Sashe 14
A Daren Farko Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
A DAREN FARKO
10
Ummi tagyara zama tare da jan dogon numfashi
tace "jiddah khalifa ya tafi ba tare da na amfana
da zaman da nayi a cikin gdansu ba, face bacin
rai da mugun gani da idanuwa na suka gani.
Jiddah tabata rai tana yimata wani irin kallo tace
"wai me yasa kika fiye gaggawa ne ummi, anya
za ki rinka cimma nasara a kan abubuwa, idan
kika dubi tsarin khalifa gaba daya da yadda kike
ba abu ne mai sauki ba mallakar zuciyarsa sai
anyi da gasken gaske.
Ummi tace "to in banda abinki jiddah tawace
hanya zan samu nasara idan nayi hakuri, kada
kimanta fa shekaru hudu khalifa zaiyi a germany
kafin yadawo kasar nan, yana chan Ina nan zan
iya jan hankalinsa jiddah, dole xuciyata takaraya,
ke bari in gaya miki wani abu daya da ban yi
zaton zan gayawa wani ba, ina cikin gdan nan fa
ina kokarin jan hankalinsa na ganshi da mace
rungume a jikinsa a dakinsa, idan zan iya jan
ra'ayinsa zai kawo mace gdan nan ina cikinsa?
Jidda ta ja dogon tsaki tace "daman kina
tsammanin ko khalifa a karan kansa yake sonki
za ki rabashi da yammata ne, namiji irin khalifa
ko baice yana son 'yanmata, za su yi tabinshi tun
bai kula ba watarana sai ya kula, don hakama
shawarar da zan ba ki itace idan kinyi nasarar
mallakar khalifa to ki sanya hakuri mai yawa a
zuciyarki akan 'yanmatan da za suyi ta bibiyar
khalifa don ba namijin mace daya bane.
Ummi tajinjina kai tace "tabdijam hakika zan
girgiza kowa a kan khalifa ba zan hada miji da
wata ba, ba zan yi tarayya da wata macen a
dakin khalifa ba.
Jiddah takyalkyale da dariya tace "ummi manya
har khalifan ya zo hannu da za ki wannan cika
bakin.
Ta lumshe ido tace "kuma fa hakane maganar
dakika fada ne naji kamar har na mallake shi na
ji tsananin takaicin hadashi da wata da zanyi a
sunan kishiya .
*************
Malam musbahu yana cigaba da karfafa
zuciyarsa ga kaunar fatima tare da tattalin farin
cikinta sai dai ba ya samun hadin kanta sbda
tsananin kunyarta, ba ta iya sakewa dashi hakan
yasa tadaina sakewa a gidan duk abinda take
idan yashigo sai taji kamar za ta nutse a kasa
don kunya hakan na takura shi shima don ya fi
son tasaki ranta auyi soyayyar da za su fahinci
juna kafin lokacin auransu.
Ranar laraba da safe inna ta tursasawa fatima
kaiwa musbahu abincinsa a kokarin innar na
ganin sun shaku ta fuskar soyayya kamar yadda
tafahimci basu sake da junansu ba, fatima ba ta
son shiga dakin musbahu sbda maganar soyayya
da yake mata na daga mata hankali alhali bata
saba ba.
**********
Lafiya kalau khalifa yasauka a kasar germany
inda zai zaman karatun likita ,har yanzu damuwar
daya taho da ita daga nigeria yana makale a
ransa ga kewar iyayansa tamkar bai taba tafiya
ba sai a wannan lokacin, yana shirin shiga motar
dazata kaishi masaukinsa kamar daga sama yaji
an rike mai hannu, yajuyo dasauri yazu bawa
yarinyar ido, Anisa? Yafada cikin shakku dan ba
shi da tabbacin ko daidai yafada sunan.
Tayi murmushi tace "amma na ji dadi daka iya
kiyaye sunana.
Yace "nikam mamaki nayi dana ganki a kasar nan
yaushe kikazo?
Tace "sai mun zauna zan ba ka labari yanzu muje
naga masukinka ko za ka fara zuwa ganin na wa
masaukin?
Yace "ah ba komi inga waya ba sai mun tafi ba.
ta langabe kai tace "kada ka sanyaya min jiki
bayan na yi farin cikin ganinka kayi murnar
ganina.
