← Book details Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 52

Sashe 4

Rudin Duniya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Shiru suka yi babu mai cewa uffan a tsakanin su, inda suke sakarwa juna wani irin kallo me tattaro saƙonnin zuciyoyin su suna aikawa juna. Yayinda murmushin farin ciki ke kwance a kan fuskartasu cikin shauƙi; tamkar sun san juna da daɗewa a yanayin kallon da suke yiwa kansu

Tsawon mintuna biyar before ya ja wani irin dogon numfashi yana lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta, sai ya buɗe baki cikin wani irin yanayi yace, "Gimbiyyata."

Ɗan waro idanu tayi cikin salo da guntun murmushin ta tace, "har na zama taka?"

"Eh mana, wace ce Gimbiyyata idan ba ke ba? Ai babu wata mace kyakykyawa a faɗin duniyar nan kamar ki, ba ki san jimawan da nayi ina bibiyan ki ba ko? Uhmm zuciyata ta jima da makancewa a kanki, ban yi tunanin zan iya kaiwa har wannan lokacin ban sanar da ke abun da ke raina ba, sai dai kuma ɗan wata tangarɗa da aka samu wanda ya hana Ni bayyanuwa a gaban ki, amma yanzu gani na dawo." Sai yayi shiru yana sake zuba mata idanu kamar yanda itama take mishi wani irin kallo me saka shi a wani irin ɓigirin da be taɓa tsintan kanshi ba, "na san za ki yi mamaki idan nace miki na san komai game da ke, Arab zuciyata ta makance a tun sanda idanuwana suka soma tozali da kyakykyawar fuskarki, na kasa natsuwa tun sanda na ganki, wlh ban taɓa jin wata ɗiya Mace ta shiga raina kamar ki ba, na so in jure amma na kasa, don Allah na zo da ƙoƙon barata ki taimaka ki amshe Ni a matsayin masoyin ki na gaskiya, ina ƙaunar ki! I love You A'isha Humaira, i love You with all my heart!"

Lumshe manyan idanuwanta tayi sabida jin sunan da ya kira ta, ba kowa yake kiranta da sunan ba sai mahaifin ta, shi kaɗai ne ba ya kiranta da suna Arab sai A'isha Humaira. Buɗe idanun tayi ta zuba mishi tana kallonsa da shu'umin murmushin ta da a koda yaushe yake saman fuskarta. Bata yi magana ba illa kallonsa da take yi tamkar zata cinye sa babu wani ɗar ko jin kunya a tare da ita, hasali ma tsantsan gogewa ne irin nata na bariki

Shi kuma sai yace, "kin yi shiru Gimbiyyata? Ko so kike yi zuciyata ta buga?"

Wani guntun murmushi ta sauke before tace, "Ina wani tunani ne a raina that's the reason da ka ji nayi shiru."

"Amma ba ki yarda da Ni bane? Wlh ina ƙaunar ki! Don Allah kiyi min magana ko ya ya ne inji daɗi." Sai ya saka hannayen sa biyu ya kamo nata da take faman shafa fuskarta dasu, ƙurawa junan su idanu suka yi na ƴan seconni before yace, "ina sonki! Me kike so in yi miki da za ki yarda?"

Still murmushin tayi tana cije baki tare da sake narke idanuwanta tana wani luuu dasu tamkar zata rufe sai kuma ta buɗe su, cikin wani irin kallonta me sake zautar da duk ma'abocin da tayi masa tare da fitar dashi a wani yanayi lokaci ɗaya

Wanda hakan ne ya soma tasiri a jikinsa har be san sanda ya sake damƙe hannayenta a cikin nashi ba yana wani irin murza mata cike da wani irin feelings da ya taso mishi

Hakan yasa tayi murmushi kaɗan tana cewa, "har yanzu ba ka sanar da Ni kai wane ne ba balle in so ƙulla alaƙa da kai."

"Haba idan har don wannan ne kar ki wani damu, na sha'afa ne, suna na Tariq... Tariq Muhammad Auwal, Ni mutumin Samaru ne, ina zaune tare da iyaye na da ƴan uwana, kuma abun farin cikin bani da Mata." Ya ƙare maganar yana mata murmushi

Yayinda ita kuma ta saki dariya kaɗan wanda ya bayyana haƙoran ta, still idanuwanta a cikin nasa, sai kuma ta sake sakin murmushinta tana janye hannayenta a cikin nasa tace, "meyasa za ka taɓa min jiki ba tare da mun yi farashi ba? I'm an expensive girl."

"Don't worry, I have the money to pay you until you say it's enough."

"Really?" Tayi maganar tana ɗan waro idanu waje wadda ya zame mata ɗabi'a; kuma yake ƙara mata kyau ainun

"Yeah. You just give me a chance."

Leɓen ƙasan bakinta ta shigar cikin bakinta tana tsotsa cikin salo da jan hankali, sai kuma ta cire tana ɗage kafaɗa tare da faɗin, "fine. I answer you both hands."

Dariya yayi cikin farin ciki tare da cewa, "gaskiya ke ta daban ce, na ji na ƙara sonki matuƙa, but yanzu kin bani damar taɓa hannun ki ko?" Ya ƙare maganar yana kashe mata ido ɗaya da murmushi a fuskarsa

"Me kake ci na baka na zuba? kar ka damu, har sai ka gaji da taɓawa."

