Sashe 9
Mawahib Complete Hausa Novel · about 8 min read
Adede lokacin Mawahib tazo kofar dakin nasu,a lokacin Captain Aryan baibawa Ashraf amsa ba, ita Kuma Jin shiru tayi tunanin basa cikin dakin,ahankali tatura qofar dakin ta shigo, gabanta ne yafadi ganin murd'ad'd'an jikinsa abaiyane,cikinsa har wani hawa-hawa yake alamun yana motsa jiki,ga faffadan qirjinsa wani irin gashi mai laushi ya kwanta,bata ta6a ganin namiji hakaba,gaba daya saita diririce jikinta yadauki rawa taqame awajan, adede lokacin Captain Aryan wanda bai lurada zuwan Mawahib dakinba,yasaki wata irin dariya wadda tunda Mawahib take, bata ta6a ganin yayi dariya haka ba,cikin dariya yacewa Ashraf "ta'inda ake hawa batanan ake sauka ba?,inacin abinda yabani najini nadawo Normal,daga ranar ban sake cewa zansha ba"
Suka saki dariya gaba dayansu,yajuya zai goge kunnansa na hannun dama, karkatawar da zaiyi yaganta a tsaye idonta yayi tsuru-tsuru, lokaci daya annurin fuskarsa ya sauya,ya wullar da towel din dake hannunsa,cikin 6acin rai yadaka mata wata irin tsawa yace"stupid girl....mekikeyi anan!!!?"
tun kafin yagama rufe bakinsa Mawahib tajuya da gudu tabar wajan,yanda yaga uban Hips dinta suna kad'awa saboda gudun datake hakanne yasake 6ata masa rai, 'yar qanqanuwar yarinya hartasan tayi ciko...(😱)
Ashraf ya ajiye manda yake shafa wa yataso yaduba baiga kowa ba,cikin damuwa yace"miye haka Aryan? Mawahib ce tazo kakoreta ko?"
Cikin 6acin rai yace"tayaya yarinya zatazo taganni ahaka ta rainani?"
Ashraf yace"nina kirata tazo tagyara mana dakinfa"
"ta barshi,kaima idan bazaka gyaraba kabarshi"
Ashraf yace"kaine qarami,kaine zaka gyara"
Aryan yace"minti nawa kabani?"
Ashraf ya harare shi yace"au Allah? to ko zamuje a tambayi Momy?"
Cikin sauri Aryan yace"muje"
Kamar wani abun arziqi zasuyi haka suka shirya cikin sauri kai tsaye suka nufi part din Hajiya Kilishi,suna shiga Ashraf yace"Momy"
Shima Aryan din yace"Momy"
Tasan duk lokacin dasuke mata irin wannan kira to musu sukeyi a tsakanin su,cikin sanin abunda ya kawosu Hajiya kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,shekaru ko? nasani, dan Allah kurabu dani zuwa yanzu yaci ace kun daina wannan musun"
Alqali dayake zaune yanashan tea yakallesu yayi murmushi,wankan shadda su kayi mai launin light blue,banda shine ya haifesu to zaiyi wahala ya banbance su saboda hatta agogonsu iri daya ne, hular dake kansu ma iri dayace,koda yaushe yana alfahri da 'ya'yansa,tsugunnawa sukai suka gaida shi, sannan Hajiya kilishi tafara hada musu tea din suma, Ashraf yanacin sultan Chips din dake gabansa yana turawa Mawahib text naban haquri,sannan yasake roqarta akan taje tagyara musu dakin itada Nabiha, Mawahib tana ganin text din ta fadawa Mamy, sannan taje tasamu Nabiha, suka nufi dakin su Yaya Ashraf din,suna zuwa suka fara gyara dakin,duk wani kaya dasuka ganshi babu ninki suka ninkesu, suka adana musu shi,saida suka wanke har toilet din komai yayi tsaf, a lokacin aka kira wayar Nabiha, ta amsa wayar tafita, Mawahib kuma ta dauki air freshener tana fesawa a dakin,tabude fridge din dakin tasake gyara lemuka da ruwan dasuke ciki,glass cup din dasuke kan fridge din suma tasake gogesu tana gyara musu zama, adede lokacin suka shigo dakin duka su biyun,Aryan yana ganinta ya daure fuska yanuna mata hanyar fita daga dakin, cikin tsawa yace"get out...."
