← Book details Yayi Sake Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 54

Sashe 4

Yayi Sake Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"ita ce mana "
Cewar mufidah, cikin tsokana yace "lallai yaran nan kun girma da yawa wannan ae Kun kusan kamo ni "mufidah dariya tayi yayin da nabila take sunkuyar da kanta k'asa ganin irin kallon da Yah Omar yake mata.

Nan fah ya dunga tsokanar su har suka k'araso gida, iyayen shi sunyi matuk'ar jin dad'in dawowar yaron nasu lafia.

Kuma a ranar su mufidah suka dunga gayyatar mutane suna fad'a musu ranar asabar ne partyn da suka shirya wa Yah Omar, ta 6angaren Yah Omar ma ya sanar da abokanan shi na nan har dasu sadeeq da musaddiq 'ya'yan abokin mahaifin nashi kuma sun bashi tabbacin xasu xo...........

Aishat A muh'd
[13/11, 2:04 p.m.] Aysher Muhd Writr: 🌲 *YAYI SAKE!*🌲

*written by*
Aishat A muh'd

♻ *E.W.F*

*Page 5*

_Washe gari_

Mufidah da nabila ba xama ranar sai shirye shirye suke har xuwa lokacin da xa'a gabatar da partyn, hatta kayan su iri d'aya ne da nabila komai da komai shima Yah Omar kayan da xai sanya colour d'in su d'aya da na su mufidah sai dai shi na maxa ne abin da ya banbanta kenan.

Har xuwa lokacin da suka sanya karfe 4 na yamma xuwa karfe 7 na dare xa'a tashi, don hka xuwa karfe hud'un duk friend's din su mufidah sun xo na skul, Wow! masha Allah na furta lokacin da na hango mufidah ta gama shirya wa cikin had'ad'd'an lace green colour nd touch d'in flowers red d'inkin riga da siket ne sun yi matuk'ar yi mata kyau sosae, mai make up suka d'auko ta tsantsara musu kwalliya, hka ma nabila tayi kyau sosae xuwa karfe 4 sun bar gidan sun tafi wajen da suka kama don yin partyn.

Cikin hall di'n ya had'u iya had'uwa ya sha decoration da kwalliyar flowers ga k'aton birthday cake mai hawa uku, friend's din Yah Omar ma sun xo sosai duk inda mufidah ta gifta idanun mutane na kanta har da mata kuwa en uwanta don ba k'aramin had'uwa tayi ba, wani abin mamakin shine duk inda Yah Omar ya d'auke kafar shi to nan nabila xata ajiye ta ta sai bata kulawa yake alamun dai sun bayyana wa kansu soyayya, mufidah na ankare dasu sai dai tayi murmishi kawai kuma tayi farinciki sosai da hkan sun dace da junan su.

"Haba musaddiq don Allah kasan mun yiwa Omar alk'awarin xamu je gashi kace ka fasa xuwa "
Cewar Yah sadeeq kenan lokacin da ya gama shirya cikin wata tsadaddiyar shadda purple ce tayi mishi kyau sosae, ya shigo d'akin musaddiq don ganin ko ya shirya sai yayi turus ganin musaddiq a xaune yana sarrafa laptop ko alamar shirya wa bai yi ba
"lafia musaddiq baka shirya ba gashi karfe 5 ma ta wuce? "
Cikin yatsina fuska yace "Yah sadeeq na fasa xuwa fah "
So shine sadeeq yake fad'a mishi sun yiwa Omar alk'awarin xuwa,nan dai dakyar Yah sadeeq yake lalla6a musaddiq ya yarda xai je, ajiye laptop d'in yayi bayan ya kashe ta ya mik'e tsaye tare da cewa
"amman baxa mu dad'e ba ko brother don ni fah banson hayaniya? "

Murmishi sadeeq yayi tare da cewa "Haba musaddiq ka d'aure mu xauna xuwa a tashi kasan yanda muke dasu Omar kamar en uwan jini "
"alright bari na shirya amman idan hayaniya ta dame ni xan gudu na bar ka " Dariya Yah sadeeq yayi yana cewa "Ehhh na dai ji ".

Toilet musaddiq ya shige shi kuwa Yah sadeeq ya fita daga bedroom d'in nashi, cikin mintuna talatin musaddiq yayi wanka a gurguje ya shirya cikin wani yadi blue colour yayi matuk'ar kar6ar shi yadin don bai fiye sa manyan kaya ba sai ta kama, bayan ya taje sumar kanshi ya shafa mata mayuka sannan ya d'aura tsadadden watch di'n shi tare da fesa perfumes masu matuk'ar k'amshi, sannan ya fito xuwa falo inda Yah sadeeq yake jiran shi.

Yana fito wa palon mumy da Yah sadeeq suka bishi da kallo yaushe rabon su ganshi da manyan kaya gashi kuma suna mishi kyau Idan ya saka mumy ce ta fara cewa
"Masha Allah d'an nawa yayi kyau Allah yasa idan aka je a sama min suruka"

Yah sadeeq ya tuntsire da dariya kafin yace "tabbb mumy wannan doctor d'in idan matan suka ganshi guduwa ma xasu yi saboda fuskar ba fara'a "

Cikin shagwa6a yace "Mumy ko kiyi wa brother magana idan ba hka ba xan mishi allura yanxu nan kuwa "
Don Yah sadeeq Akwai shi da tsoron allura kamar mace nan kuwa ya marairaice fuska yana cewa "Haba d'an k'anina na dai na wuce mu je ni don Allah kada yi min xancen wata injection ina xama na lafia"

Nan musaddiq da Mumy suka tuntsire da dariya shi kuwa Yah sadeeq da sauri ya fice daga falon yana cewa "ni nayi gaba ina jiran ka a mota "

Musaddiq ne ya kalli mumy cikin murmishi yace "mun tafi sai mun dawo "
Ya K'arasa fad'i yana bata peck a kumatu ita ma cikin murmishi xuciyar ta cike da k'aunar d'an nata tace "Allah ya dawo min daku lafia Allah ya tsare min ku "
"Ameeen mumyn mu thanks for your du'a,bye"

Daga hka ya juya ya fita mumy ta bishi da kallon k'aunar 'ya'yan ta, su kad'ai Allah ya mallaka mata ba K'aramin so take musu ba.

