Sashe 5
Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yayinda su Inna suna zaune a tsakar gidan a gindin bishiyar Mangwaro da ke dirke a tsakiyar gidan suna shan iska, kasancewar garin akwai zafi sosai. Daga ita har su Ummu suke zaune suna cin abinci a cikin faranti ɗaya, tunda haka suke yi a koyaushe, Inna Harira Mace ce mai tsananin ƙaunar yaranta, akwai sabo mai ƙarfi a tsakanin su, ta ɗauke su tamkar ƙawayenta ne, a rayuwa babu abin da take ɓoye musu nata haka su ma, suna rayuwar su ne cikin ƙaunar juna da tsantsan shaƙuwa a tsakanin su, tun farko haka ta sabar musu cin abinci tare a kwano ɗaya, sai dai idan ɗaya ba ta nan ne ko tayi dogon zango shine zasu ci babu ita, ko kuma su jira ta idan ta dawo su ci tare, amma duk runtsi dole sai kaga cikin su wasu sun ci tare, shiyasa shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakanin su, su kansu yaran suna ƙaunar junan su matuƙa, kuma basu yarda wasu sun shigo rayuwar su ba, kaf ɗinsu babu mai ƙawa sai junan su, su ne ƙawayen juna su kashe tare su binne tare, shiyasa duk da babu tarbiyya a tare dasu amma suna rayuwar farin ciki a gidan su, basu damu da surutun mutane a kan rayuwar su ba, a ganinsu rayuwar su ne babu wanda ya isa ya hana su tafiyar da ita yanda suke buƙata, duk wanda yace zai taka su sai inda ƙarfin su ya ƙare, kaf ɗinsu basu da haƙuri suna rayuwarsu tamkar ƴan tasha, musamman Arab wacce duk ta fi su sheɗananta, ita abun kunya gaba ta ba shi ba baya ba, ba ta shakkan kowa sannan babu wanda zai mata a duniyar nan bata mayar mishi ba, komin tsufan shi komin girman shi, wannan sun sha a nonon uwar su ne. Domin idan wani ya taɓawa Inna Harira yara abu me sauƙi ne ta bi Mutum har gida ta ci mishi mutunci ta uwa ta uba, kowa ya sansu a kaf anguwan su har da maƙota, ba a taɓa su su ƙyale, an sha yin dambe da Inna a kan yaranta, bata da mutunci ko kaɗan a kan ka taɓa mata Yara, musamman zata saka wandon dambe ta bi ka har gida ku caku. Shiyasa yanzu da yaran nata suka girma wani lokacin tare suke zuwa ayi ta dambe ana faɗa a anguwa, in dai aka tayar da husuma a anguwan nan to kowa ya san ƴan gidan Malam Iro mai kifi ne, su ne ba sa barin anguwan ta zauna lafiya, an sha kaisu police station a kan husuma, su yanzu har sun saba da kowacce fitina ba sa tsoron ko wanne shege, bare yanda kaf ɗinsu Yaran suna da samari a station ɗin, ana kaisu za'a sako su, wani lokacin ma ƴan sandan ba sa jirgawa ko nan da can da su, a wajen zasu kashe maganar, shiyasa ma ƴan anguwan suke musu kirari da gidan Fitina. Wannan kaɗan kenan daga rayuwar iyalan Malam Iro.
Kai tsaye wajen su ta nufa tana cewa, "Inna wai Baba yace a aika mishi da abincin sa waje."
"Ga yi can a ƙofar ɗakina ki ɗauka ki kai mishi."
Gyalenta ta cire ta jefa a saman tabarman da suke kai, sannan ta nufi coolarn abincin Baban nasu ta ɗauka ta fita da gudu ta kai mishi. Tana shigowa nepa suka ɗauke wuta, dogon tsaki ta ja tana cewa, "ka ga ƴan iskan mutanen nan, daga shigowa kuma sai ɗauke wuta? Ga shi ina son saka caji."