Yace "hakika na yi farin cikin ganinki domin ina
bukatar abokin debe kewa a wannan kasa da
nazo.
Tace"to kayi hakuri mutafi mana.
Yace "to muje.
Sashensa daban a gdan da zai zauna, falo guda
daya da bedroom ba dai wani girma bane amma
akwai kayatarwa, kitchen kamar na mace sbda
tsaruwar da yayi shi kansa saida yayi sha'awar
ace yanada matar aure wadda za tarika dafa
masa abinci irin na mamansa, wadda yayi mugun
sabo dashi, a zaman da yayi da mamansa bai da
matsalar komi ta fuskar abinci duk abinda yakeso
shi ake masa, duk yawonsa da gararinsa bai iya
cin kowani abinci sai a gdansu sbda shi mutum
ne mai kyama da kuma son cin abinci mai dadi
duk dadin abinci bai iya ci sai a gdansu ko a
halin yanzu yunwa sosai a cikinsa bai san yadda
zai yi ba tunda bai iya girki ba ko ruwan tea bai
iya dafawa ba, hakan yasa tunda ya zube akan
gado bai kara motsawa ba dan ko takalmansa
anisa ce tazare masa.
Tana zaune daf dashi tace "khalifa bayan gajiya
kana tre da damuwa kataimaka kagaya min.
Ya lumshe ido yace "Anisa ba za ki iya magance
min matsalata ba shi yasa nace kar ki biyoni, ba
za ki ga walwala ta ba a wannan lokacin.
Ta marairaice kamar za tai kuka tace "dan Allah
kafada min Abbakar.
Yace "Anisa yunwa nakeji kuma ba za ki iya dafa
min irin abincin dazai gamsar dani ba.
Ta bushe da dariya tace "Abbakar idan yau ban
dafa maka abincin daya gamsar dakai ba to mata
na rako duniya, kuma har yanzu bakasan wacece
ni anisa ba, ko ka san cewa sbda na ji labarin
kana matukar son abinci mai dadi na shiga
fafutukan koyon girki ko ta ina?
Ya fiddo ido yna kallonta, tamike tace banga
tazama ba kafin kagama nazarin maganata bara
in dafa ma abincin.
Ido yabita dashi har ta fice yamaida idonsa kan
rufin dakin.
A wani party suka fara haduwa wanda wasu
dalibai suka shiga sbda nishadi, a lkcn bata dade
dafara xuwa mkarantar ba, tana zaune tare da
kawarta nafisa, suna hira wasu samari suka
tskoanesu har nafisa za tayi magana anisa
tahanata tace "kyalesu dan mu kulasu ne zo mu
bar gun.
Za suci gaba da binsu shi kuma khalifa yana
kallonsu ya aika a gaya wa wadannan samarin su
shiga hankalinsu su kyale su anisa ko yasa a
musu tsirara a gun, samarin wanda sakon yafito
daga gareshi yasa sukayi nasu gurin, ya aika
akira mai anisa.
Mamaki yakamata jin ance wai wani ne yake
kiransu kamar wasu 'ya'yansa taduvi dan aiken
tace "kaje kace a za mu zo ba. ..
Nafisa tayi saurin rufe mata baki tace kinsan
waye Abbakar muhammad? zo muje kawai.
Anisa tace "to me zai mana da har zai ce muzo?
Idan wani abu yakeso garemu mai zai hana shi
yazo da kansa? kai je kace bazamu zo ba.
Dan aiken khalifa yace "idan kika kara furta kalma
mara dadi akan maigidana zanje in gaya mai idan
kuwa nagaya mai daga wannan rana kin daina
farin ciki a wannan makarantar.
Ga dukkan alamu ita kawarki ta san shi ke kuwa
bakuwa ce shiyasa nayi miki uzuri.
Anisa takara fusata sosai za tayi magana nafisa
tarufe mata baki ta ja hannunta tace zo muje.
Har anisa ta dage akan ba ta zuwa sai kuma taga
bara taje taga abinda wannan mai gadarar yake
takama dashi tabashi mamaki.
Khalifa na zaune kan kujera tare da abokansa,
Anisa da Nafisa sukazo gabansu, Nafisan ce tayi
musu sallama ita kuwa anisan bakinta ne yayi
nauyi duk abinda nayi niyyan fada masa ya
gagara sai ido data bishi da shi.
