Sashe 3
Yayi Sake Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sallama ta shiga umman nabila da take tsaye 6angaren dinning table tana shirya abinci akai ta jiyo tare da amsa sallamar ganin mufidah ce yasa ta fad'ad'a fuskar ta da fara'a tare da cewa
"Oyoyo my daughter, baki da kirki mufidah yaushe rabon ki da shigowa cikin gidan nan sai dai ki sauke nabila a bakin gate "
Umman nabila ta fad'a cikin wasa, Murmishi mufidah tayi tare da kama kunnen ta tace "sorry ammin mu na tuba na dai na"
Dariya umman nabila tayi tare da cewa "Okay shikenan ya wuce sauran ki k'ara "
Da sauri mufidah tace "baxan ma k'ara ba Insha Allah ammi "
Dariya suka yi gaba d'ayan su sannan umman tace "Allah yasa hka ne, ina umman taki ?"
"tana gida "
Sai a lokacin suka gaisa tukunna ta nufi bedroom d'in nabila a gaban dressing mirror ta same ta tana shirya wa alamar fitowar ta daga wanka kenan nan fah suka sakar wa junan su murmishi sannan mufidah ta xauna gefen bed tana cire mayafin da tayi rolling d'in kanta ta furta
"wash Allah na nayi matuk'ar gajiya yau "
Cikin mamaki nabila tace "gajiyar me kuma? "
"yanxu dai ya jikin na ki? "
"ah na samu lafia daman fah ciwon kai ne na tashi dashi "
"Ayyah Allah ya k'ara sauk'i sannu " Cewar mufidah
"Ameeen ya rabbi "
Cikin tsokana nabila tace "kin had'u da mutumin na ki ne yau? "
cikin rashin fahimta mufidah tace "wa kike nufi? "
"musaddiq Abubakar man "
Wata dariya ce ta kubce wa mufidah ta dunga yi yayin da nabila ta saki baki tana kallon ta kawai cike da mamaki sai da tayi dariyar ta ta gama har da hawaye sannan ta bawa nabila labarin abin da tayi mishi, nan fah nabila me xatayi ban da dariya daman tasan mufidah baxa ta kyale shi ba sai tayi mishi wani abun.
"Allah k'awata baki da kirki amman ina rok'an ki ki rabu dashi a matsayin ki na 'ya mace ki rabu dashi kuma ki kiyaye abin da xai sake had'a ku a gaba"
D'an hararar ta mufidah tayi tare da cewa Kina nufin ya ci bulus kenan marin da yayi min ?"
"Haba k'awata ban sanki da wannam halin ba ki rabu dashi please "
"Okay naji na yarda amman da sharad'i guda idan yayi min xan rama"
Mufidah tana rufe bakin ta umman nabila ta shigo d'akin tana cewa "ku dai idan kuka shigo d'akin kuna surutu mance wa da komai kuke toh lokacin cin abinci yayi don hka oya ku fito mu ci"
"toh ummah " suka fad'i sannan suka fito daga d'akin dinning table suka nufa nan suka ci abinci sannan suka dawo falo suna ta6a hira sai yamma sannan mufidah ta tafi gida...............
Aishat A muh'd ✍🏻
[13/11, 2:03 p.m.] Aysher Muhd Writr: 🌲 *YAYI SAKE*🌲
*written by*
Aishat A muh'd
♻ *E.W.F*
_Wannan shafin na kine k'awata sadeey S Adam (SaNaz), ngde da k'aunar da kike nuna min Allah ya bar xumunci ya k'are min ke a duk inda kike, ina miki fatan alkhairi_😍
*Page 4*
*WACE CE MUFIDAH*
Mufidah El Hussaen 'yace a wajen Alhj EL Hussein da hajia Aisha, mahaifin ta haifaffen garin d'ambatta ne sana'a ce ta dawo da mahaifin shi cikin garin kano iyayen shi ba wasu masu kud'i ba ne rufin asirin Allah ne da hka yayi karatun boko dana addini da yake shi kad'ai suka mallaka akan fannin Shari'ah yayi karatun cikakken alk'ali ne Wanda yasha gwagwarmaya Kafin kuma yayi ritaya ya koma harkar kasuwanci ta siyar da motoci.