"Haka suke yi matsiyata, yanzu suka gama wasa dashi, ga shi kuma sun ɗauke, idan ba wasa ba kuma sai tsakar dare su dasu kawo wutan nan." Cewar Ummu bayan ta haɗiye abincin bakin ta
Inna kuma tace, "Auta kunna mana Gen ɗin kafin ki zauna, Allah yasa ma muna da ishashshen mai a ciki."
Wucewa tayi ta kunna sannan ta wuce ta wanke hannu ta zo ta zauna, ta saka hannu a abincin tana cewa, "wai Aunty Zahra aina kika samu wannan guy ɗin ne?"
Zahra kallonta tayi tace, "wai Salisu? Ba ki sanni dashi bane? Shi ne fa wanda nace miki mun haɗu a bikin gidan Jamila ƴar gidan sanata da muka je mata, Ni ban ma san waye ya nuna mishi gidan mu ba, muna dai waya dashi kusan kwana biyu, sai yau kuma na ganshi ya zo."
"To shi ɗan gidan waye ne? Ba ki bani labari ba Mamana?" Inji Inna tana washe baki
Dariya suka yi gaba ɗayansu
Yayinda Zahra take basu labarin Salisu da aikin da yake yi
Itama Arab kuɗin da Tariq ya bata ta ciro ta miƙa wa Inna duka tana cewa, "nima kamun wani nayi wlh, duk da ban san ɗan waye ba amma da alamu yana da fararen." Ta ƙare maganar tana dariya cike da farin ciki
Haka su ma suna taya ta
Inda Inna tace, "ai na san ki Autana babu wasa a lamarin ki, sai dai idan ba ki fita ba, Allah yayi muku albarka baki ɗaya, haƙiƙa na haifi yara masu farin jini, hakan a jini na yake wlh, Ni na san da haka, duk wani me baƙin ciki sai dai ya mutu, ga shi yara mata suna share min hawaye."
Dukkan su murmushi suke yi suna sauraron Innar tasu. Da haka suke ta hira abin su
Yayinda Arab ta tashi ita ta nufi bayi, bata jima ba ta fito ta ɗaura alwala ta wuce ɗakinsu ta rama sallan da ake bin ta na magriba da isha'i. Sai ta zauna a ɗakin tana waya da Ibrahim
A nan yake sake bata labarin Mutumin da ya samo mata, da komai nashi sai da ya faɗa mata, sannan yace, "ta kira shi su soma magana yanzu."
Tace, "a'a sai zuwa gobe."
Dariya yayi yace, "ai girman ki ne Besty na, ina jin daɗin jan ajin nan naki, gaskiya ke ta daban ce a cikin mata, har yanzu ban ga kamar ki ba, kina lokaci ƴan mata na, kin fi ƙarfin Yaro sai dai baban Yaro."
Itama dariyan tayi tana cewa, "Besty kana fasa min kai da yawa."
"Ai matsayin ki ne My Besty, ke ɗin ce ban san yanda zan kwatanta ki ba, amma wlh kin kere duk wata Mace da na sani a rayuwata, Allah ya barmu tare."
"Amin." Tayi maganar tana dariya, "shiyasa nake ƙara sonka Besty na."
"Nima haka Besty, i love You wujiga-wujiga, ba don kin fi ƙarfi na ba da tuni nayi wuff da ke."
Dariya take yi sosai
"Allah kuwa My Besty, yanzu meye tukuici na?"
"Oh Besty! Ba ka yin abu don Allah fa na lura?"
Kashe murya yayi tare da cewa, "haba dai, Ni na isa? Ai duk abun da zan miki don Allah ne, kin san Ni na sanki, Ni da ke ba ta ɓaci, Allah ne ya haɗa jinin mu, abun da kike so shi nake so, haka kuma abun da kike ƙi shi nake ƙi, ke ma kin sani ai.. kawai dai kwaɗayin nawa ne ya tashi wlh."