Tsawar da yayi matane yasa ta tsorata batasan lokacin data saki cup din hannunta ba, nan take yafashe,bai damu da yanayin datake ciki na tsorata ba yasake daka mata tsawa yace"zoki fice nace"
cikin 6acin rai shima Ashraf yace"Mawahib karki fita"
Cikin sauri Captain Aryan ya'iyo kanta gadan-gadan,cikin sauri tayi gudu ta6uya a bayan Yaya Ashraf,ganin Captain Aryan yana tattare hannun rigar sa hakan yasa Ashraf yasaka hannu zai kareta,Mawahib kuwa tana ganin Yaya Ashraf ya tareta tayi qasa tarage tsawon ta, tafice da gudu daga dakin.
Cikin 6acin rai Ashraf yace"wai dan Allah menene damuwar kane da yarinyar nan? Aaka kawai yarinya tana walwalarta harka tsorata ta kasa tafita babu nutsuwa"
Captain Aryan yana jinsa ya shareshi, Ashraf yaci gaba da fadin "meta tsare ma? haka kawai kasaka yar mutane agaba bakada buri wanda yafi ka zalunceta?"
Cikin 6acin rai Captain Aryan yace"wai Ashraf saboda wannan abar kakemin masifa?kanamin masifa saboda ita kamar wanda ka haifeni?"
Lokaci daya jikin Ashraf din yayi sanyi,koda suke fadansu saide akan abinda ya shafesu,amma basa fada saboda wani, bazaka ta6a Jin kansuba inde akan wani ne,saide akan abinda ya shafesu su biyu,to yanzu kuma ga Mawahib tana nema tashiga tsakani, cikin damuwa yasaka hannunsa yadafe goshinsa(🤦🏻♂️)
Sannan ya kalli Captain Aryan yace"meyasa naga kamar kana cikin damuwa ne?,meyake damunka?"
Cikin damuwa Captain Aryan yace"no,babu abinda yake damuna,kawai de banajin dadin yanda yarinyar nan take nema tashiga tsakanina dakai,kadena son abinda nakeso saboda ita,banajin dadin zaman,gara in tafi "
Cikin sauri Ashraf yace" babu inda zakaje"
sannan yakama hannunsa suka zauna abakin gado,ya Kalle shi yace"inajin wani iri wannan zuwan naka Aryan,may be idan katafi sainayi rashin lafiya kamar yanda nasaba,kokuma kai kayi"
Captain Aryan yace"kadena tunanin komai,babu abinda zai faru insha Allah,bani kad'ai nazo ba,akwai yaran dasuke tare dani,yakamata inkoma next time idan nazo nikad'ai saina huta sosai"
Cikin sanyin jiki Ashraf yace"to Allah yasa,yau ba muje wajan Anty Mamy ba"
Captain Aryan ya yatsina fuskar sa yace"inason ganin Anty Ma-my, but banason ganin wannan yarinyar..."
Ashraf yalumshe idonsa ya bude tareda girgiza kansa baice komai ba.
Haka suka wuni a daki babu inda suka fita,saide suje sallah sudawo,Captain Aryan baya gajiya da zance inde tareda Ashraf ne,suyi fada su shirya kansu da kansu babu wanda yajisu.
