Sashe 7
Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaskiya sun yi murnan ganin ta sosai. Musamman sanda Firdausi ta shiga ɗakinta ta hange ta, ai sai ta washe baki tsaban farin ciki, bata taɓa yarda da gaske Nafi'u yake mata ba wlh, domin ta san ko kowa zai zo Arab baza ta zo ba, in fact ma Inna baza ta barta ba tunda ta fi ƙaunar Arab, baza ta so ta matsa a kusa da ita ba, bare ta san halin Arab sai abun da taga dama take yi, sai ga shi kuma ta ganta a ɗakinta. Da sauri ta nufe ta tana rungume ta tare da cewa, "Auta ke ce? Ashe za ki zo?" Sai ga hawaye sharr sun soma bin kuncinta
Ita kuma Arab kallonta kawai take yi saboda yanda ta sauya mata, ta zama wata ƙatuwar Mata, ko don tana da ciki ne oho. Sai kawai ta ɗage kafaɗa alamun hakan bai dame ta ba, dariya tayi tace, "Aunty da kuka kuma? Kai! kai! Kar kiyi abun kunya a gabar ƙanwar ki mana."
Yanda tayi maganar ne dole Firdausi tayi dariya tana kai hannunta ta ɗan buge ta, sai tace, "kin raina ni ko?"
Murmushi ita kuma tayi tace, "a'a ina girmama ki, ke ce fa babbar Yaya, ina Ni ina raina ki?"
Still dariyan Firdausi tayi sai tace, "idan na biye miki ko; za ki mayar dani mahaukaciya, ya su Inna da kowa da kowa? Ina su Ummu meyasa baku zo tare ba?"
"Hhmm ke ma kin san Inna baza ta barmu gaba ɗaya mu taho ba, da ya ya ta bar Ni nima? Sai dai sun ce suna gaishe ki sosai, su Aunty Ummu ma zasu taho ranan Asabar sai mu koma tare."
Sai Firdausin ta washe baki cikin farin ciki tace, "kai naji daɗi, Allah ya kaimu rai da lafiya, gaskiya kin faranta min da zuwan nan naki, wlh duk naji babu daɗi yanda ku ka manta dani, sai nayi tunanin ko Inna ne ta hana ku zuwa tunda ko a waya ba kwa nema na."
"Ayya ba haka bane Aunty, kin san makaranta ga kuma sana'a, so bamu da lokacin kanmu."
"Shi ne kuma har da lokacin ƴar uwanku baku dashi? Kar ki manta Ni fa ƴar uwanku ce." Tayi maganar cikin rauni har da hawaye suke son zubo mata
Sai dai sallaman Nafi'u ne ya tsayar da Arab yin magana. Ya shigo ciki bayan sun amsa mishi, hannunsa da ledoji har guda uku yace, "to Autanmu ga abinci na siyo miki tunda me yi ba lafiya, ke kuma daga baƙunta baza mu wahalar da ke ba."
Dariya tayi tace, "Ayya Yayanmu, wlh da baka siyo ba ka bar Ni inyi mana, ai ba wani abu bane don na shiga kichen."
"A'a, gwara dai ki huta tunda yanzu kika zo." Sai ya kalli Firdausi yace, "kin yi sallah ne?"
Girgiza mishi kai tayi da faɗin, "a'a."
"To tashi kiyi mana sai ki ci abincin ke ma, kin san abun da likita yace ai. Bari inje falo idan kun gama sai ku same Ni."
"To." Firdausi ta amsa mishi
Sannan ya fice a ɗakin
Kallonta Firdausi tayi tace, "buɗe ledan ki duba abun da ke ciki, bari in Yi sallah."
"Ok." Arab ta furta tana ajiye wayan da ke hannunta, sannan ta jawo ledojin ta soma dubawa. Takeaways ne a ɗaya, sai kuma fruits sannan ledan tsire. Tana ganin tsiren ta ciro ta hau ci tana kaɗa kanta
Firdausi da ta fito ta ganta a haka sai tayi dariya tace, "har yanzu kina nan da halin ki Auta, baza ki bar kwaɗayi ba."
"To me ya fi hakan daɗi? Kowa fa na son daɗi Aunty sai dai idan bai samu ba, Ni duk abun da zai sa Ni jindaɗi a rayuwata shi nake yi bazan ƙwari kaina ba."
