← Book details Mawahib Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 68

Sashe 8

Mawahib Complete Hausa Novel · about 8 min read

Koda wasa baima kalli inda suke ba yabude get din zai shige,Nabil ya kalle shi cikin mutuntawa yace"barka da shigowa Ina wuni?"

Ba tareda ya kallesu ba yace"lafiya"
kamar anyi masa dole, yana shigewa ciki Nabil ya Kalli Mawahib yace"Sojan gidanku yadawo ne? naga shine baya fara'ah, kinsan niba ganesu nakeba"

Mawahib tayi wata dariya Mai kamada yaqe, tace"shine...,"

Saide cikin ranta tana mamakin sauya war Yaya Ashraf zuwa fishi, idan ta cewa Yaya Nabil bashi bane zai Iya tunanin wani abu, shiyasa tayi masa qarya cewa Yaya Captain ne.

Nabil yayi ajiyar zuciya yace"rannan naga bbc sunyi posting din karramawar da'aka musu,naga photon sa shida shugaban qasa, Allah yasanya Alkhairi"

Kanta aqasa tace masa "Amin ya Allah"

Motarsa yabude yadauko mata wata babbar leda fara, yabata yace "ki shiga da wannan ciki,babu yawa yar qaramar kyautata ce izuwa gareki"

Cikin sauri ta girgiza masa kai tace"A a,Mamy zatamin fada,babu ruwana ka barshi"

Murmushi yayi yace"naji, to ki kar6a zankirata awaya inyi mata magana"

Saida taji haka sannan ta kar6a tayi masa godia,yace zaije suyi sallama dasu Alqali sannan yawuce,tayi masa Addu'ah,sannan tajuyo zuwa cikin gida.

Tana shiga part dinsu, ta tsinci muryar Yaya Ashraf cikin fishi yana fadin"Amma Anty Mamy yaushe tafara karatu da zaku barta tafara sauraron samari yanzu? waye yabata damar kula samari haka anyhow....?"

baima tsaya jin amsar da Mamyn zata bashi ba yajuya cikin 6acin rai zai fice daga part din,yana ganin Mawahib abakin qofa a tsaye da U
uwar leda a hannunta yazo wucewa ta gefenta qiris yarage ya bigeta, cikin sauri ta matsa gefe, tsananin mamaki ya cikata dama shima yana fishi haka?(🤔)

Mamy takasa magana tabi Ashraf da kallon mamaki harya fice daga part din,a hankali tasaki murmushi ganin wannan qarfin hali nasa, gaba daya tagama gane inda yadosa,kuma hakan bazai ta6a iyuwa ba,koda ace Mawahib din tana sonshi dole zata haqura dashi, haka inma mazan gidan sukace zasu qullah to bazata yarda ba,saide wannan karon a saketa har abada tafice tabar familyn Alqali.

(wata sabuwa🥺😱)

Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼

Zaki turo 500 ta wannan account din

0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034

Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034

Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034

Amnah El Yaqoub✍🏻
[7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗
(Hot luv)

Writing By Amnah El Yaqoub

9&10

Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin Samun Audio Novel's👇🏻
https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels

Captain Aryan yaci gaba da fadin "please kadena min maganar ta"

Ashraf yace"dole inyi ma maganar ta kuwa, saboda Ina sonta, najira kadawo ne infara yima maganar,banason kai tsaye in yiwa su Daddy maganar, kaima kuma kadawo kace kana sonta"

Captain Aryan dayake kwance cikin wani irin fargici ya tashi zaune yace"inso wa? ni...? Inrasa wazan aura sai wannan abar?"

