← Book details Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 52

Sashe 16

Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Morning Nawwara, har kin fito? Ga shi mutumin naki har yanzu shiru nake ji ya ƙi fitowa."

Ikhlas tace, "ai yanzu Mummy za ki ganshi, naga ya shiga part ɗin Abba but maybe ya fito." Sai kuma ta kalli Nawwara tana cewa, "Aunty kin Yi kyau wlh, sosai da sosai."

Baki Nawwara ta washe tare da cewa, "thank you sister, Ina Zainab?"

"Tana school, yanzu ta fita."

"Ok Mummy bari in je in duba shi ko ya shirya." Nawwaran tafaɗa tana miƙewa

Mummy tace, "to, but tell him don't waste time please, you should go now, gwara ku tafi da wuri zai fi ai.. Ikhlas tashi ki je ɗaki na ki ɗauko min baƙin ledan nan dana ɗaura a kan gado, ki riƙo da kyau fa kar kiyi min ɓanna."

Miƙewa tayi da sauri tana cewa, "kai Mummy sai kace wata yarinya?" Sai ta ruga a guje kuma ta hau steps ɗin benen

While Mummy na cewa, "ai na san halin ki ne tunda ba kya abu da hankali".

                   *****

         Nawwara kuwa tana shiga ɗakin Malik ta hange shi zaune a gaban gadon shi yana ƙoƙarin saka shoes ɗin sa

Shima ɗago kai yayi ya zuba mata idanuwansa masu shegen haske da ɗaukar hankali, sai ya sakar mata murmushi kawai yana bin ta da kallo tare da ƙarewa shiganta kallo

Doguwar riga ce a jikinta kalan ruwan hanta, me gajeren hannu da igiyoyi, rigan ta lafe mata daga sama har ƙasa babu wani shafe sai na jikinta, ƙam ta kama ta, stones ne kawai aka yi kwalliya dashi a gaban rigan while ta ɗaura farin gyale a saman attachment ɗin kanta; yayinda ya rufe mata har zuwa kafaɗun ta, kasancewarta fara rigan tayi mata matuƙar kyawu musamman yanda ta sha makeup a fuska, sai sheƙi fuskar nata take yi tana glowing, sai tayi using da farin hill shoes tare da Hangbag ɗinta me ɗaukar hankali

While shima Malik farin yadi ya saka wanda aka yi mishi ɗinki dai-dai da jikinsa na zamani, yayi masa kyau matuƙa ya fito da ainihin kyawu da kamalansa, kyakykyawar fuskarsa yana zagaye da ƙasumba da dogon gemu da ya ƙara ƙawata face ɗin nasa, duk wata Mace idan ta kalle sa dole ta sake kallonsa sabida haɗuwar sa, kana kallon sa zaka hangi irin tsantsan tsaftar shi da gayun shi, shiyasa Mata suke mishi rubuti sabida ya iya wanka matuƙa Malik, duk inda namiji ya kai Malik ya kai, ga iya soyayya da ba wa Mata muhimmanci, shi dai a rayuwa yana bala'in ƙaunar Mata, ko ya ya suke yana matuƙar girmama su kuma yana jin daɗin mu'amala da su, shiyasa ba ya rabo da su a koda yaushe

Nawwara tahowa wajensa tayi tana murmusawa tare da cewa, "Wow! My prince charming you look very well, honestly can choose."

