← Book details Yayi Sake Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 54

Sashe 52

Yayi Sake Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gid'a kai Mumy tayi tare da cewa
"Okay "
Kallon Mufidah yayi suka had'a ido yayi mata alamar da ido ta taso su tafi, langa6e kai tayi tana nuna mishi Mumy na wurin, amman sai ya d'aga kafad'a alamar shi ina ruwan shi .

Mumy tana kallon shi sai kawai ta tashi tana cewa
"Mufidah ki tafi kema ki huta kin ji 'yata "
Tana gama fad'in haka ta wuce kitchen, gwalo Musaddiq yayi mata don yana kula da kunyar da ta kamata, d'an hararar shi tayi irin ta wasan nan.

"ta so mu tafi habibty"
"zo ka d'auke ni idan kana son mu tafi "
"kai babyna agajiye nake, gashi kin k'ara nauyi sosai "
"toh shikenan tun da baza ka iya ba, naga kuma babyn ka ne ya samin nauyin tun da ba haka nake ba",ta fad'a cikin shagwa6a .

'Yar dariya yayi kafin ya k'arasa inda take yana cewa
"Sorry 'yammata na, duk nauyin da kika yi Musaddiq d'in ki bazai kasa d'aukar ki ba "
Hannun shi ya sanya tare da taimaka mata ta tashi tsaye, sannan ya d'auke ta cak suka fita daga side d'in Mumy zuwa nasu.

Yana shiga cikin parlourn wani k'amshin turare mai dad'i ya ziyarci hancin shi, ko'ina tsaf dashi cikin zuciyar shi yana godiya ga Allah da ya azurta mishi Mufidah matsayin matar shi, duk da girman cikin da yake jikin ta hakan bai hana ta tsaftace ko'ina ba, duk buk'atar da yazo mata da shi zata kar6e ta ko a fuskar shi baza ta nuna mishi rashin jin dad'in hakan ba, ko da kuwa bata so, shi yasa kullum sonta yake k'ara shiga cikin zuciyar shi.

Bai ajiye ta a ko'ina ba sai a bathroom, kallon ta yayi sai yaga tayi murmishi idan da sabo yaci ace ta saba da hakan, tun da kullum ya dawo daga office idan zai yi wanka tare suke yi, ba ma iya na lokacin ba kullum ma haka suke abin su.

Bayan sun gama wankan sun fito ne, kowanne d'aure da towel akan bed ya zaunar da Mufidah tare da zama kusa da ita yace
"habibty yaushe zamu fara zuwa siyayyan kayan babyn mu? "
Kallon shi take cikin mamaki kafin tace
"Sweetheart ina ce last week ka tak'ura wa Mumy taje dubai ta siyo komai"
Murmishi yayi tare da cewa
"Duk da haka baby na, ina son mu je ki za6i ra'ayin ki "
Girgiza kai tayi tana jan kunnen shi d'aya da hannun ta tace
"Wannan kunnen baya jin abin da nace mishi yau da safe, ba haka nace mishi a bar maganar nan ba "
Yatsina fuska yayi tare da cewa
"Wash habibty it hurts fah, zan rama nima "
Dariya ya bata ganin yanda yake sosa wurin da ta rik'e, kafin tace
"sai dai ka rame d'an samari "

Zaro ido yayi kafin yace "tabd'ijam baby nine d'an samari? "
Cikin dariyar tsokana tace "Ehh mana "
Janyo ta yayi cikin jikin shi yana gyara mata gashin kanta tare da cewa
"lallai baby kin rainani da yawa, ni yanzu daddy ne ina da Afnan ga shi kin kusa haifa min new baby's "
Ya k'arasa fad'i yana shafa cikin ta tare da kissing d'in shi.

"baby's naji kace ba?"
Lumshe idanun shi yayi tare da bud'e su yace
"Yes of course insha Allah baby's zaki haifa min "
Kwa6e fuska tayi tace
"Wayyo Musaddiq ba kasan yanda ake shan wahalar haihu ba ne "

Dariya ta bashi ganin yanda tayi, cikin lalla6a ta yace
"Haba wacce wahala kuma baby, lafiya zaki haihu mybe ma kina bacci zan tashe ki nace kin haifa mana baby "

Sosai maganar shi ta bata dariya, nan ta shiga yin dariyar shima ya taya ta, tsaya wa yayi da tashi dariya ya zuba mata ido yana kallon ta cikin wata irin sha'awar ta,

"I luv u Mufidah "
Ya furta hakan cikin muryar shauk'in ta,
"I luv u too "
Mufidah ta mayar mishi da martanin maganar.

Sake matse ta yayi cikin jikin shi yana lalubar bakin ta, kissing d'in ta ya fara yi, nan fah ya fara aika mata da zafafan kalamai tare da sak'onnin shi zuwa gare ta, cikin en mintuna suka fara shiga wata duniyar ta daban.

*** *** ***
Cikin Mufidah ya shiga watanni na 8 ya girma sosai, duk ta bi ta kumbura ga girman ciki, zama dakyar tashi dakyar don wani lokacin sai an taimaka da tashi tsaye.

Ba k'aramin tausaya mata Musaddiq dasu Mumy suke ba, kullum cikin bata kula wa da addu'ar Allah ya sauke ta lafiya duk wani masoyin ta yake, don cikin yafi na Afnan girma sosai kuma tafi shan wahala.

Gaba d'aya ta k'agu taga ta haihu ko ta huta da wannan wahalar da take faman sha, wani lokacin ita take k'arfafa wa Musaddiq gwiwa ganin duk yanda ya karaya ganin yanda take shan wahala.