Alhj El Hussaen baxa ka kirawo shi da mai dukiya sosai ba yana da arxikin shi dai dai gwargwado yana xaune a sultan crescent, matar shi hajia Aisha uwar 'ya'yan shi bafulatana ce amman ta samu karatu sosai don ita ma k'wanan nan ta bar aiki tana matsayin babbar lecture da ake damawa dasu a makarantar buk.
Yaran su biyu Omar da mufidah sune yaran da Allah ya basu Yah Omar yana k'asar london yana karatun shi ya ma kammala karatun cikin wannan watan suke sa ran dawowar tashi.
Mufidah itace mai bin Yah Omar ya bata wajen shekara 4, ita ma ta kammala karatun ta na primary da secondary yanxu tana buk ta d'ora karatun ta, tana masifar son karatun na ta bata k'aunar abin da xai ta6a neman ilimin nata, kuma ba iyakar ilimin boko ta tsaya ba har da na addinin islam ta ma yi saukar alqur'ani da sauran mahimman littatafai na addini dai dai gwargwado tana da ilimi anan 6angaren.
Kuma ta kasance kyakkyawar yarinya mai kama da mahaifin ta amman farin umman ta ta d'auko duk da uban shi ma ba bak'i ba ne, gashi akwai ta kirki bata shiga harkar da bata shafe ta ba akwai hankali da nutsuwa sai dai aka ta6a ta bata kyale wa kamar yanda musaddiq Abubakar ya ta6o ta.
*WACE CE NABILA K'AWAR TA*?
Nabila yarinya mai hankali da nutsuwa ga hak'uri maman ta hajia Amina k'awa ce ga hajia Aisha umman mufidah tare suka yi koyarwa a buk k'awaye ne sosai shi yasa mufidah da nabila suka xama k'awaye sosai, sai dai ita nabila mahaifin ta ya rasu kuma ita kad'ai ce ta rayu cikin 'ya'yan ta da take haihuwa duk mutuwa suke, gashi ita ma nabilan kyakkyawa ce sai dai mufidah ta fita kyau, duk tare suka yi karatun su kan su a had'e yake.
_mun dawo labari_
Tun da suka shiga mota musaddiq Ko magana ya kasa saboda tsabar takaici har suka k'araso gida, Yah sadeeq yana parking da mota musaddiq ya fito ya nufi cikin gidan d'akin shi ya shige ya cire kayan jikin shi ya shiga toilet wanka yayi sannan ya fito ya shirya cikin wata riga mara hannu red colour da ash d'in 3quater bayan ya fesa perfumes ya fito xuwa babban palon gidan, anan ya tarar da mumy da Yah sadeeq a xaune suna hira xama yayi kusa da mumy yace
" I'm hungry Mumy "
Har Yah sadeeq ya bud'e baki xai yi magana kamar musaddiq yasan abin da xai fad'a wa mumyn aikuwa yayi mishi alamar kada ya fad'a mata don hka yaja bakin shi yayi shiru kawai.
" my son me xa'a kawo maka?" Cewar mumy
D'an yatsina fuska yayi tare da cewa " Duk abin da kika dafa mumy, amman a had'a min da fura mai sanyi"
"kaje dinning table xaka samu komai acan akwai kuma fura cikin frige din kusa da dinning table, maxa tashi kaje ka ci"
Tashi yayi ya nufi 6angaren dinning table d'in yana yatsine fuska, shi kuwa Yah sadeeq yana danne dariyar da taxo mishi.