Hannu ya miƙa mata yana kama nata tare da cewa, "ai ban kai ki ba, anya zan iya tafiya da ke? Kar azo a samu matsala kuma wani yayi min ƙwace." Ya ƙare maganar yana ɗaura ta a saman cinyan sa, tare da kai fuskarsa kan nata yana shinshina ta cike da tsantsan shauƙi

While itama haka, sai dai murmushi ne a kan fuskarta, inda ta sauke mishi hot kiss before ta janye bakinta tana cewa, "babu wanda ya isa ya ƙwace maka Ni, Ni an yi ni ne saboda kai kaɗai, I'm yours, don haka ka dena saka wani abu a ranka, idan ba kai ba sai rijiya, rijiyan ma mai kwalabe." Ta sake kai bakinta ta lashe saman laɓɓansa

Shi kuma sai ya ɗaura hannunsa a ƙeyanta ya haɗe bakunansu waje ɗaya, tsawon lokaci suna kissing junan su before su janye wanda har sun soma fita cikin hayyacin su. Hakan bai ishe su ba sai da suka sake romance din juna sannan suka haƙura ganin suna shirin manta a inda suke da kuma abun da zasu yi

Ita ta ƙarisa saka mishi takalmin sannan suka fito tare da ɗan ƙaramin Jakar sa kasancewar kwana zasu yi

Mummy da Ikhlas har yanzu suna zaune a Falon, inda Ikhlas har ta kawo mata saƙon da ta aike ta

Mummy tuni ta soma koɗa su don ba ƙaramin ƙaunar Nawwara take yi a ranta ba, tana matuƙar sonta da ɗanta saboda wayewanta da ƙaunar ɗanta da take yi, shiyasa take ganin kamar duk duniya ɗanta ya fi dacen Mace ta gari idan ya auri Nawwara

Nawwara ɗiya ce wajen ƙanwar Abban su Malik. Gidan su a farkon anguwa ne duk da akwai nisa da gidan su Malik, but komai na rayuwar Nawwara a gidan su Malik take yin sa tun tana ƙarama, babu wanda bai san soyayyar su a family ba har dangin Mummy da suke Kano, kasancewar ita Mummy ɗiya CE wajen Sarkin Kano, ita ce ƴa ta biyu a yaranshi da ya mallaka, tana aure a nan Abuja tare da mijinta Alhaji Atiku Nera, shahararren ɗan kasuwa da yayi suna a faɗin Nigeria da kewayen ta, babu abun da bai mallaka ba sabida tsaban kuɗin sa, yaran sa uku Allah ya ba shi, Abdul Malik sai Zainab sannan sai Ikhlas mai sunan Mahaifiyar shi da ta rasu, Habiba

Alh. Atiku su biyu ne iyayen su suka haifa, daga shi sai Mahaifiyar Nawwara. Itama a Abuja take Aure kuma abokin Alhaji Atiku ta aura. Nawwara kaɗai suka haifa ita kenan musu, suna sonta kamar ransu domin ba sa son abun da zai ɓata mata rai, shiyasa ta tashi cikin sangarta tunda ƴar gata ce gaba da baya, duk abun da take so shi take yi. Allah ya ɗaura mata ƙaunar Malik tun tana yarinya bata san meye rayuwa ba, shiyasa ya soma koya mata duk wani rayuwar wayewa da tanbaɗewa, kuma shi ya soma sanin ta a ɗiya Mace bayan yayi mata wayau ya amshe mata budurcin ta tare da yin mata alƙawaruka kala-kala, shiyasa take ganin babu wata Mace da ta isa ta mallake shi face ita, ita kaɗan ta, shi nata ne domin an yi shi ne don ita, tana da tsananin kishi zata iya komai domin shi