Yayi murmushi yanuna musu gun zama yace
"kuzauna 'yammata.
Bata san sanda tazauna ba, gayen ya gaji da
haduwa ya yi mata ya burgeta anya kuwa ta taba
ganin matashi mai kyaun wannan a rayuwarta?
Tun daga wannan rana suke gaisuwar mutunci da
shi da abokansa, zuciyar Anisa ko yaushe a cike
yake da kuncin son khalifa batasan yadda za ayi
tasamu soyayyar ta sa ba, hatta nafisa duk yadda
suke ba sa boyewa juna sirrinsu amma ta kasa
gaya mata .
Lokacin dataji cieon so na neman hallakata ne ta
sanar da nafisa halin datake ciki, tayi dariya tace
"haba sister na san halin dakike ciki boye min din
da kikayi ne yasa na nuna miki ban sani ba.
Tace ni dai na ji ina mafita? Anisa kai tsaye
zance ba za kisamu khalifa ba, ba za ki iya
mallakarsa ba sai dai in Allah ya sa ravonki ne
amma sai kinyi hkuri mai nisa kafin kicin ma
nasara, kada kifito kigaya mai kina sonsa saidai
kici gaba da hakurin bin wasu hanyoyi dan kija
ra'ayinsa.
Anisa taci gaba da binciken rayuwar khalifa daki
daki me yakeso da wanda bai so, har a gdansu,
abinda yatsorata ta shi ne mata dayake
mu'amula da su sannan ba shi da niyyar aure.
Lokacin daya kammala karatunsa na Bayero duka
shekararta biyu a nata karatun, anan ne
hankalinta yatashi sosai ganin bbu hanyar da
zata kara ganinshi kuma tashiga binciken ina
yasa gaba a rayuwarsa, aiki zai fara ko ci gabada
karatu, bata samu cikakken byani ba sai da aka
dade tana fama da azaban ciwon sonsa a
zuciyarta, tadagawa mominta hankali akan sai an
maidta kasar germany ta karsa karatunta acan,
momin tadube ta cike da mamaki tace "ke kuwa
sbda me?
Kasancewar nisa ce diya tafari a gun mahaifiyarta
kamar kawa da kawa haka suke bata iya boye
mata duk wani sirrin daya shafeta ko meye shi,
taciro wayarta tanuna mata hoton khalifa tare da
bayyana mata halin datake ciki a kansa, tace
"momi tsawon shekaru biyu zuciyata ta rayu ckin
azabtacciyar soyayyar har wani lokaci inaji a
raina kamar mutiwa zanyi idan ban mallakeshi
ba, mom ba zan iya rayuwa bbu khalifa ba ke
kadai ce za ki iya min wannan taimakon.
Hnklin mmin yatashi sosai ta tausaya wa Anisa,
ta jima tana kallonta sannan tayi ajiyar zuciya
tace, "Anisa ba zan ga laifinki ba dan kin kamu da
soyayyar wanda kikeso tunda ba mutum ne yake
dorawa kansa so ba kuma zan yi iya kokarin inga
burinki ya cika.
Zan sa abanku yashirya maki zuwa germany
kiriga khalifa zuwa, zanyi ta binciken tafiyar shi
da saukar shi a kasan, inaso ki kasance a filin
jirgin lkcn dazai sauka domin kibashi mamaki,
dan zai sauka ckin kewar iyaye da abokansa Na
gida tabbas sai ya yi farin ckin ganinki.
Abu guda daya zan rokeki Anisa shi ne kitsare
mutuncinki, kada kiyarda soyayyarsa tasa kibiye
mishi ya lalata miki rayuwa.
Ta gyara zama tace "mom ban taba kallon khalifa
da wata manufa ba mara kyau burina shi ne
muzama miji da mata, ba zan iya bata rawana da
tsalle ba akan khalifa.
Mom tayi murmushi tace "anisa duniya fadi
gareta abinda kika sani shi kika sani wanda baki
sani ba baki sani ba, na san mutumcin soyayya
kuma ina darajata, ni ce mace ta uku da mahaifin
ki ya aura kinsan da wannan ko?
To ina mai tabbatar miki da cewa ni ce mace
tafarko daya fara so a rayuwarsa".
