yau nasake kamata da makamancin dressing dinnan sai na lahira yafita jindadi"yakarisa shiga motar tare da kunnata yayi reverse yana dannan wani azababben horn. Juyawa Ammi tayi taga dressing din jikin Zuhra,babu wani aibu a shiganta amma yamata wannan marin?girgiza kai Ammi tayi tare da nufar Zuhra wacce banda kuka babu abinda takeyi gashi bakinta yakasa shiru cikin muryan kuka take magana"Ni me dressing dina yayi?kawai saboda cin zali zemun wannan marin wallahi sai Allah yasaka min tun ina karama yatsaneni saboda kawai yatsaneni shine zaizo yamin marin nan Allah nagani,kuma ban......"Zuhra!!! Bata karisa maganar ba taji ankirata cikin daga murya, Ummie ce,karisowa tayi fuskar ta babu wani walwala tace"mekike so kice?cewa zakiyi da baki yafe ba?shidin sa'an kine?kull kada nasake ji,meyasa bema sauran ba sai ke kidubi shigan su mana,amma ai basu fito ba suna killace a daki bari har idon security yakai kansu. Cikin muryan kuka Zuhra tace"amma Ummi aini shiga ta duk tafi tasu mutumci. Ummie tace"naki yaga yafi muni sai ki gyara gaba inba haka ba zakisha wahalar sa kuma niba zan hanashi hukunta ki ba,tana kare fadan hakan tajuya,kamota Ammi tayi tanufi apartment dinta da ita"Why? Why?dani kadai yasama ido a gidan nan baga su Aunty Mashahuda ba wallahi Ammi nima aurena zanyi na huta kawai ranar bikinsu Aunty Mashahuda a dauramin aure tare da nasu nima na huta"takarisa maganar cikin muryan kuka,dubanta Aunty Maryam tayi tace"Oh really?to a'ina kika samo mana mijin naki?sai ama Daddy magana idan yadawo.Duk dariya 'yan parlon suka sanya,Ammi tace"gaskiya kam Maryam ya kamata bari muji Koda wa za'a samata ranar. Shiru Zuhra tayi kamar ruwa yacita sai yanzu ta fanimci baran baramar da tayi,rufe fuska tayi da sauri, Mashahuda tace"kila da Shuraim ne Ammi, Ammi tace"wanene haka? Mashahuda tace"Shuraim fa cousin din su ya Asheer din Aunty falmata, Ammi tace"wannan yaron?lallai na ganesa kuma sosai na yaba da halayensa don yayi his very innocent,murmushi Zuhra tayi tare da nufar hanyar bedroom din Aunty Mashahuda cikin daga murya tace"wallahi Ammi niba da gaske nakeyi ba da wasa nakeyi wallahi niba yanzu zanyi aure ba sai na kammala degree dina tukuna. Duk cikansu dariya suka sanya. *** *NIJAR* *** Sosai ya kura mata idanuwa saboda yaji dadin maganarta,cigaba da magana tayi"nifa boka hatsabibi babu cin amana a cikin lamarin nan naga tana wasa da aurenta shiyasa ninakeso na aure Alhaji iliyasu zanyi tattalin sa tare da basa kulawa tunda ita tazama ballagaza,duk fa cin amanar da zanyi bekai Wanda takeyi,wallahi har gwara nawa raya sunna nakeson aikatawa ita kuma fa?wani irin dariya boka hatsabibi ya kyalkyale da ita tare da tsuke face yace"kisa a ranki aikinki yama yiwu ya gama,dole kishiga gidan Alhaji iliyasu matsayin matansa ta aure,domin nima hajiya Zainab tayi min lefin da dole namata mugayen hukuncin da bata taba zato ba,tasa nayi asaran aljanu bila adadin kuma sune sojoji duk ciki wallahi sai ta girbi abinda ta shuka,zaro idanuwa hajiya Aliya tayi bakinta na rawa tace"b..bo..boka wai shima wannan aikin ba'ayi nasara bane?juyowa yayi a fusace ya watsa mata idanuwan sa cikin daga murya yace"kada kija lefinta ya shafeki duk da cewa harda ke amma nata yafi