Cikin nutsuwa ya d'ebe abincin yaci Kad'an sannan ya sha furar nan da yawa, bayan ya gama sai ya dawo palon amman bai xauna ba ya kalli mumy da Yah sadeeq yace
"ni xan je na kwanta na huta "
"Okay son ae gwara ka huta " Cewar mumy yayin da Yah sadeeq yace
"ae dole ma ka huta brother saboda ka sha........... "
Kafin ya K'arasa fad'i musaddiq ya harare shi yayi gaba shi kuwa Yah sadeeq dariya ya tuntsire da ita mumy kuwa cewa take
"je ka huta son ka rabu da yayan nan naka sarkin tsokana "
"auuu hka xaki ce mumy "
Cikin murmishi mumy tace "Ehhh mana "
Nan dai suka cigaba da hirar su cikin kwanciyar hankali.
A 6angaren musaddiq kuwa ba hutawar xai yi ba kawai tunanin Wanda yasa aka kawo mishi wannan abin kaxantar yake amman duk tunanin shi ya rasa gano ko wane, amman lallai xan bincika, da hka bacci ya d'auke shi.
*WANE NE MUSADDIQ ABUBAKAR*?
Dr Musaddiq Abubakar kyakkyawan saurayi ne hadadden guy wanda ilimin addini dana boko suka ratsa shi nutsatstsan mutum ne ma'abocin miskilan ci da rashin son hayaniya, bai dad'e da kammala karatun likita ba, mahaifin shi yana gina mishi asibiti, sai dai kuma musaddiq don ra'ayin kanshi yake koyarwar amman shi cikakken likita ne.
Iyayen shi kuwa Alhj Abubakar da hajia khadija su biyu ne 'ya'yan su daga Abubakar sadeeq Wanda yaci sunan uban nashi suna ce mishi sadeeq sai kuma musaddiq ,suna xaune cikin xaman lafia da kwanciyar hankali gashi suna k'aunar junan su sosai har baxa ka iya banbance tsakanin sadeeq da musaddiq wanne yafi k'aunar d'an uwan shi ba, mahaifin shi d'an kasuwa ne hka shima sadeeq sana'ar mahaifin nashi yake.
Alhj Abubakar da Alhj El Hussaen abokanan juna ne na k'ut da k'ut,amintaka ce a tsakanin su sosai hka ma matan su.
_mun dawo labari_
Tun daga lokacin mufidah take xuwa skul da wuri idan ta fuskanci ranar musaddiq yana da lecture a ranar don hka bai k'ara korar ta ba, sai dai fah har yanxu haushin yarinyar yaji sosai, ita kuwa bata k'ara bi ta kanshi ba gashi duk test d'in da yake musu da assignment kusan ita ce kan gaba wajen ci,kuma yaga kusan lecture's din makarantar suna yaba ma yarinyar sosai.
Ana cikin hka Yah Omar yayi waya xai dawo nan da k'wana 2 don Allah mufidah ba xama ita da nabila suna kok'arin had'a mishi partyn murnar kammala makarantar shi da kuma murnar xagoyowar shekarar haihuwar shi, sosai suke shirya Inda xa'a yi partyn da a abubuwan da xa'a buk'ata a wajen.
Ranar Friday da misalin karfe 7 jirgin su Yah Omar yayi landing a airport d'in malam aminu kano, mufidah da nabila ne suka d'aukar shi yana fito wa daga cikin jirgin mufidah ta nufi inda yake da gudu ta rungume shi cikin tsananin farincikin ganin d'an uwan nata ,nan shima ya rungume ta cikin murnar ganin kanwar tashi xuwa can ta sake shi tare da kallon shi cikin murmishi tace
"Yah Omar ka ga yanda ka koma lallai london ta kar6e ka"
"lallai yarinyar nan kin rainani daman can da Kyan nawa "
Ya Omar ya fad'a cikin dariya a lokacin kuma nabila ta k'araso tana gaida shi tare da yi mishi sannu da xuwa rik'e baki yah Omar yayi tare da cewa
"kai kai wannan ba dai itace nabila ba?"