Murmushi kawai tayi mata sai ta saka Hijab ta tayar da sallah
Lokacin wayan Arab tayi ƙara, ganin sunan Besty ɗinta sai ta ɗauka tana cewa, "Ya ne Besty?"
"Bazan amsa ba tunda kika yi tafiya ba ki sanar dani ba, na zo gida Zahra take sanar dani kina Kaduna."
Dariya tayi tace, "oh! Sorry my Besty, wlh I have not forgotten you, right now I want to call you."
Yace, "ai kin kyauta, kin san ba na fushi da ke, to ya Kadunan? Ya su Aunty Firdausin?"
"Lafiya ƙalau. Hope kaima kana lafiya?"
"Uhmm ina fa lafiya kin tafi kin bar Ni cikin maraichi, bayan kin san yau akwai alƙawari a tsakanin mu."
Dariya tayi sosai tana siɗe hannunta, sai ta sauke ledan tsiren daga jikinta ta ajiye ma Firdausi, still tana ci gaba da wayan da cewa, "i Know. Amma ka san bazan manta da kai ba, Let me be with you when I return."
"Fine. Ya na iya haka nan zan jira, but zan yi kewar ki sosai wlh, ba ki ga yanda ake tambayar ki bane yau a wajen sana'a, kowa yana tambayana ina kika je? Ni kuma sai na kira wayanki maybe network problem did not enter, after na je gidan ku ake faɗa min kin tafi KD."
Taɓe baki tayi tace, "you just delete them and I don't have time for them. Ya labari?"
Dariya yayi yace, "ok Gimbiyyar Mata, girman ki ne ai. But labari ke za ki bani, You have not spoken to Alhaji Bashir yet?"
Yatsina fuska tayi sabida kallon da Firdausi take mata. Sai ta kawar da kanta tana kwanciya a kan gadon tare da cewa, "I spoke to him on WhatsApp, but I have not been able to go online again."
"Haba Besty kina wasa da Mutumin nan ko? Zuwa yanzu yakamata ace har kun gama fahimtar juna, na san ki ba kya wasa da irin Alhazawan nan, amma da alamu har yanzu ba ki san ko shi waye bane."
Murmushi tayi me sauti sai tace, "ka bari zamu yi maganar daga baya, yanzu ga Tariq nan yana kira na zan amsa call."
"Ok when you're done I'll call you."
Daga haka suka yi sallama ya kashe wayan
"Kar ki ɗauki wayan nan please ki bari ki gama." Firdausi tayi maganar tana kallonta
Itama sai ta ɗago tana kallonta. Sai kuma ta ɗage kafaɗa before tace, "ok." Ajiye wayan tayi ta sauko ƙasan inda Firdausi ke zaune tana cin abinci. Itama ta buɗe ɗaya takeaway ɗin ta sanya Robber spoon ɗin tana ci
Sai da Firdausi ta ɗago ta kalle ta sannan ta kawar da kanta tana girgiza shi, ko kaɗan halayen ƙanninta ba sa mata daɗi, tana shiga ƙunci da baƙin ciki duk sanda ta tuna yanda suke rayuwarsu kuma bata da halin hana su, musamman ma Arab wacce take tsananin tausaya mata kasancewarta ƙaramar yarinya amma ta fi su hatsabibanci, ba ta jin magana ko kaɗan, yanzu tana buɗe baki don tayi mata nasiha zata iya jawowa kanta, sai ma tace mata, "zata koma gida tunda ita ba wa'azi ta zo tayi mata ba." Shiyasa tayi shiru ta ƙyale ta. Bayan ta gama cin abincin sai ta miƙe da gudan takeaway ɗin, sai drinks guda biyu tace, "idan kin gama muna falo, bari in kaiwa Nafi'u abincin shima ya ci."
"Ok." Tace mata kawai tana ci gaba da cin abincinta. Bayan fitan ta ne ta ɗauki wayan taga Tariq yayi mata three missed calls. Sai bata bi kiran ba ta miƙe ta shiga toilet. Bakinta ta kuskure sannan ta fito ta ɗauki wayanta zata fice sai kuma kiran Tariq ɗin ya sake shigowa. Zama tayi a bakin gadon tana amsa call ɗin. Sallama yayi mata ta amsa
"Baby ina kika shige ne ina ta kiran wayan ki but ba ki yi peacking ba?"
Ɗan muskuta zamanta tayi tana kwanciya sosai a kan gadon. A hankali cikin yanga tace, "ina cin abinci ne."