Don haka shi kansa yana taka-tsan-tsan saboda shegen kishin ta, but hakan bai hana shi yin mu'amala da mata kala-kala ba duk da ya san halin ta, sai dai har a zuciyarsa bai taɓa son wata ɗiya Mace ba bayan Nawwara. Amma yanzu kuma ƙaddara tana neman canza mishi akala, duk da a baya yayi mata alƙawarin ita kaɗai ce matar shi a duniya, to bai taɓa tunanin zai iya cin karo da wata wacce zuciyar shi zata faɗa da kogin ƙaunar ta a nan take ba, sai dai abun haushin ma bai san inda zai ganta ba, a kullum da hoton ta yake kwana yake tashi, shi kaɗai yake gani ya ji daɗi a ransa, soyayyarta ta shiga cikin jikinsa ta zame mishi jini da hanta, abun da yake ji a kanta bai taɓa jin makamanciyar irin sa a kan kowacce Mace ba har Nawwara da yake tunanin yana matuƙar ƙauna, sai dai kuma bai san ya wannan soyayyar tashi zata kasance ba domin yana ganin makauniyar soyayya ce wacce zata iya kai shi ga halaka, bai san ya zai yi ba duk da yana fatan ace wata rana ya haɗu da yarinyar, koda hakan zai zama silan mutuwar shi ce sai ya mallake ta, dole ne ya mallake ta, sai dai idan Nawwara zata haƙura amma dole ne ayi ɗayan biyu, ko ya aure su duka biyun ko kuma ita kaɗai, amma babu fashi bazai taɓa iya cire soyayyar ta ba, kuma ko nawa ne zai iya kashewa don samun ta a cikin rayuwar shi, amma taya ya hakan zai faru? Abun da kamar wahala domin bai san ta inda zai soma ba, aina zai ganta bare har ya bayyana mata irin soyayyarta da ya kamu da ita? Tabbas idan aka ci gaba da tafiya da yiwuwar ya rasa tunanin sa gaba ɗaya saboda bege da tsananin shauƙin haukan soyayyarta.

                 *******

             Har suka gama sallama da su Mummy suka rako su haraban gidan, gaba ɗayansu har Abba da shima ya fito daga part ɗinsa. Sannan suka hau Mota suka tasarwa hanya ɗoɗar

Duk da Malik ba ya cikin walwala sakamakon damuwa da tunanin yarinyar da take ƙarƙashin ransa, amma haka ya biyewa Nawwara da ke mishi hira, suna zantawa sama-sama yayinda yake kwasa gudu a titi. Wayan sa ne tayi ƙara sai ya ciro ta daga aljihu yana dubawa, ganin sunan wani friend ɗinsa sai ya ɗauka yana karawa a kunne. A haka suka ɗauki lokaci suna waya before ya kashe yana kallon Nawwara tare da kashe mata ido ɗaya yace, "ƴan Matana zamu wuce Zaria kafin mu je Kano, akwai Aboki na da zamu haɗu a can, yace min yana Zaria so ina son mu haɗu tunda muna kan hanya. I want to say hello because we haven't met in a long time."

Murmushi tayi tace, "babu komai my Prince, ka san yau ina matuƙar farin ciki sabida kasancewar mu tare, so duk inda zamu je bazan gajiya ba Ni dai fatana mu kasance tare, ba don kar su Mummy su kira waya ace musu bamu ƙarisa ba da yau kawai mun hutawar mu a wani hotel, hakan zai faranta min rai sosai."

Hannu ɗaya yasa ya kamo nata yana mata murmushi da cewa, "nima haka nayi tunani, but ki bari zamu samu time zamu kasance tare har sai mun gaji, duk sanda zamu dawo gida zamu yi yawon mu before mu koma."

"Yauwa my prince, haka nake son ji, Allah ya barmu tare." Ta furta tana kai mishi kiss a kuncin sa

Dariya yayi yace, "ki bari fa kinga tuƙi nake yi kar ki ja min matsala."

Narke fuska tayi da cewa, "uhm kai ne ka san ba na gajiya da kai, ban ƙi ba mu dauwama manne da juna a koyaushe, ina matuƙar ƙaunar ka Malik, na mallaka maka komai nawa sai yanda kayi dani."

Murmushi yayi yana sake tamke hannunta a cikin nasa, tare da sakar mata kyakykyawar kallo mai tsananin shauƙi da shiga jiki, a hankali cikin raɗa-raɗa da jan hankali irin nasa yace, "na san da haka Princess ɗina, nima ina tsananin ƙaunar ki, but baza ki gane hakan ba sai a nan gaba."
Chapter 16 · 0% Book details