10
Ummi tagyara zama tare da jan dogon numfashi
tace "jiddah khalifa ya tafi ba tare da na amfana
da zaman da nayi a cikin gdansu ba, face bacin
rai da mugun gani da idanuwa na suka gani.
Jiddah tabata rai tana yimata wani irin kallo tace
"wai me yasa kika fiye gaggawa ne ummi, anya
za ki rinka cimma nasara a kan abubuwa, idan
kika dubi tsarin khalifa gaba daya da yadda kike
ba abu ne mai sauki ba mallakar zuciyarsa sai
anyi da gasken gaske.
Ummi tace "to in banda abinki jiddah tawace
hanya zan samu nasara idan nayi hakuri, kada
kimanta fa shekaru hudu khalifa zaiyi a germany
kafin yadawo kasar nan, yana chan Ina nan zan
iya jan hankalinsa jiddah, dole xuciyata takaraya,
ke bari in gaya miki wani abu daya da ban yi
zaton zan gayawa wani ba, ina cikin gdan nan fa
ina kokarin jan hankalinsa na ganshi da mace
rungume a jikinsa a dakinsa, idan zan iya jan
ra'ayinsa zai kawo mace gdan nan ina cikinsa?
Jidda ta ja dogon tsaki tace "daman kina
tsammanin ko khalifa a karan kansa yake sonki
za ki rabashi da yammata ne, namiji irin khalifa
ko baice yana son 'yanmata, za su yi tabinshi tun
bai kula ba watarana sai ya kula, don hakama
shawarar da zan ba ki itace idan kinyi nasarar
mallakar khalifa to ki sanya hakuri mai yawa a
zuciyarki akan 'yanmatan da za suyi ta bibiyar
khalifa don ba namijin mace daya bane.
Ummi tajinjina kai tace "tabdijam hakika zan
girgiza kowa a kan khalifa ba zan hada miji da
wata ba, ba zan yi tarayya da wata macen a
dakin khalifa ba.
Jiddah takyalkyale da dariya tace "ummi manya
har khalifan ya zo hannu da za ki wannan cika
bakin.
Ta lumshe ido tace "kuma fa hakane maganar
dakika fada ne naji kamar har na mallake shi na
ji tsananin takaicin hadashi da wata da zanyi a
sunan kishiya .
*************
Malam musbahu yana cigaba da karfafa
zuciyarsa ga kaunar fatima tare da tattalin farin
cikinta sai dai ba ya samun hadin kanta sbda
tsananin kunyarta, ba ta iya sakewa dashi hakan
yasa tadaina sakewa a gidan duk abinda take
idan yashigo sai taji kamar za ta nutse a kasa
don kunya hakan na takura shi shima don ya fi
son tasaki ranta auyi soyayyar da za su fahinci
juna kafin lokacin auransu.
Ranar laraba da safe inna ta tursasawa fatima
kaiwa musbahu abincinsa a kokarin innar na
ganin sun shaku ta fuskar soyayya kamar yadda
tafahimci basu sake da junansu ba, fatima ba ta
son shiga dakin musbahu sbda maganar soyayya
da yake mata na daga mata hankali alhali bata
saba ba.
**********
Lafiya kalau khalifa yasauka a kasar germany
inda zai zaman karatun likita ,har yanzu damuwar
daya taho da ita daga nigeria yana makale a
ransa ga kewar iyayansa tamkar bai taba tafiya
ba sai a wannan lokacin, yana shirin shiga motar
dazata kaishi masaukinsa kamar daga sama yaji
an rike mai hannu, yajuyo dasauri yazu bawa
yarinyar ido, Anisa? Yafada cikin shakku dan ba
shi da tabbacin ko daidai yafada sunan.
Tayi murmushi tace "amma na ji dadi daka iya
kiyaye sunana.
Yace "nikam mamaki nayi dana ganki a kasar nan
yaushe kikazo?
Tace "sai mun zauna zan ba ka labari yanzu muje
naga masukinka ko za ka fara zuwa ganin na wa
masaukin?
Yace "ah ba komi inga waya ba sai mun tafi ba.
ta langabe kai tace "kada ka sanyaya min jiki
bayan na yi farin cikin ganinka kayi murnar
ganina.