Da daddare suna kwance sunyi shirin bacci Captain Aryan yadauki wayarsa yakamo wani hadadden gida gari guda kamar ba'a qasar yake ba,yabawa Ashraf wayar yace"Ash kaga aikin gidan nan har sun gamashi,ansaka komai aciki,wannan komawar da zanyi a cikinsa zan sauka,matata ma nasa sun saka mata komai da komai kawai clothes ne babu,shima dan bansan size dinta bane danayi mata order ansaka mata kafin tashigo gidan, but....naso ace tareda ita zamu fara shiga"
Ashraf ya kalli photunan gidan yace"Wow...,gaskiya yayi kyau,banbancin sa da nawa na nan garin kadanne,naka farin fenti nawa brown,to amma kayi auren mana saika tafi da matarka kushiga tare tunda haka kakeso"
Captain Aryan ya girgiza kansa kawai sannan ya basar da zancen alamun bayaso,yace"nima kayan ciki har windows din duka brown ne,yayi kyau sosai,inaso wannan shekarar gaba daya yan gidannan sutafi aikin hajji,daga nan kawai saika taho muje muyi zamanmu a gidan muhuta kafin su dawo"
Cikin farinciki Ashraf yace"babu damuwa Allah yakaimu,sannan bazaka samu lada kai kadai ba,kai kabiyawa su Daddy nikuma su Momy,sannan gaskiya ni bazan tare agidana yanzu ba,saina jira na auri Mawahib tukunna,sai mu koma tare rana daya,duk wasu yan'uwa zan basu sati daya sugama zuwa ganin amarya, daga nan kuma zan rufe gidan in fara amarci na hankali na kwance"
Cikin yatsina fuska Captain Aryan yace"mekace? kayi aure kuma kana kallon amaryar har tsawon sati daya?kayi aure bakayi komai ba a wannan ranar saika ce wani kidahumi?"
Ashraf yace"menene yakawo maganar kidahumi kuma Aryan?,kana nufin kai bazaka Iya jiran sati daya ba kenan? kaide matarka taga ta kanta wallahi,zan fadawa Daddy yayima aure"
Cikin rashin damuwa Captain Aryan yace"gaskiya kam,because nide babu wasa,cikin kwana biyu ma zan'iya yimata ciki"
Ashraf yanajin haka yakai masa dukan wasa,yariqe kunnansa yace"bakajin magana Aryan"
Dahaka sukai addu'ah suka kwanta cikin farinciki.
Washegari yahada kayansa tsaf zaikoma bakin aikinsa,jikin Ashraf duk yayi sanyi,kokadan bayason tafiyar Aryan din baisan meyasaba,saida sukayi sallama da Hajiya Kilishi,bayan ya ajiye mata wasu manyan kudade a gabanta, sannan sukaje yayiwa Mama Sadiya sallama,itama ya ajiye mata kudi masu yawa akan kujera, sannan suka d'unguma suka tafi part din Mamy.
Suna shiga part din Mamy suka tarar da'ita tareda wata baquwa, babbar mace ce sosai tana zaune akan kujera da wayarta a hannunta tana dannawa, Cikin farinciki Mamy tace"Captain har tafiyar tatashi?"
Captain Aryan yayi murmushi ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa,yace"Anty Ma-my barka da safiya"
Ta amsa masa cikin girmamawa tareda shige wa dan qaramin kitchen din dake falon ta.
Ashraf ya kalli babbar matar dake zaune afalo yace"ina kwana"
Cikin walwala tadago kanta tace"lafiya kalau yagida"
Kafin Ashraf yabata amsa shima Captain Aryan cikin sauri ya rissina yace mata "Barka da safiya"
Ta kalleshi tace"masha Allah,yawwa sannunku"
Adede lokacin Mamy tafuto daga kitchen hannunta daukeda leda,tabawa Captain Aryan tace"ga dambun kaza"
Ya kalli ledar hannunta cikin shagwa6a yace"haba Anty Ma-my, gaskiya ni bazan tafi dashi a leda ba,saikace wani marar gata,Allah nide saide ki sauya min,haba Anty Ma-my kina d'an girmama ni mana,amma haka abu aleda?"
ya qarasa maganar cikin shagwa6a kamar zai fashe da kuka.