naki domin aikinda akayi gabadaya babu wanda akayi nasara. Dafe kirji hajiya Aliya tayi da karfi tace"Nashiga uku ni Aliya,amma ya akayi aikin beyiba,wallahi boka da hannuna nataya ta barbada maganin a shimfidar ta kuma ta kwanta akan shimfidar,wani banzan kallo boka hatsabibi yama Aliya cikin muryan tsawa yace"shine nace miki beyi ba don asirin ya karye,kekuma ga wannan kwalin ki sanya a idanuwan ki,a ranar da kikaji Alhaji iliyasu zai dawo kafin yafara kallon kowa ki tabbatar da kece yafara kalla,sannan kada ki kuskura ki hada idanu da wani idan ba haka ba to tabbas wanda kika fara hada idanu dashi shine zaki aura"ya karasa maganar yana mika mata kullin maganin,jikin hajiya Aliya na rawa ta amsa tare da cewa"da yardan boka hatsabibi sai na mallaki Alhaji iliyasu,kuma aikina baza'a samu kuskure ba. Anan sukayi sallama inda sai da wadannan kattan munanan mata suka biya bukata da ita. ____*NIGERIA*____ Sosai shirye n biki ya kankama ran ar laraba su Mashahuda sukayi bridel shower,sosai events din ya hadu,don suyi kyau matuka, Shuraim yazo gidan don shine yakawo Aunty safeena,sosai yakema zuhra wani irin so wanda shikansa mamakin kansa yakeyi,fuskansa dauke da murmushi ya zubanya mata idanuwa,dan cuno mouth tayi cike da shagwaba tafara bubbuga kafa"To wai ni ya Shuraim kallon na menene?tayi maganar cikin shagwababbiyan murya tare da zaki da sanyi,"zakasa Allah nakoma ciki,tunda tasani zakayi kamar wata television kana kallo,sosai yanayin nata yakara rikitar dashi har ya rasa lissafin sa ajiyan zuciya ya sauke"Huh bazaki gane bane ina imagine ne wai na mallakeki,huhhh da ranar sai anyi sadaka na abinci,kudade, everything,yakarisa maganar cikin shauki,dariya Zuhra ta sanya"I am still young,dudu shekaruna 18 ne fa,why not?na gama degree na daura B8? Wani banzan kallo ya Shuraim ya mata cikin sigar Wasa yace"wa kike tunanin zai tsaya jiranki har wannan shekarun?ai malama kawai kya cigaba a gidana,dariya sosai ya bata don haka tasake tafara dariyar ta wanda dimple, Gap teeth dinta duk suka bayyana a kuma dai dai wannan lokacin ne motar su ya Sauban ta danno kai cikin gidan,fitowa sukayi su duka ukun,sai dai shi gogan face nasa a dore,ba kamar taufeeq da kareem ba,duk da shi Kareem na ciki na ciki. Cikin sauri Zuhra ta nufi inda suke sai dai kaitsaye ta wuce Sauban ko kallon sa batayi ba ta nufi wajen taufeeq,kamo hannunsa tayi,"yawwa Yaya ga ya Shuraim can kazo ku gaisa, bata jira mezece ba tafara jansa. Tun kafin su kariso Shuraim ya karisu,cike da girmamawa yadan rissina kadan tare da mikawa Taufeeq hannu yace"Yaya sannu da zuwa,shima Taufeeq face dinsa babu yabo ba fallasa yamika masa yace"sannu ko malam Shuraim ya mutanen gidan? Shuraim yace"kowa lafiya lou Yaya,dubansa Taufeeq yayi sannan yadubi Zuhra,sake maida duban sa yayi ga Shuraim din yace"Ko zan iya sanin matsayin ka a wajen kanwata malam Shuraim? Shuraim na kokarin magana cikin sauri Zuhra tace"he's my friend...tayi maganar tana sakin murmushi,gyada kai Shuraim yayi yace"yes Yaya,murmushi Taufeeq yayi yace"Ok nice to meet yhu malam Shuraim,insha Allah zansa mana lokaci musake gaisawa da kyau,dariya Shuraim yayi cikin jindadi yace"babu damuwa Yaya a shirye nake don amsa kiranka. Taufeeq yace"Ok