"Oyoyo my daughter, baki da kirki mufidah yaushe rabon ki da shigowa cikin gidan nan sai dai ki sauke nabila a bakin gate "
Umman nabila ta fad'a cikin wasa, Murmishi mufidah tayi tare da kama kunnen ta tace "sorry ammin mu na tuba na dai na"
Dariya umman nabila tayi tare da cewa "Okay shikenan ya wuce sauran ki k'ara "
Da sauri mufidah tace "baxan ma k'ara ba Insha Allah ammi "
Dariya suka yi gaba d'ayan su sannan umman tace "Allah yasa hka ne, ina umman taki ?"
"tana gida "
Sai a lokacin suka gaisa tukunna ta nufi bedroom d'in nabila a gaban dressing mirror ta same ta tana shirya wa alamar fitowar ta daga wanka kenan nan fah suka sakar wa junan su murmishi sannan mufidah ta xauna gefen bed tana cire mayafin da tayi rolling d'in kanta ta furta
"wash Allah na nayi matuk'ar gajiya yau "
Cikin mamaki nabila tace "gajiyar me kuma? "
"yanxu dai ya jikin na ki? "
"ah na samu lafia daman fah ciwon kai ne na tashi dashi "
"Ayyah Allah ya k'ara sauk'i sannu " Cewar mufidah
"Ameeen ya rabbi "
Cikin tsokana nabila tace "kin had'u da mutumin na ki ne yau? "
cikin rashin fahimta mufidah tace "wa kike nufi? "
"musaddiq Abubakar man "
Wata dariya ce ta kubce wa mufidah ta dunga yi yayin da nabila ta saki baki tana kallon ta kawai cike da mamaki sai da tayi dariyar ta ta gama har da hawaye sannan ta bawa nabila labarin abin da tayi mishi, nan fah nabila me xatayi ban da dariya daman tasan mufidah baxa ta kyale shi ba sai tayi mishi wani abun.
"Allah k'awata baki da kirki amman ina rok'an ki ki rabu dashi a matsayin ki na 'ya mace ki rabu dashi kuma ki kiyaye abin da xai sake had'a ku a gaba"
D'an hararar ta mufidah tayi tare da cewa Kina nufin ya ci bulus kenan marin da yayi min ?"
"Haba k'awata ban sanki da wannam halin ba ki rabu dashi please "
"Okay naji na yarda amman da sharad'i guda idan yayi min xan rama"
Mufidah tana rufe bakin ta umman nabila ta shigo d'akin tana cewa "ku dai idan kuka shigo d'akin kuna surutu mance wa da komai kuke toh lokacin cin abinci yayi don hka oya ku fito mu ci"
"toh ummah " suka fad'i sannan suka fito daga d'akin dinning table suka nufa nan suka ci abinci sannan suka dawo falo suna ta6a hira sai yamma sannan mufidah ta tafi gida...............
Aishat A muh'd ✍🏻
[13/11, 2:03 p.m.] Aysher Muhd Writr: 🌲 *YAYI SAKE*🌲
*written by*
Aishat A muh'd
♻ *E.W.F*
_Wannan shafin na kine k'awata sadeey S Adam (SaNaz), ngde da k'aunar da kike nuna min Allah ya bar xumunci ya k'are min ke a duk inda kike, ina miki fatan alkhairi_😍
*Page 4*
*WACE CE MUFIDAH*
Mufidah El Hussaen 'yace a wajen Alhj EL Hussein da hajia Aisha, mahaifin ta haifaffen garin d'ambatta ne sana'a ce ta dawo da mahaifin shi cikin garin kano iyayen shi ba wasu masu kud'i ba ne rufin asirin Allah ne da hka yayi karatun boko dana addini da yake shi kad'ai suka mallaka akan fannin Shari'ah yayi karatun cikakken alk'ali ne Wanda yasha gwagwarmaya Kafin kuma yayi ritaya ya koma harkar kasuwanci ta siyar da motoci.