Yace "hakika na yi farin cikin ganinki domin ina
bukatar abokin debe kewa a wannan kasa da
nazo.
Tace"to kayi hakuri mutafi mana.
Yace "to muje.
Sashensa daban a gdan da zai zauna, falo guda
daya da bedroom ba dai wani girma bane amma
akwai kayatarwa, kitchen kamar na mace sbda
tsaruwar da yayi shi kansa saida yayi sha'awar
ace yanada matar aure wadda za tarika dafa
masa abinci irin na mamansa, wadda yayi mugun
sabo dashi, a zaman da yayi da mamansa bai da
matsalar komi ta fuskar abinci duk abinda yakeso
shi ake masa, duk yawonsa da gararinsa bai iya
cin kowani abinci sai a gdansu sbda shi mutum
ne mai kyama da kuma son cin abinci mai dadi
duk dadin abinci bai iya ci sai a gdansu ko a
halin yanzu yunwa sosai a cikinsa bai san yadda
zai yi ba tunda bai iya girki ba ko ruwan tea bai
iya dafawa ba, hakan yasa tunda ya zube akan
gado bai kara motsawa ba dan ko takalmansa
anisa ce tazare masa.
Tana zaune daf dashi tace "khalifa bayan gajiya
kana tre da damuwa kataimaka kagaya min.
Ya lumshe ido yace "Anisa ba za ki iya magance
min matsalata ba shi yasa nace kar ki biyoni, ba
za ki ga walwala ta ba a wannan lokacin.
Ta marairaice kamar za tai kuka tace "dan Allah
kafada min Abbakar.
Yace "Anisa yunwa nakeji kuma ba za ki iya dafa
min irin abincin dazai gamsar dani ba.
Ta bushe da dariya tace "Abbakar idan yau ban
dafa maka abincin daya gamsar dakai ba to mata
na rako duniya, kuma har yanzu bakasan wacece
ni anisa ba, ko ka san cewa sbda na ji labarin
kana matukar son abinci mai dadi na shiga
fafutukan koyon girki ko ta ina?
Ya fiddo ido yna kallonta, tamike tace banga
tazama ba kafin kagama nazarin maganata bara
in dafa ma abincin.
Ido yabita dashi har ta fice yamaida idonsa kan
rufin dakin.
A wani party suka fara haduwa wanda wasu
dalibai suka shiga sbda nishadi, a lkcn bata dade
dafara xuwa mkarantar ba, tana zaune tare da
kawarta nafisa, suna hira wasu samari suka
tskoanesu har nafisa za tayi magana anisa
tahanata tace "kyalesu dan mu kulasu ne zo mu
bar gun.
Za suci gaba da binsu shi kuma khalifa yana
kallonsu ya aika a gaya wa wadannan samarin su
shiga hankalinsu su kyale su anisa ko yasa a
musu tsirara a gun, samarin wanda sakon yafito
daga gareshi yasa sukayi nasu gurin, ya aika
akira mai anisa.
Mamaki yakamata jin ance wai wani ne yake
kiransu kamar wasu 'ya'yansa taduvi dan aiken
tace "kaje kace a za mu zo ba. ..
Nafisa tayi saurin rufe mata baki tace kinsan
waye Abbakar muhammad? zo muje kawai.
Anisa tace "to me zai mana da har zai ce muzo?
Idan wani abu yakeso garemu mai zai hana shi
yazo da kansa? kai je kace bazamu zo ba.
Dan aiken khalifa yace "idan kika kara furta kalma
mara dadi akan maigidana zanje in gaya mai idan
kuwa nagaya mai daga wannan rana kin daina
farin ciki a wannan makarantar.
Ga dukkan alamu ita kawarki ta san shi ke kuwa
bakuwa ce shiyasa nayi miki uzuri.
Anisa takara fusata sosai za tayi magana nafisa
tarufe mata baki ta ja hannunta tace zo muje.
Har anisa ta dage akan ba ta zuwa sai kuma taga
bara taje taga abinda wannan mai gadarar yake
takama dashi tabashi mamaki.
Khalifa na zaune kan kujera tare da abokansa,
Anisa da Nafisa sukazo gabansu, Nafisan ce tayi
musu sallama ita kuwa anisan bakinta ne yayi
nauyi duk abinda nayi niyyan fada masa ya
gagara sai ido data bishi da shi.