Mamy tace"naqi,bazan sauya maba, kaje kayi aure sai matarka ta dinga saka maka a flask"
Captain Aryan yayi shiru yana kallon wannan leda,duk girmansa Anty Mamy bazata sake girmama shi tazuba masa a qayataccen food flask ba?bai Isa yayi magana ba komai sai tace yaje yayi aure(😔)
Ashraf yayi murmushi yazuba musu ido yana kallon wannan drama tasu, adede lokacin Mawahib tafuto daga dakinta tana sanye cikin riga da siket 'yan kanti, amma tasaka mayafi a jikinta, ganinsu yaya Captain a falon yasa taja ta tsaya daga nan bakin qofar d'akinta.
Ashraf yana ganin futowar ta yamaida kallonsa gareta,yazuba mata manyan idonsa yana kallonta cikeda so.
Qawar Mamy dake zaune agefe tana ganin abinda yake faruwa tayi dariya tace"Maryam wannan kamar yaran nan naki dakika yayesu ko?"
Cikin sauri Captain Aryan yajuya yana sake kallon matar, tunda yaji tana maganar lokacin da Anty Mamy ta yayesu yasan cewa tabbas babbar mace ce,kuma tasan yarintar su,yagama qarewa matar kallo kenan yajuyo zai maida kallonsa wajan Mamy anan idonsa yasauka akan Mawahib,sai akayi dace idonsa ya sauka cikin nata qwayar idon,lokaci daya bugun zuciyar su yasauya,cikin sauri kowa ya janye idonsa.
Mamy tayi murmushi tace"Sister Hadiza sune wallahi, gasunan duk sun girma"
Babbar matar da aka kira da Sister Hadiza tace"ikon Allah,kinga duk sun girma sun taroki kamar wasu qannanki, waye kwa me tsoron ruwan zafi acikinsu lokacin da aka musu kaciya?"(🙊🙈😂🙆🏻♀️)
Mawahib ta dago kanta da sauri ta kalli Sister Hadiza.
Cikin sauri Captain Aryan ya runtse idonsa, saboda yasan akansa ake maganar, shitake tambaya, yatuna Mawahib fa tana cikin falon nan,shikkenan matar nan tagama dashi,ta kunyata shi agaban wannan yarinyar, cikin sauri yafuto daga falon da ledar dambun kazansa a hannu yanaji kamar ya nutse awajan dan kunya(😂)
Ashraf yayi dariya shima yabi bayansa
(Sister Hadiza baki kyauta mana ba🤣 asauka lafiya captain 🙏🏻)
Suka saki dariya gaba dayansu,yajuya zai goge kunnansa na hannun dama, karkatawar da zaiyi yaganta a tsaye idonta yayi tsuru-tsuru, lokaci daya annurin fuskarsa ya sauya,ya wullar da towel din dake hannunsa,cikin 6acin rai yadaka mata wata irin tsawa yace"stupid girl....mekikeyi anan!!!?"
tun kafin yagama rufe bakinsa Mawahib tajuya da gudu tabar wajan,yanda yaga uban Hips dinta suna kad'awa saboda gudun datake hakanne yasake 6ata masa rai, 'yar qanqanuwar yarinya hartasan tayi ciko...(😱)
Ashraf ya ajiye manda yake shafa wa yataso yaduba baiga kowa ba,cikin damuwa yace"miye haka Aryan? Mawahib ce tazo kakoreta ko?"
Cikin 6acin rai yace"tayaya yarinya zatazo taganni ahaka ta rainani?"
Ashraf yace"nina kirata tazo tagyara mana dakinfa"
"ta barshi,kaima idan bazaka gyaraba kabarshi"
Ashraf yace"kaine qarami,kaine zaka gyara"
Aryan yace"minti nawa kabani?"
Ashraf ya harare shi yace"au Allah? to ko zamuje a tambayi Momy?"