"Uhmm shikenan. Let's meet tomorrow."
"Ok. But ba ki bani labarin Mutumin da kuka haɗu ɗazu ba?"
"Ai yanzu zan faɗa maka ka san ba na ɓoye maka komai." Daga nan ta ba shi labarin yanda suka yi. Basu jima suna wayan ba ta katse sabida ganin baƙuwar number tana kiran ta. Bayan ta ɗauka sallaman Tariq ya doki kunnen ta, rage murya tayi tana kwanciya a kan gadonta, yayinda ta juya baya ganin Ummu da Zahra sun shigo ɗakin. Haka tayi ta wayanta baza ka taɓa cewa waya take yi ba. Sun raba dare suna tare da Tariq before su yi sallama ta kwanta
A time ɗin su Ummu su ma har sun yi barci.
Zuwa washe gari kuma suka ta fi makaranta. Dayake ita Arab text suke yi a school, saura two weeks su fara Exams, daga nan kuma sai su shiga S.S 3. Ƙarfe sha biyu ta dawo gida
A lokacin Baba yana gida domin dawowar shi kenan daga wajen suyan kifin sa; yake sanar da Inna halin da Firdausi take ciki. Mijinta Nafi'u ya kira shi yace mishi, "bata da lafiya, yanzu haka suna asibiti an kwantar da ita, duk da dai yace jikin da sauƙi yanzu."
"To Allah ya sauwaƙe." Cewar Inna tana wucewa cikin kichen tare da cewa, "Auta har kin dawo?"
"Eh Inna." Ta furta itama tana shigowa tare da zama a kan kujeran zuƙuno, sai kuma ta kalli Babansu tace, "sannu Baba."
"Yauwa Aisha Humaira. An dawo?"
Fitowar Inna tana kallonta tace, "wai ba karatun ne kika dawo da wuri?"
"Akwai mana, muna yin text ne kuma ba wani abu ake yi ba shiyasa na dawo."
Baba ya kalli Innan yana cewa, "yanzu babu wanda zai je a cikin ku ne? Ai ya kamata ko ɗaya daga cikin yaran ne ya je ya zauna da ita, itama zata ji daɗi idan ta ga ƴan uwa, Mijin yace min idan da hali wata ta zo ta zauna da ita tunda kullum damuwar ta yaran nan ne, ta ce a tura mata ɗaya a ciki."
Mitsitstsike baki Inna tayi da cewa, "a tura wa? Ai babu inda zasu je tunda kowacce ba zaman banza take yi ba, in ba iya shege ba ai ta san babu wanda zai je yayi mata bauta tunda ta san suna makaranta, kuma sana'ar nawa ubanta zai yi min?"
Shiru Baba yayi be iya cewa komai ba illa kallonta da yake yi, sai kuma ya girgiza kanshi sabida takaicin Inna
Arab tace, "Inna ni zan je domin dama ina son zuwa, yakamata ace ko sau ɗaya ne mun je amma har yanzu bamu ƙara zuwa gidanta ba tun auren."
"To makarantar naki fa Auta? A'a babu inda za ki je."
"Allah Inna zan je, ai Ni nace miki ina son zuwa, kuma makaranta bani da matsala da hakan tunda Exams ya rage kuma ba yanzu zamu yi ba, har zan je in dawo, zan mata kwana biyu sai in dawo."
Baba washe baki yayi yace, "yauwa A'isha, ai zata ji daɗi idan ta ganku, to yaushe za ki tafi in ba ki kuɗin mota?"
"Ka bar shi kawai Baba ina da kuɗi, idan rana tayi sanyi sai in wuce."
Kai tsaye wajen su ta nufa tana cewa, "Inna wai Baba yace a aika mishi da abincin sa waje."
"Ga yi can a ƙofar ɗakina ki ɗauka ki kai mishi."