Alhj El Hussaen baxa ka kirawo shi da mai dukiya sosai ba yana da arxikin shi dai dai gwargwado yana xaune a sultan crescent, matar shi hajia Aisha uwar 'ya'yan shi bafulatana ce amman ta samu karatu sosai don ita ma k'wanan nan ta bar aiki tana matsayin babbar lecture da ake damawa dasu a makarantar buk.
Yaran su biyu Omar da mufidah sune yaran da Allah ya basu Yah Omar yana k'asar london yana karatun shi ya ma kammala karatun cikin wannan watan suke sa ran dawowar tashi.
Mufidah itace mai bin Yah Omar ya bata wajen shekara 4, ita ma ta kammala karatun ta na primary da secondary yanxu tana buk ta d'ora karatun ta, tana masifar son karatun na ta bata k'aunar abin da xai ta6a neman ilimin nata, kuma ba iyakar ilimin boko ta tsaya ba har da na addinin islam ta ma yi saukar alqur'ani da sauran mahimman littatafai na addini dai dai gwargwado tana da ilimi anan 6angaren.
Kuma ta kasance kyakkyawar yarinya mai kama da mahaifin ta amman farin umman ta ta d'auko duk da uban shi ma ba bak'i ba ne, gashi akwai ta kirki bata shiga harkar da bata shafe ta ba akwai hankali da nutsuwa sai dai aka ta6a ta bata kyale wa kamar yanda musaddiq Abubakar ya ta6o ta.
*WACE CE NABILA K'AWAR TA*?
Nabila yarinya mai hankali da nutsuwa ga hak'uri maman ta hajia Amina k'awa ce ga hajia Aisha umman mufidah tare suka yi koyarwa a buk k'awaye ne sosai shi yasa mufidah da nabila suka xama k'awaye sosai, sai dai ita nabila mahaifin ta ya rasu kuma ita kad'ai ce ta rayu cikin 'ya'yan ta da take haihuwa duk mutuwa suke, gashi ita ma nabilan kyakkyawa ce sai dai mufidah ta fita kyau, duk tare suka yi karatun su kan su a had'e yake.
_mun dawo labari_
Tun da suka shiga mota musaddiq Ko magana ya kasa saboda tsabar takaici har suka k'araso gida, Yah sadeeq yana parking da mota musaddiq ya fito ya nufi cikin gidan d'akin shi ya shige ya cire kayan jikin shi ya shiga toilet wanka yayi sannan ya fito ya shirya cikin wata riga mara hannu red colour da ash d'in 3quater bayan ya fesa perfumes ya fito xuwa babban palon gidan, anan ya tarar da mumy da Yah sadeeq a xaune suna hira xama yayi kusa da mumy yace
" I'm hungry Mumy "
Har Yah sadeeq ya bud'e baki xai yi magana kamar musaddiq yasan abin da xai fad'a wa mumyn aikuwa yayi mishi alamar kada ya fad'a mata don hka yaja bakin shi yayi shiru kawai.
" my son me xa'a kawo maka?" Cewar mumy
D'an yatsina fuska yayi tare da cewa " Duk abin da kika dafa mumy, amman a had'a min da fura mai sanyi"
"kaje dinning table xaka samu komai acan akwai kuma fura cikin frige din kusa da dinning table, maxa tashi kaje ka ci"
Tashi yayi ya nufi 6angaren dinning table d'in yana yatsine fuska, shi kuwa Yah sadeeq yana danne dariyar da taxo mishi.