Cikin sauri Aryan yace"muje"
Kamar wani abun arziqi zasuyi haka suka shirya cikin sauri kai tsaye suka nufi part din Hajiya Kilishi,suna shiga Ashraf yace"Momy"
Shima Aryan din yace"Momy"
Tasan duk lokacin dasuke mata irin wannan kira to musu sukeyi a tsakanin su,cikin sanin abunda ya kawosu Hajiya kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni kilishi,shekaru ko? nasani, dan Allah kurabu dani zuwa yanzu yaci ace kun daina wannan musun"
Alqali dayake zaune yanashan tea yakallesu yayi murmushi,wankan shadda su kayi mai launin light blue,banda shine ya haifesu to zaiyi wahala ya banbance su saboda hatta agogonsu iri daya ne, hular dake kansu ma iri dayace,koda yaushe yana alfahri da 'ya'yansa,tsugunnawa sukai suka gaida shi, sannan Hajiya kilishi tafara hada musu tea din suma, Ashraf yanacin sultan Chips din dake gabansa yana turawa Mawahib text naban haquri,sannan yasake roqarta akan taje tagyara musu dakin itada Nabiha, Mawahib tana ganin text din ta fadawa Mamy, sannan taje tasamu Nabiha, suka nufi dakin su Yaya Ashraf din,suna zuwa suka fara gyara dakin,duk wani kaya dasuka ganshi babu ninki suka ninkesu, suka adana musu shi,saida suka wanke har toilet din komai yayi tsaf, a lokacin aka kira wayar Nabiha, ta amsa wayar tafita, Mawahib kuma ta dauki air freshener tana fesawa a dakin,tabude fridge din dakin tasake gyara lemuka da ruwan dasuke ciki,glass cup din dasuke kan fridge din suma tasake gogesu tana gyara musu zama, adede lokacin suka shigo dakin duka su biyun,Aryan yana ganinta ya daure fuska yanuna mata hanyar fita daga dakin, cikin tsawa yace"get out...."
Tsawar da yayi matane yasa ta tsorata batasan lokacin data saki cup din hannunta ba, nan take yafashe,bai damu da yanayin datake ciki na tsorata ba yasake daka mata tsawa yace"zoki fice nace"
cikin 6acin rai shima Ashraf yace"Mawahib karki fita"
Cikin sauri Captain Aryan ya'iyo kanta gadan-gadan,cikin sauri tayi gudu ta6uya a bayan Yaya Ashraf,ganin Captain Aryan yana tattare hannun rigar sa hakan yasa Ashraf yasaka hannu zai kareta,Mawahib kuwa tana ganin Yaya Ashraf ya tareta tayi qasa tarage tsawon ta, tafice da gudu daga dakin.
Cikin 6acin rai Ashraf yace"wai dan Allah menene damuwar kane da yarinyar nan? Aaka kawai yarinya tana walwalarta harka tsorata ta kasa tafita babu nutsuwa"
Captain Aryan yana jinsa ya shareshi, Ashraf yaci gaba da fadin "meta tsare ma? haka kawai kasaka yar mutane agaba bakada buri wanda yafi ka zalunceta?"
Cikin 6acin rai Captain Aryan yace"wai Ashraf saboda wannan abar kakemin masifa?kanamin masifa saboda ita kamar wanda ka haifeni?"
Lokaci daya jikin Ashraf din yayi sanyi,koda suke fadansu saide akan abinda ya shafesu,amma basa fada saboda wani, bazaka ta6a Jin kansuba inde akan wani ne,saide akan abinda ya shafesu su biyu,to yanzu kuma ga Mawahib tana nema tashiga tsakani, cikin damuwa yasaka hannunsa yadafe goshinsa(🤦🏻♂️)
Sannan ya kalli Captain Aryan yace"meyasa naga kamar kana cikin damuwa ne?,meyake damunka?"