Sam hankalin shi yanzu ba'a kwance yake ba, hospital d'in ma yanzu bai fiye zuwa ba sosai, ko yaje ma hankalin shi yana gida, haka zai dawo gidan ya sata a gaba yayi ta kallon ta yana tambayar ta ko akwai inda yake mata ciwo, ko tana son wani abin.

A haka lokaci yana tafiya, rana ku na wuce wa har cikin Mufidah ya shiga wata na tara da sati uku, ta kusan cinye wata na goma shiru babu alamar haihuwa, sai dai ciwon mara da baya da take yi, wannan kuma daman idan ciki ya tsufa haka zaka yi ta fama har zuwa lokacin da za'a haihu lafiya.

Musaddiq gajiya yayi da ganin yanda take shan wahala duk ta rame sai kumburi da k'aton ciki da farin da ta k'ara yi, ya fad'a wa Mumy kawai ayi mata cs a cire cikin, nan Mumy tak'i yarda sam saboda duk wani gwaje gwaje da aka yi mata an tabbatar lafia qlau take da babyn, sai dai kawai lokacin haihuwar ne da bai zo ba.

Sai da cikin Mufidah ya shiga wata 10 dai dai, a wata safiyar monday ta tashi da nak'uda, nan da nan suka wuce hospital d'in Dr Musaddiq, kai tsaye labour room na daban aka wuce da ita.

Musaddiq kasa fita yayi daga room d'in yana rik'e da ita a jikin shi, ga Doctor Aishat nd nurse Billy ladan suna kanta lol, duk wani taimakon da ya kamata su yi mata suna mata.

Mufidah wahala dai tasha a wannan lokacin, don sai ta ga haihuwar Afnan sauk'i gare ta fiye da wannan, Musaddiq har da hawayen tausayin habibty d'in shi, tun safe ake fama har zuwa daf da mangarib sannan Allah ya sauke ta lafiya, ta haihu beautiful baby's boy's d'in ta, masu kama da Musaddiq like father like son.

Tuni Musaddiq mai hawaye ya koma yin dariyar farinciki, bayan angama gyara su tsaf ne an kaisu d'akin hutu, tukunna su Mumy suka samu ganin su.

Kowanne ka kalle shi yana cikin farinciki da murna da wannan k'aruwar da aka samu ta yara biyu maza, Musaddiq wanda baki yak'i rufuwa yana zaune kusa da Mufidah da take baccin wahalar da ta gama sha.

Dr Muh'd wanda ya ke d'auke da d'ayan babyn ya kalli Musaddiq yace
"lover boy sai a daina kukan tausayi a koma na farinciki "
Gaba d'aya aka kwashe da dariya, yayin da Musaddiq ya harari Muh'd, sai washe gari da safe aka sallame su zuwa gida, kafin su k'araso tuni 'yan uwa da abokanan arzik'i sun zo don taya su murnar samun kyautar Allah wanda kud'in ka ko mulkin ka bazai sa ka samu ba, sai dai idan Allah ya baka, Allah ya bamu yara masu albarka ya kare mana su tare da basa ilimi mai amfani, ya tarbiyyantar mana dasu irin tarbiyyar addinin islam, Amin.

Mumy dawo da Mufidah tayi side d'in ta domin bata kula sosai, tana kuma taya ta rainon 'yan biyu don rainon su sai da taimako, hakan kuwa ba k'aramin tak'ura wa Musaddiq aka yi ba, shima sai ya tattara ya dawo side d'in cikin d'akin shi na da, Afnan sai rawar kai ake an samu k'anne har biyu.

Daren ranar Musaddiq ya shiga d'akin Mufidah ya tarar da ita kwance kan bed, ga yaran kwance kusa da ita suna baccin su hankali kwance, k'arasa wa yayi ya zauna kusa da k'afafun ta yana cewa
"Babyna kin yi bacci ne? "
Tashi tayi tana murmishi tare da koma wa kusa da shi ta kwanta a cikin jikin shi, k'ara gyara mata kwanciyar yayi a jikin shi yanda zata fi jin dad'i sosai,
"ban yi bacci ba, ina jiran ka ne don nasan zaka shigo "
Mufidah ta bashi amsa, wani dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar shi, kullum Mufidah k'ara shiga zuciyar shi take, tana bashi duk wata kulawa da ta kamata, shafa fuskar ta yayi da hannun shi yace
"Ngde da wannan kulawar take habibty "
Kafin ya cigaba da cewa
"wanne suna kike ganin zamu sanya wa yaran mu? "
D'an murmishi tayi tana cewa
"Ni ban da wani za6i sai naka, duk sunan da ka sanya musu yayi min "

Wani murmishin jin dad'in abin da tace yayi, sake rungume ta yayi a jikin shi yana shak'ar daddad'an k'amshin turaren yace
"sunan da nake son sanya musu shine, babban zai ci sunan Abubakar sadeeq d'ayan kuma sunan Muh'd ko ya kika gani idan bai yi ba sai ki fad'i wanda kike so"

Wasu hawaye masu zafi ne suka zubo wa Mufidah, tabbas daman kudurta cikin zuciyar ta idan Allah yasa ta samu d'a namiji sunan Sadeeq zata mayar shi, sai gashi Musaddiq ma hakan ne cikin zuciyar shi.

D'ago kanta yayi yana girgiza kanshi tare da sanya hannun shi yana goge mata hawayen fuskar ta yace
"Kiyi hak'uri Mufidah addu'a kad'ai zaki na yiwa Yah sadeeq, don ita kad'ai ce zamu yi mishi mu nuna kaunar shi a gare mu, bana son ganin kukan ki, ki daina please"
Chapter 52 · 0% Book details