"Haba idan ko haka ne bazan taɓa gajiyawa da taɓa kyakykyawar halitta kamar ki ba, ba ki san yanda kike da matsayi a cikin raina ba."

Bakinta ta ɗan turo gaba before ta ja numfashi tace, "ok. Zan tafi, ka ga dare yayi."

"To, babu ko ɗan kiss haka zamu rabu?"

Ƙura masa idanu tayi tana kallonsa na ɗan wani daƙiƙu, sai ta saki wannan shu'umin murmushin nata kafin tace, "me kake yiwa sauri haka? Za ka samu abun da ya fi kiss ma, but not know."

Langaɓe kai yayi, yayi mata fuskar tausayi tare da cewa, "Please Princess."

"No. Zan ta fi." Ta furta tana ƙoƙarin buɗe ƙofan

Sai yayi saurin kamo hannun ta da cewa, "haba Gimbiyyata kar ki tafi, I'm sorry to, na daina maganar."

Hannunta ta zame tana kallon fuskarsa

Sai yayi mata murmushi yace, "to ki bani Numban ki mana."

"Ok." Kawai ta furta tare da karanto mishi numbern

Sai ya rubuta sannan ya buɗe lockern motan ya ciro kuɗi 20k ya miƙa mata

Ta sanya hannu kuwa ta amsa ko jan aji bata yi ba, sai ga kyakykyawar murmushin ta ya bayyana a kan fuskarta, yayinda take bin sa da kallo me ban sha'awa tace, "tnx. Bye."

"Bye dear." Sannan ya ɗaga mata hannu yana mata murmushi har ta fice, sai da ya ga tafiyar ta before ya ja motan ya bar wajen cike da farin ciki a zuciyarsa.

_Don't forget to follow me on Wattpad, and voted 🙏🙏. Tnx._
[07/07, 11:27 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍

    *RUƊIN DUNIYA!*

🌍🌍🌍🌍🌍🌍

*NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL*
_UMMUDAHIRAH_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝*

*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

                  *P.W.A✍️*

_________________________

*BABI NA UKU*

_______________A bakin ƙofan gidan su ta ci karo da mahaifinsu, wanda yake zaune tun dawowar shi masallaci sallan isha'i, ya shimfiɗa tabarma yana shan iska. Ganinta ne yasa ya kira sunan ta yana cewa, "A'isha Humaira daga ina?"

Yamutsa fuska tayi tana ɗan sosa kanta tace, "Baba daga wurin saurayi na."

Shiru yayi yana kallon ta don ya san halinta ba kunya ne da ita ba, bata da ɓoye-ɓoye abin da ke ranta shi take faɗa. Ganin zata wuce ciki sai yace mata, "dawo ban sallame ki ba."

Dawowa tayi tana faman tura baki tare da ƙunƙunai

"yanzu A'ishah Humaira abun da kika ɗaukarwa kanki kenan? Ban hana ku yawon dare ku kai war haka baku dawo gida ba?"

"To Baba ai nace maka wajen saurayi na naje, ba fa yawo na je ba ina nan bakin layi."

"Shikenan. Allah ya shirya, idan kin shiga ki kawo min abinci na in CI a nan."

Wucewa tayi ba tare da ta amsa mishi ba ta shige gidan

Yayinda shi kuma ya girgiza kansa a ransa yana takaicin wannan rayuwa na yaranshi, ya rasa yanda zai yi ya gyara su, ko yayi ma a banza tunda uwarsu tana warware wa, duk halin su ɗaya gaba ɗaya babu me kallonsa da wani ƙima, sun riga sun taso ba sa shakkar shi bare tsoron shi, tamkar shi ba mahaifinsu ba saboda yanda suka ɗauke shi, ko ince yanda uwar su tayi musu tarbiyya, Firdausi ce kawai ta fita zakka a cikin su, kuma duk hakan yana faruwa ne kasancewar sa me tsananin haƙuri kuma mara faɗa, yana da sauƙin kai ko kaɗan be iya faɗa ba bare ya ce zai ɗauki mataki a kansu, yana ƙaunar yaranshi shiyasa a kullum fatan shiriya yake musu, duk da abun yana matuƙar damun shi domin yanzu babu inda gidan shi bai zagaya ba a faɗin arean nan, kowa ya san yaran shi basu da tarbiyya, wasu ma don rashin ta ido har taren shi suke yi a hanya suna mishi zancen Yaran shi basu da tarbiyya, ya kan yi kuka wani lokacin saboda be san yanda zai yi ba, yayi nasihan duk wani abu da ya kamata uba yayi; yayi musu, amma uwar su ta ɗaure musu gindi, bai da wani fawa a gidan, bare yanda ta mallake shi sai abun da tace, shiyasa be da kataɓus a gidan, ko ya so ɗaukar mataki mummuna ba ya iyawa, sai dai ya zira musu idanu yana musu addu'ar shiriya, ya san wata rana Allah zai dubi maraicin sa ya shirya mishi su, fatansa kenan a rayuwa. Numfashi kawai ya ja yana ci gaba da jan carbin shi.

             *******

       Arab kuwa tana shiga gidan ko sallama bata yi ba
Chapter 4 · 0% Book details