Gyalenta ta cire ta jefa a saman tabarman da suke kai, sannan ta nufi coolarn abincin Baban nasu ta ɗauka ta fita da gudu ta kai mishi. Tana shigowa nepa suka ɗauke wuta, dogon tsaki ta ja tana cewa, "ka ga ƴan iskan mutanen nan, daga shigowa kuma sai ɗauke wuta? Ga shi ina son saka caji."
"Haka suke yi matsiyata, yanzu suka gama wasa dashi, ga shi kuma sun ɗauke, idan ba wasa ba kuma sai tsakar dare su dasu kawo wutan nan." Cewar Ummu bayan ta haɗiye abincin bakin ta
Inna kuma tace, "Auta kunna mana Gen ɗin kafin ki zauna, Allah yasa ma muna da ishashshen mai a ciki."
Wucewa tayi ta kunna sannan ta wuce ta wanke hannu ta zo ta zauna, ta saka hannu a abincin tana cewa, "wai Aunty Zahra aina kika samu wannan guy ɗin ne?"
Zahra kallonta tayi tace, "wai Salisu? Ba ki sanni dashi bane? Shi ne fa wanda nace miki mun haɗu a bikin gidan Jamila ƴar gidan sanata da muka je mata, Ni ban ma san waye ya nuna mishi gidan mu ba, muna dai waya dashi kusan kwana biyu, sai yau kuma na ganshi ya zo."
"To shi ɗan gidan waye ne? Ba ki bani labari ba Mamana?" Inji Inna tana washe baki
Dariya suka yi gaba ɗayansu
Yayinda Zahra take basu labarin Salisu da aikin da yake yi
Itama Arab kuɗin da Tariq ya bata ta ciro ta miƙa wa Inna duka tana cewa, "nima kamun wani nayi wlh, duk da ban san ɗan waye ba amma da alamu yana da fararen." Ta ƙare maganar tana dariya cike da farin ciki
Haka su ma suna taya ta
Inda Inna tace, "ai na san ki Autana babu wasa a lamarin ki, sai dai idan ba ki fita ba, Allah yayi muku albarka baki ɗaya, haƙiƙa na haifi yara masu farin jini, hakan a jini na yake wlh, Ni na san da haka, duk wani me baƙin ciki sai dai ya mutu, ga shi yara mata suna share min hawaye."
Dukkan su murmushi suke yi suna sauraron Innar tasu. Da haka suke ta hira abin su
Yayinda Arab ta tashi ita ta nufi bayi, bata jima ba ta fito ta ɗaura alwala ta wuce ɗakinsu ta rama sallan da ake bin ta na magriba da isha'i. Sai ta zauna a ɗakin tana waya da Ibrahim
A nan yake sake bata labarin Mutumin da ya samo mata, da komai nashi sai da ya faɗa mata, sannan yace, "ta kira shi su soma magana yanzu."
Tace, "a'a sai zuwa gobe."
Dariya yayi yace, "ai girman ki ne Besty na, ina jin daɗin jan ajin nan naki, gaskiya ke ta daban ce a cikin mata, har yanzu ban ga kamar ki ba, kina lokaci ƴan mata na, kin fi ƙarfin Yaro sai dai baban Yaro."
Itama dariyan tayi tana cewa, "Besty kana fasa min kai da yawa."
"Ai matsayin ki ne My Besty, ke ɗin ce ban san yanda zan kwatanta ki ba, amma wlh kin kere duk wata Mace da na sani a rayuwata, Allah ya barmu tare."
"Amin." Tayi maganar tana dariya, "shiyasa nake ƙara sonka Besty na."
"Nima haka Besty, i love You wujiga-wujiga, ba don kin fi ƙarfi na ba da tuni nayi wuff da ke."
Dariya take yi sosai
"Allah kuwa My Besty, yanzu meye tukuici na?"
"Oh Besty! Ba ka yin abu don Allah fa na lura?"