A parking space ya tarar da Yah sadeeq xaune cikin mota yana jiran shi don hka shima shiga yayi ba tare da 6ata lokaci ba Yah sadeeq yayi wa motar key sannan suka fice daga gidan duk wanda ya gansu sai sun bashi sha'awa saboda yanda suka yi matuk'ar yin kyau gasu kyawawa tubarkallah, motar da suke ciki ma kanta abar kallo ce.

Cikin mintuna da basu gaxa 50 ba suka K'arasa wajen partyn, waje Yah sadeeq ya samu yayi parking sannan suka fito jerawa suka yi kamar wasu tagwaye suka nufi wajen sam baxa kaji irin tashin sautin kid'an nan ba wanda xai dami mutane, slow music ne yake tashi a wajen.

Shigowar su wajen shi ya janyo hankalin mutanen wajen kansu don ba k'aramin burge su suka yi ba musamman ma musaddiq yawancin matan wajen suka raja'a da kallon shi, irin kallon nan na daman kace kana so na.

Yah Omar yana tsaye gaban cake mufidah na gefen daman shi yayin da nabila tana hagun shi kenan sun sashi a tsakiya,xai yanka cake din kenan yaga shigowar su musaddiq don hka ya dakata da yankawar wajen su ya k'arasa suka rungume junan su cikin farinciki Kafin su saki juna Yah Omar ya kalli sadeeq yace
"abokina musaddiq fah ya girma nema ma yake yafi mu girma ya kamata mu ajiye iyalai mun girma "
Dariya ya sadeeq yayi suka tafa da Yah Omar sannan yace "k'warai da gaske abokina ka kawo shawara mai kyau "
Shi kuwa musaddiq murmusa wa kawai yayi, suna cikin tafiya xuwa gaban cake din ya Omar ya cigaba da cewa
"gwara mu yi mu bawa k'annan namu fili su ma su yi "

Dai dai lokacin sun k'araso wajen don hka Yah Omar ya kalli mufidah yace
"sadeeq ka gane wannan kuwa?"
Ya fad'i yana nuna mufidah da hannu, d'ago kan shi yayi ya kalli mufidah ita ma anyi sa'a ta d'ago kanta nan idanun su suka sark'e da na juna take Yah sadeeq yaji wani abu a tattare shi yana bin ilahirin jikin shi, lokaci d'aya sadeeq yaji wani son mufidah a cikin xuciyar shi wanda ake cewa love at first sight gaba d'aya ya mance a inda suke ya kasa janye idanun shi a kanta.

Mufidah ce ta janye idanun ta a cikin xuciyar ta tace wannan ya fiye kallo da yawa ta d'an murgud'a bakin ta Kad'an hkan da tayi sai sadeeq ya ji ta k'ara shiga xuciyar shi, ya Omar da ya ankare da kallon da yake yiwa mufidah sai yayi Murmishi tare da dafa kafad'ar sadeeq yayi gyaran murya tare da cewa
" uhm uhm abokina ko er gida xa'a yi NE? "
Ya fad'i hkan saitin kunnen sadeeq, firgigit sadeeq yayi kamar wanda ya tashi daga bacci d'an sosa k'eya yayi tare da cewa
"da xaka ba ni ae da naji dad'i "
Sannan kuma ya jiyo ya sake kallon mufidah tukunna yace "gaskia ba don ka fad'a min ba baxan ta6a gane ta ba "
Yah Omar yayi dariya tare da cewa "sadeeq musaddiq wannan ita ce k'anwa ta mufidah, ke kuma mufidah wad'annan sune sadeeq abokina musaddiq kuma k'anin shi, kuma nasan kin san Alhj Abubakar daddy aminin abba "
Gid'a kai tayi alamar ehh ta gane sannan cikin sanyin murya tace
"ina yinin ku"
Sam bata kula da musaddiq ba shi ma hkan jin wata murya mai shegen dad'i tana gaida su yasa shi jiyo wa ya Kalli wajen nan kuwa suka had'a ido da musaddiq tuni annurin fuskar shi da annurin fuskar ta suka d'auke lokaci d'aya ta wani juyar da kanta gefe, sai yah sadeeq ne ya amsa gaisuwar ta ta cikin murmishi, nabila kuwa cikin mamaki take kallon musaddiq sai dakyar ta iya bud'e baki tace
"malam ina yini?"

Dak'yar ya iya bud'e bakin shi yace "lafia " daga hka yaja bakin yayi shiru, yah Omar kallon nabila Yayi yace
"ashe kun san shi? "
"ehhh malamin mu ne "
Cikin mamaki Yah Omar yace "malamin ku kuma shi da likita ne kuma, mene gaskiyar xancen sadeeq? "
"wlh Omar ra'ayin musaddiq ne amman naji yana cewa ya fara gaji da koyarwar, xai fara aiki a wani hospital kafin a kammala gina nashi "

"okay hkan yayi kyau mu yanka cake din don idan muka biye wa hirar nan xamu iya 6atawa mutane lokaci "
"alright hkan yayi kyau"
Chapter 4 · 0% Book details