Cikin damuwa Captain Aryan yace"no,babu abinda yake damuna,kawai de banajin dadin yanda yarinyar nan take nema tashiga tsakanina dakai,kadena son abinda nakeso saboda ita,banajin dadin zaman,gara in tafi "
Cikin sauri Ashraf yace" babu inda zakaje"
sannan yakama hannunsa suka zauna abakin gado,ya Kalle shi yace"inajin wani iri wannan zuwan naka Aryan,may be idan katafi sainayi rashin lafiya kamar yanda nasaba,kokuma kai kayi"
Captain Aryan yace"kadena tunanin komai,babu abinda zai faru insha Allah,bani kad'ai nazo ba,akwai yaran dasuke tare dani,yakamata inkoma next time idan nazo nikad'ai saina huta sosai"
Cikin sanyin jiki Ashraf yace"to Allah yasa,yau ba muje wajan Anty Mamy ba"
Captain Aryan ya yatsina fuskar sa yace"inason ganin Anty Ma-my, but banason ganin wannan yarinyar..."
Ashraf yalumshe idonsa ya bude tareda girgiza kansa baice komai ba.
Haka suka wuni a daki babu inda suka fita,saide suje sallah sudawo,Captain Aryan baya gajiya da zance inde tareda Ashraf ne,suyi fada su shirya kansu da kansu babu wanda yajisu.
Da daddare suna kwance sunyi shirin bacci Captain Aryan yadauki wayarsa yakamo wani hadadden gida gari guda kamar ba'a qasar yake ba,yabawa Ashraf wayar yace"Ash kaga aikin gidan nan har sun gamashi,ansaka komai aciki,wannan komawar da zanyi a cikinsa zan sauka,matata ma nasa sun saka mata komai da komai kawai clothes ne babu,shima dan bansan size dinta bane danayi mata order ansaka mata kafin tashigo gidan, but....naso ace tareda ita zamu fara shiga"
Ashraf ya kalli photunan gidan yace"Wow...,gaskiya yayi kyau,banbancin sa da nawa na nan garin kadanne,naka farin fenti nawa brown,to amma kayi auren mana saika tafi da matarka kushiga tare tunda haka kakeso"
Captain Aryan ya girgiza kansa kawai sannan ya basar da zancen alamun bayaso,yace"nima kayan ciki har windows din duka brown ne,yayi kyau sosai,inaso wannan shekarar gaba daya yan gidannan sutafi aikin hajji,daga nan kawai saika taho muje muyi zamanmu a gidan muhuta kafin su dawo"
Cikin farinciki Ashraf yace"babu damuwa Allah yakaimu,sannan bazaka samu lada kai kadai ba,kai kabiyawa su Daddy nikuma su Momy,sannan gaskiya ni bazan tare agidana yanzu ba,saina jira na auri Mawahib tukunna,sai mu koma tare rana daya,duk wasu yan'uwa zan basu sati daya sugama zuwa ganin amarya, daga nan kuma zan rufe gidan in fara amarci na hankali na kwance"
Cikin yatsina fuska Captain Aryan yace"mekace? kayi aure kuma kana kallon amaryar har tsawon sati daya?kayi aure bakayi komai ba a wannan ranar saika ce wani kidahumi?"
Ashraf yace"menene yakawo maganar kidahumi kuma Aryan?,kana nufin kai bazaka Iya jiran sati daya ba kenan? kaide matarka taga ta kanta wallahi,zan fadawa Daddy yayima aure"
Cikin rashin damuwa Captain Aryan yace"gaskiya kam,because nide babu wasa,cikin kwana biyu ma zan'iya yimata ciki"
Ashraf yanajin haka yakai masa dukan wasa,yariqe kunnansa yace"bakajin magana Aryan"
Dahaka sukai addu'ah suka kwanta cikin farinciki.
Washegari yahada kayansa tsaf zaikoma bakin aikinsa,jikin Ashraf duk yayi sanyi,kokadan bayason tafiyar Aryan din baisan meyasaba,saida sukayi sallama da Hajiya Kilishi,bayan ya ajiye mata wasu manyan kudade a gabanta, sannan sukaje yayiwa Mama Sadiya sallama,itama ya ajiye mata kudi masu yawa akan kujera, sannan suka d'unguma suka tafi part din Mamy.