Cikin nutsuwa ya d'ebe abincin yaci Kad'an sannan ya sha furar nan da yawa, bayan ya gama sai ya dawo palon amman bai xauna ba ya kalli mumy da Yah sadeeq yace
"ni xan je na kwanta na huta "
"Okay son ae gwara ka huta " Cewar mumy yayin da Yah sadeeq yace
"ae dole ma ka huta brother saboda ka sha........... "
Kafin ya K'arasa fad'i musaddiq ya harare shi yayi gaba shi kuwa Yah sadeeq dariya ya tuntsire da ita mumy kuwa cewa take
"je ka huta son ka rabu da yayan nan naka sarkin tsokana "
"auuu hka xaki ce mumy "
Cikin murmishi mumy tace "Ehhh mana "
Nan dai suka cigaba da hirar su cikin kwanciyar hankali.
A 6angaren musaddiq kuwa ba hutawar xai yi ba kawai tunanin Wanda yasa aka kawo mishi wannan abin kaxantar yake amman duk tunanin shi ya rasa gano ko wane, amman lallai xan bincika, da hka bacci ya d'auke shi.
*WANE NE MUSADDIQ ABUBAKAR*?
Dr Musaddiq Abubakar kyakkyawan saurayi ne hadadden guy wanda ilimin addini dana boko suka ratsa shi nutsatstsan mutum ne ma'abocin miskilan ci da rashin son hayaniya, bai dad'e da kammala karatun likita ba, mahaifin shi yana gina mishi asibiti, sai dai kuma musaddiq don ra'ayin kanshi yake koyarwar amman shi cikakken likita ne.
Iyayen shi kuwa Alhj Abubakar da hajia khadija su biyu ne 'ya'yan su daga Abubakar sadeeq Wanda yaci sunan uban nashi suna ce mishi sadeeq sai kuma musaddiq ,suna xaune cikin xaman lafia da kwanciyar hankali gashi suna k'aunar junan su sosai har baxa ka iya banbance tsakanin sadeeq da musaddiq wanne yafi k'aunar d'an uwan shi ba, mahaifin shi d'an kasuwa ne hka shima sadeeq sana'ar mahaifin nashi yake.
Alhj Abubakar da Alhj El Hussaen abokanan juna ne na k'ut da k'ut,amintaka ce a tsakanin su sosai hka ma matan su.
_mun dawo labari_
Tun daga lokacin mufidah take xuwa skul da wuri idan ta fuskanci ranar musaddiq yana da lecture a ranar don hka bai k'ara korar ta ba, sai dai fah har yanxu haushin yarinyar yaji sosai, ita kuwa bata k'ara bi ta kanshi ba gashi duk test d'in da yake musu da assignment kusan ita ce kan gaba wajen ci,kuma yaga kusan lecture's din makarantar suna yaba ma yarinyar sosai.
Ana cikin hka Yah Omar yayi waya xai dawo nan da k'wana 2 don Allah mufidah ba xama ita da nabila suna kok'arin had'a mishi partyn murnar kammala makarantar shi da kuma murnar xagoyowar shekarar haihuwar shi, sosai suke shirya Inda xa'a yi partyn da a abubuwan da xa'a buk'ata a wajen.
Ranar Friday da misalin karfe 7 jirgin su Yah Omar yayi landing a airport d'in malam aminu kano, mufidah da nabila ne suka d'aukar shi yana fito wa daga cikin jirgin mufidah ta nufi inda yake da gudu ta rungume shi cikin tsananin farincikin ganin d'an uwan nata ,nan shima ya rungume ta cikin murnar ganin kanwar tashi xuwa can ta sake shi tare da kallon shi cikin murmishi tace
"Yah Omar ka ga yanda ka koma lallai london ta kar6e ka"
"lallai yarinyar nan kin rainani daman can da Kyan nawa "
Ya Omar ya fad'a cikin dariya a lokacin kuma nabila ta k'araso tana gaida shi tare da yi mishi sannu da xuwa rik'e baki yah Omar yayi tare da cewa
"kai kai wannan ba dai itace nabila ba?"