"Oh. Har kin sa na ji sanyi a raina, nayi tunanin laifi nayi ko kuma babu lafiya. Yau ban ganki a wajen suyan wara ba? Allah yasa lafiya?"
"Ƙalau. I just Traveling."
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!." Ya furta cikin wani irin yanayi da ya faɗarwa da Arab da gaba
Da sauri ta furta, "lafiya dai?"
Sai da ya ɗan ja numfashi before yace, "ina fa lafiya, shikenan Baby bazan samu ganin ki ba kin yi tafiya?"
"Wai saboda haka ne kake jan wannan salatin?"
"Eh mana. Ai babu abun da zai ɗaga min hankali a yanzu sama da rashin ki a tare da Ni, wlh ba ki san yanda na kwana da tunaninki bane jiya, na ƙosa yau tayi in zo in ga kyakykyawar fuskarki but sai ga shi na rasa ki, kuma kina faɗa min kin yi tafiya, yanzu shikenan sai yaushe zan ganki?"
Murmushinta me kyau tayi kafin tace, "kana da abin dariya gaskiya, but I will be back soon, only four days."
"Ki ce zan mutu kafin lokacin nan, Please kar kiyi min wannan horon na rashin ganinki, zan iya mutuwa ba ki san yanda na kamu da soyayyar ki ba ko? Please Aisha help me to give me a chance to show you how much I love you, ki bani dama don Allah in aure ki wlh I really love you."
"Meyasa kake min maganar aure yanzu daga haɗuwar mu jiya? Ko nace maka zan yi aure yanzu ne?"
"A'a, amma Baby ki fahimce Ni, ƙaunar da nake miki ne bazan iya jure tsawon lokaci ba na tare da ke ba, zan so ace Ni na mallake ki a matsayin Mata..."
Katse shi tayi da faɗin, "kaga Malam Ni babu aure a gabana a yanzu, a tunaninka daga haɗuwar mu sai kawai in ba ka damar da zaka iya aure na? Duka-duka nawa nake da zan yi aure yanzu? Don haka ka dena min maganar aure yanzu sabida babu shi a raina kuma ban shirya yi yanzu ba, now ina gaɓar yarintana ban shirya tsufa da wuri ba, and sannan ba na son takura gaskiya idan ka san wannan maganar zaka riƙa min kar ka sake kira na." Sai ta ja tsaki ta kashe kiran. Ai kuwa ko ajiye wayan bata yi ba ya sake kira, kamar baza ta ɗauka ba sai kuma ta ɗaga
Ita kuma Arab kallonta kawai take yi saboda yanda ta sauya mata, ta zama wata ƙatuwar Mata, ko don tana da ciki ne oho. Sai kawai ta ɗage kafaɗa alamun hakan bai dame ta ba, dariya tayi tace, "Aunty da kuka kuma? Kai! kai! Kar kiyi abun kunya a gabar ƙanwar ki mana."
Yanda tayi maganar ne dole Firdausi tayi dariya tana kai hannunta ta ɗan buge ta, sai tace, "kin raina ni ko?"
Murmushi ita kuma tayi tace, "a'a ina girmama ki, ke ce fa babbar Yaya, ina Ni ina raina ki?"
Still dariyan Firdausi tayi sai tace, "idan na biye miki ko; za ki mayar dani mahaukaciya, ya su Inna da kowa da kowa? Ina su Ummu meyasa baku zo tare ba?"
"Hhmm ke ma kin san Inna baza ta barmu gaba ɗaya mu taho ba, da ya ya ta bar Ni nima? Sai dai sun ce suna gaishe ki sosai, su Aunty Ummu ma zasu taho ranan Asabar sai mu koma tare."
Sai Firdausin ta washe baki cikin farin ciki tace, "kai naji daɗi, Allah ya kaimu rai da lafiya, gaskiya kin faranta min da zuwan nan naki, wlh duk naji babu daɗi yanda ku ka manta dani, sai nayi tunanin ko Inna ne ta hana ku zuwa tunda ko a waya ba kwa nema na."
"Ayya ba haka bane Aunty, kin san makaranta ga kuma sana'a, so bamu da lokacin kanmu."