Suna shiga part din Mamy suka tarar da'ita tareda wata baquwa, babbar mace ce sosai tana zaune akan kujera da wayarta a hannunta tana dannawa, Cikin farinciki Mamy tace"Captain har tafiyar tatashi?"
Captain Aryan yayi murmushi ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa,yace"Anty Ma-my barka da safiya"
Ta amsa masa cikin girmamawa tareda shige wa dan qaramin kitchen din dake falon ta.
Ashraf ya kalli babbar matar dake zaune afalo yace"ina kwana"
Cikin walwala tadago kanta tace"lafiya kalau yagida"
Kafin Ashraf yabata amsa shima Captain Aryan cikin sauri ya rissina yace mata "Barka da safiya"
Ta kalleshi tace"masha Allah,yawwa sannunku"
Adede lokacin Mamy tafuto daga kitchen hannunta daukeda leda,tabawa Captain Aryan tace"ga dambun kaza"
Ya kalli ledar hannunta cikin shagwa6a yace"haba Anty Ma-my, gaskiya ni bazan tafi dashi a leda ba,saikace wani marar gata,Allah nide saide ki sauya min,haba Anty Ma-my kina d'an girmama ni mana,amma haka abu aleda?"
ya qarasa maganar cikin shagwa6a kamar zai fashe da kuka.
Mamy tace"naqi,bazan sauya maba, kaje kayi aure sai matarka ta dinga saka maka a flask"
Captain Aryan yayi shiru yana kallon wannan leda,duk girmansa Anty Mamy bazata sake girmama shi tazuba masa a qayataccen food flask ba?bai Isa yayi magana ba komai sai tace yaje yayi aure(😔)
Ashraf yayi murmushi yazuba musu ido yana kallon wannan drama tasu, adede lokacin Mawahib tafuto daga dakinta tana sanye cikin riga da siket 'yan kanti, amma tasaka mayafi a jikinta, ganinsu yaya Captain a falon yasa taja ta tsaya daga nan bakin qofar d'akinta.
Ashraf yana ganin futowar ta yamaida kallonsa gareta,yazuba mata manyan idonsa yana kallonta cikeda so.
Qawar Mamy dake zaune agefe tana ganin abinda yake faruwa tayi dariya tace"Maryam wannan kamar yaran nan naki dakika yayesu ko?"
Cikin sauri Captain Aryan yajuya yana sake kallon matar, tunda yaji tana maganar lokacin da Anty Mamy ta yayesu yasan cewa tabbas babbar mace ce,kuma tasan yarintar su,yagama qarewa matar kallo kenan yajuyo zai maida kallonsa wajan Mamy anan idonsa yasauka akan Mawahib,sai akayi dace idonsa ya sauka cikin nata qwayar idon,lokaci daya bugun zuciyar su yasauya,cikin sauri kowa ya janye idonsa.
Mamy tayi murmushi tace"Sister Hadiza sune wallahi, gasunan duk sun girma"
Babbar matar da aka kira da Sister Hadiza tace"ikon Allah,kinga duk sun girma sun taroki kamar wasu qannanki, waye kwa me tsoron ruwan zafi acikinsu lokacin da aka musu kaciya?"(🙊🙈😂🙆🏻♀️)
Mawahib ta dago kanta da sauri ta kalli Sister Hadiza.
Cikin sauri Captain Aryan ya runtse idonsa, saboda yasan akansa ake maganar, shitake tambaya, yatuna Mawahib fa tana cikin falon nan,shikkenan matar nan tagama dashi,ta kunyata shi agaban wannan yarinyar, cikin sauri yafuto daga falon da ledar dambun kazansa a hannu yanaji kamar ya nutse awajan dan kunya(😂)
Ashraf yayi dariya shima yabi bayansa
(Sister Hadiza baki kyauta mana ba🤣 asauka lafiya captain 🙏🏻)