Yayi murmushi yanuna musu gun zama yace
"kuzauna 'yammata.
Bata san sanda tazauna ba, gayen ya gaji da
haduwa ya yi mata ya burgeta anya kuwa ta taba
ganin matashi mai kyaun wannan a rayuwarta?
Tun daga wannan rana suke gaisuwar mutunci da
shi da abokansa, zuciyar Anisa ko yaushe a cike
yake da kuncin son khalifa batasan yadda za ayi
tasamu soyayyar ta sa ba, hatta nafisa duk yadda
suke ba sa boyewa juna sirrinsu amma ta kasa
gaya mata .
Lokacin dataji cieon so na neman hallakata ne ta
sanar da nafisa halin datake ciki, tayi dariya tace
"haba sister na san halin dakike ciki boye min din
da kikayi ne yasa na nuna miki ban sani ba.
Tace ni dai na ji ina mafita? Anisa kai tsaye
zance ba za kisamu khalifa ba, ba za ki iya
mallakarsa ba sai dai in Allah ya sa ravonki ne
amma sai kinyi hkuri mai nisa kafin kicin ma
nasara, kada kifito kigaya mai kina sonsa saidai
kici gaba da hakurin bin wasu hanyoyi dan kija
ra'ayinsa.
Anisa taci gaba da binciken rayuwar khalifa daki
daki me yakeso da wanda bai so, har a gdansu,
abinda yatsorata ta shi ne mata dayake
mu'amula da su sannan ba shi da niyyar aure.
Lokacin daya kammala karatunsa na Bayero duka
shekararta biyu a nata karatun, anan ne
hankalinta yatashi sosai ganin bbu hanyar da
zata kara ganinshi kuma tashiga binciken ina
yasa gaba a rayuwarsa, aiki zai fara ko ci gabada
karatu, bata samu cikakken byani ba sai da aka
dade tana fama da azaban ciwon sonsa a
zuciyarta, tadagawa mominta hankali akan sai an
maidta kasar germany ta karsa karatunta acan,
momin tadube ta cike da mamaki tace "ke kuwa
sbda me?
Kasancewar nisa ce diya tafari a gun mahaifiyarta
kamar kawa da kawa haka suke bata iya boye
mata duk wani sirrin daya shafeta ko meye shi,
taciro wayarta tanuna mata hoton khalifa tare da
bayyana mata halin datake ciki a kansa, tace
"momi tsawon shekaru biyu zuciyata ta rayu ckin
azabtacciyar soyayyar har wani lokaci inaji a
raina kamar mutiwa zanyi idan ban mallakeshi
ba, mom ba zan iya rayuwa bbu khalifa ba ke
kadai ce za ki iya min wannan taimakon.
Hnklin mmin yatashi sosai ta tausaya wa Anisa,
ta jima tana kallonta sannan tayi ajiyar zuciya
tace, "Anisa ba zan ga laifinki ba dan kin kamu da
soyayyar wanda kikeso tunda ba mutum ne yake
dorawa kansa so ba kuma zan yi iya kokarin inga
burinki ya cika.
Zan sa abanku yashirya maki zuwa germany
kiriga khalifa zuwa, zanyi ta binciken tafiyar shi
da saukar shi a kasan, inaso ki kasance a filin
jirgin lkcn dazai sauka domin kibashi mamaki,
dan zai sauka ckin kewar iyaye da abokansa Na
gida tabbas sai ya yi farin ckin ganinki.
Abu guda daya zan rokeki Anisa shi ne kitsare
mutuncinki, kada kiyarda soyayyarsa tasa kibiye
mishi ya lalata miki rayuwa.
Ta gyara zama tace "mom ban taba kallon khalifa
da wata manufa ba mara kyau burina shi ne
muzama miji da mata, ba zan iya bata rawana da
tsalle ba akan khalifa.
Mom tayi murmushi tace "anisa duniya fadi
gareta abinda kika sani shi kika sani wanda baki
sani ba baki sani ba, na san mutumcin soyayya
kuma ina darajata, ni ce mace ta uku da mahaifin
ki ya aura kinsan da wannan ko?
To ina mai tabbatar miki da cewa ni ce mace
tafarko daya fara so a rayuwarsa".