"Shi ne kuma har da lokacin ƴar uwanku baku dashi? Kar ki manta Ni fa ƴar uwanku ce." Tayi maganar cikin rauni har da hawaye suke son zubo mata
Sai dai sallaman Nafi'u ne ya tsayar da Arab yin magana. Ya shigo ciki bayan sun amsa mishi, hannunsa da ledoji har guda uku yace, "to Autanmu ga abinci na siyo miki tunda me yi ba lafiya, ke kuma daga baƙunta baza mu wahalar da ke ba."
Dariya tayi tace, "Ayya Yayanmu, wlh da baka siyo ba ka bar Ni inyi mana, ai ba wani abu bane don na shiga kichen."
"A'a, gwara dai ki huta tunda yanzu kika zo." Sai ya kalli Firdausi yace, "kin yi sallah ne?"
Girgiza mishi kai tayi da faɗin, "a'a."
"To tashi kiyi mana sai ki ci abincin ke ma, kin san abun da likita yace ai. Bari inje falo idan kun gama sai ku same Ni."
"To." Firdausi ta amsa mishi
Sannan ya fice a ɗakin
Kallonta Firdausi tayi tace, "buɗe ledan ki duba abun da ke ciki, bari in Yi sallah."
"Ok." Arab ta furta tana ajiye wayan da ke hannunta, sannan ta jawo ledojin ta soma dubawa. Takeaways ne a ɗaya, sai kuma fruits sannan ledan tsire. Tana ganin tsiren ta ciro ta hau ci tana kaɗa kanta
Firdausi da ta fito ta ganta a haka sai tayi dariya tace, "har yanzu kina nan da halin ki Auta, baza ki bar kwaɗayi ba."
"To me ya fi hakan daɗi? Kowa fa na son daɗi Aunty sai dai idan bai samu ba, Ni duk abun da zai sa Ni jindaɗi a rayuwata shi nake yi bazan ƙwari kaina ba."
Murmushi kawai tayi mata sai ta saka Hijab ta tayar da sallah
Lokacin wayan Arab tayi ƙara, ganin sunan Besty ɗinta sai ta ɗauka tana cewa, "Ya ne Besty?"
"Bazan amsa ba tunda kika yi tafiya ba ki sanar dani ba, na zo gida Zahra take sanar dani kina Kaduna."
Dariya tayi tace, "oh! Sorry my Besty, wlh I have not forgotten you, right now I want to call you."
Yace, "ai kin kyauta, kin san ba na fushi da ke, to ya Kadunan? Ya su Aunty Firdausin?"
"Lafiya ƙalau. Hope kaima kana lafiya?"
"Uhmm ina fa lafiya kin tafi kin bar Ni cikin maraichi, bayan kin san yau akwai alƙawari a tsakanin mu."
Dariya tayi sosai tana siɗe hannunta, sai ta sauke ledan tsiren daga jikinta ta ajiye ma Firdausi, still tana ci gaba da wayan da cewa, "i Know. Amma ka san bazan manta da kai ba, Let me be with you when I return."
"Fine. Ya na iya haka nan zan jira, but zan yi kewar ki sosai wlh, ba ki ga yanda ake tambayar ki bane yau a wajen sana'a, kowa yana tambayana ina kika je? Ni kuma sai na kira wayanki maybe network problem did not enter, after na je gidan ku ake faɗa min kin tafi KD."
Taɓe baki tayi tace, "you just delete them and I don't have time for them. Ya labari?"
Dariya yayi yace, "ok Gimbiyyar Mata, girman ki ne ai. But labari ke za ki bani, You have not spoken to Alhaji Bashir yet?"
Yatsina fuska tayi sabida kallon da Firdausi take mata. Sai ta kawar da kanta tana kwanciya a kan gadon tare da cewa, "I spoke to him on WhatsApp, but I have not been able to go online again."
"Haba Besty kina wasa da Mutumin nan ko? Zuwa yanzu yakamata ace har kun gama fahimtar juna, na san ki ba kya wasa da irin Alhazawan nan, amma da alamu har yanzu ba ki san ko shi waye bane."
Murmushi tayi me sauti sai tace, "ka bari zamu yi maganar daga baya, yanzu ga Tariq nan yana kira na zan amsa call."
"Ok when you're done I'll call you."