Kashe murya yayi tare da cewa, "haba dai, Ni na isa? Ai duk abun da zan miki don Allah ne, kin san Ni na sanki, Ni da ke ba ta ɓaci, Allah ne ya haɗa jinin mu, abun da kike so shi nake so, haka kuma abun da kike ƙi shi nake ƙi, ke ma kin sani ai.. kawai dai kwaɗayin nawa ne ya tashi wlh."
"Uhmm shikenan. Let's meet tomorrow."
"Ok. But ba ki bani labarin Mutumin da kuka haɗu ɗazu ba?"
"Ai yanzu zan faɗa maka ka san ba na ɓoye maka komai." Daga nan ta ba shi labarin yanda suka yi. Basu jima suna wayan ba ta katse sabida ganin baƙuwar number tana kiran ta. Bayan ta ɗauka sallaman Tariq ya doki kunnen ta, rage murya tayi tana kwanciya a kan gadonta, yayinda ta juya baya ganin Ummu da Zahra sun shigo ɗakin. Haka tayi ta wayanta baza ka taɓa cewa waya take yi ba. Sun raba dare suna tare da Tariq before su yi sallama ta kwanta
A time ɗin su Ummu su ma har sun yi barci.
Zuwa washe gari kuma suka ta fi makaranta. Dayake ita Arab text suke yi a school, saura two weeks su fara Exams, daga nan kuma sai su shiga S.S 3. Ƙarfe sha biyu ta dawo gida
A lokacin Baba yana gida domin dawowar shi kenan daga wajen suyan kifin sa; yake sanar da Inna halin da Firdausi take ciki. Mijinta Nafi'u ya kira shi yace mishi, "bata da lafiya, yanzu haka suna asibiti an kwantar da ita, duk da dai yace jikin da sauƙi yanzu."
"To Allah ya sauwaƙe." Cewar Inna tana wucewa cikin kichen tare da cewa, "Auta har kin dawo?"
"Eh Inna." Ta furta itama tana shigowa tare da zama a kan kujeran zuƙuno, sai kuma ta kalli Babansu tace, "sannu Baba."
"Yauwa Aisha Humaira. An dawo?"
Fitowar Inna tana kallonta tace, "wai ba karatun ne kika dawo da wuri?"
"Akwai mana, muna yin text ne kuma ba wani abu ake yi ba shiyasa na dawo."
Baba ya kalli Innan yana cewa, "yanzu babu wanda zai je a cikin ku ne? Ai ya kamata ko ɗaya daga cikin yaran ne ya je ya zauna da ita, itama zata ji daɗi idan ta ga ƴan uwa, Mijin yace min idan da hali wata ta zo ta zauna da ita tunda kullum damuwar ta yaran nan ne, ta ce a tura mata ɗaya a ciki."
Mitsitstsike baki Inna tayi da cewa, "a tura wa? Ai babu inda zasu je tunda kowacce ba zaman banza take yi ba, in ba iya shege ba ai ta san babu wanda zai je yayi mata bauta tunda ta san suna makaranta, kuma sana'ar nawa ubanta zai yi min?"
Shiru Baba yayi be iya cewa komai ba illa kallonta da yake yi, sai kuma ya girgiza kanshi sabida takaicin Inna
Arab tace, "Inna ni zan je domin dama ina son zuwa, yakamata ace ko sau ɗaya ne mun je amma har yanzu bamu ƙara zuwa gidanta ba tun auren."
"To makarantar naki fa Auta? A'a babu inda za ki je."
"Allah Inna zan je, ai Ni nace miki ina son zuwa, kuma makaranta bani da matsala da hakan tunda Exams ya rage kuma ba yanzu zamu yi ba, har zan je in dawo, zan mata kwana biyu sai in dawo."
Baba washe baki yayi yace, "yauwa A'isha, ai zata ji daɗi idan ta ganku, to yaushe za ki tafi in ba ki kuɗin mota?"
"Ka bar shi kawai Baba ina da kuɗi, idan rana tayi sanyi sai in wuce."