Daga haka suka yi sallama ya kashe wayan
"Kar ki ɗauki wayan nan please ki bari ki gama." Firdausi tayi maganar tana kallonta
Itama sai ta ɗago tana kallonta. Sai kuma ta ɗage kafaɗa before tace, "ok." Ajiye wayan tayi ta sauko ƙasan inda Firdausi ke zaune tana cin abinci. Itama ta buɗe ɗaya takeaway ɗin ta sanya Robber spoon ɗin tana ci
Sai da Firdausi ta ɗago ta kalle ta sannan ta kawar da kanta tana girgiza shi, ko kaɗan halayen ƙanninta ba sa mata daɗi, tana shiga ƙunci da baƙin ciki duk sanda ta tuna yanda suke rayuwarsu kuma bata da halin hana su, musamman ma Arab wacce take tsananin tausaya mata kasancewarta ƙaramar yarinya amma ta fi su hatsabibanci, ba ta jin magana ko kaɗan, yanzu tana buɗe baki don tayi mata nasiha zata iya jawowa kanta, sai ma tace mata, "zata koma gida tunda ita ba wa'azi ta zo tayi mata ba." Shiyasa tayi shiru ta ƙyale ta. Bayan ta gama cin abincin sai ta miƙe da gudan takeaway ɗin, sai drinks guda biyu tace, "idan kin gama muna falo, bari in kaiwa Nafi'u abincin shima ya ci."
"Ok." Tace mata kawai tana ci gaba da cin abincinta. Bayan fitan ta ne ta ɗauki wayan taga Tariq yayi mata three missed calls. Sai bata bi kiran ba ta miƙe ta shiga toilet. Bakinta ta kuskure sannan ta fito ta ɗauki wayanta zata fice sai kuma kiran Tariq ɗin ya sake shigowa. Zama tayi a bakin gadon tana amsa call ɗin. Sallama yayi mata ta amsa
"Baby ina kika shige ne ina ta kiran wayan ki but ba ki yi peacking ba?"
Ɗan muskuta zamanta tayi tana kwanciya sosai a kan gadon. A hankali cikin yanga tace, "ina cin abinci ne."
"Oh. Har kin sa na ji sanyi a raina, nayi tunanin laifi nayi ko kuma babu lafiya. Yau ban ganki a wajen suyan wara ba? Allah yasa lafiya?"
"Ƙalau. I just Traveling."
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!." Ya furta cikin wani irin yanayi da ya faɗarwa da Arab da gaba
Da sauri ta furta, "lafiya dai?"
Sai da ya ɗan ja numfashi before yace, "ina fa lafiya, shikenan Baby bazan samu ganin ki ba kin yi tafiya?"
"Wai saboda haka ne kake jan wannan salatin?"
"Eh mana. Ai babu abun da zai ɗaga min hankali a yanzu sama da rashin ki a tare da Ni, wlh ba ki san yanda na kwana da tunaninki bane jiya, na ƙosa yau tayi in zo in ga kyakykyawar fuskarki but sai ga shi na rasa ki, kuma kina faɗa min kin yi tafiya, yanzu shikenan sai yaushe zan ganki?"
Murmushinta me kyau tayi kafin tace, "kana da abin dariya gaskiya, but I will be back soon, only four days."
"Ki ce zan mutu kafin lokacin nan, Please kar kiyi min wannan horon na rashin ganinki, zan iya mutuwa ba ki san yanda na kamu da soyayyar ki ba ko? Please Aisha help me to give me a chance to show you how much I love you, ki bani dama don Allah in aure ki wlh I really love you."
"Meyasa kake min maganar aure yanzu daga haɗuwar mu jiya? Ko nace maka zan yi aure yanzu ne?"
"A'a, amma Baby ki fahimce Ni, ƙaunar da nake miki ne bazan iya jure tsawon lokaci ba na tare da ke ba, zan so ace Ni na mallake ki a matsayin Mata..."
Katse shi tayi da faɗin, "kaga Malam Ni babu aure a gabana a yanzu, a tunaninka daga haɗuwar mu sai kawai in ba ka damar da zaka iya aure na? Duka-duka nawa nake da zan yi aure yanzu? Don haka ka dena min maganar aure yanzu sabida babu shi a raina kuma ban shirya yi yanzu ba, now ina gaɓar yarintana ban shirya tsufa da wuri ba, and sannan ba na son takura gaskiya idan ka san wannan maganar zaka riƙa min kar ka sake kira na." Sai ta ja tsaki ta kashe kiran. Ai kuwa ko ajiye wayan bata yi ba ya sake kira, kamar baza ta ɗauka ba sai kuma ta ɗaga