Cikin zafin rai Ashraf yace"yauka fara? sau nawa Ina nemo yarinyar dazan aura kana cewa kaima ita kakeso? ban'isa inyi sabuwar Baby ba, kaima saika sota, 'yanbiyu mata masu kama daya kakeso insamo mana? shiyasa nafara fad'ama maganar,kar inje infad'awa su Daddy inason Mawahib kaima ka dage kace kai sai ita..., inkasan kana sonta to tun wuri inyi shiru da maganar"

Cikin taqaici Captain Aryan yace"kaga Ashraf,dan Allah idan zakayi zancen 'yanmata, toka dena saka yarinyar nan aciki, idan zaka so kowacce irin yarinya tonima zan'iya sonta,saboda jinin mu ahad'e yake,zan'iya son dukkan 'yanmatanka,amma banda ita..."(🙆🏻‍♀️)

Ashraf yayi shiru yana qarewa dan'uwan nasa kallo, tunda yacewa Mawahib qwaila yake tantama aransa anya Aryan yana cikin hankalin sa kuwa?kokuma de ya makance?
Ahankali yasaki ajiyar zuciya yace"kagama?"

Kai tsaye Captain yace"ban gamaba,inaso kasani batada abubuwan dazaija hankali na har'insota,bazan ta6a sontaba har abada,nawuce ajinta,bata cikin tsarina,bata Isa takama qafar irin matar dazan aura ba, sannan kaima Ina gargadinka,karka bari Momy taji maganar nan ,kuma abinda ya shafeni kaima yariga ya shafeka,bana qaunar ta,saboda haka dole kaima karabu da'ita tunda bana sonta...."

Ashraf yace"saboda
kaine kakawo ni duniyar ko? to saina aureta,inyaso ka mutu"

Cikin sauri Captain Aryan yace"saide kaika mutu,kuma baka Isa ka auretaba INDE INA RAYE"

Ashraf yace"tosaika hana mugani"

Yafadi hakan tareda sakin tsaki, ya dauke fillonsa yamaida shi qafafun Aryan,ma'ana sukai kaida qafa.

Kusan minti biyar dukansu sukai shiru babu wanda yasake yin magana, sai can Captain Aryan shima yasaki tsaki yadauke fillonsa yadawo dashi kusadana Ashraf.(😂)

Ashraf yana jinsa yayi shiru ya qyaleshi,Captain yaji shiru Ashraf bai kula shi ba duk da yadawo da fillonsa wajansa,a hankali yace"Ashraf..."

Ashraf yayi shiru yaqyaleshi, yasake sakin dan qaramin tsaki yace"Ashraf katashi kayi Addu'ah"

Babu musu Ashraf yatashi yafara Addu'ah,saida yagama addu'ar sannan ya kalli Captain Aryan yace"kai kayi addu'ar ne?"

shima Captain Aryan yanajin Ashraf din yayi shiru yarabu dashi(😂)
Ashraf yasan sarai yana jinsa,sai yayi murmushi kawai yad'ora hannunsa akan lallausar sumar Aryan din batare daya qara magana ba,yanajin lokacin da Aryan din yafara bacci, amma shi bai fara bacci ba yana tunanin yanda zai 6ullowa iyayensu akan maganar aurensa da Mawahib,har wajan qarfe biyu nadare yana tunanin mafita,yanajin yanda Captain Aryan yaketa juye-juye kamar akwai abinda yake damunsa,ahankali ya rufe idonsa har bacci yayi nasarar daukar sa.

Cikin dare Captain Aryan yafarka dawani irin ciwon mara,tun yana daurewa harya fara ciza lallausan lips dinsa, ga esi yanayi adakin amma Captain Aryan sai gumi yake had'awa,ahankali ya runtse idonsa yana tuna shawarar da likita yabashi akan wannan ciwon cikin nasa yakamata ace yanemi mace yayi aure hakanne zai kawo qarshan jinyar,ahankali yatashi zai dauko maganinsa yaji bazai Iya miqewa ba.

Cikin sauri yafara tashin Ashraf, yace"Ash,tashi!!"

Cikin bacci Ashraf yabude idonsa a hankali,ganin Captain Aryan a zaune sai had'a gumi yake hakan yasa yatashi cikin sauri, yadora hannunsa a kafadar Captain din sannan yace"meyake damunka?"

Saida ya cija lips dinsa sannan yace"magani na,bani maganina"

Cikin sauri Ashraf yasauko daga gadon,yabude yar qaramar jakar da Captain din yazo da'ita ya dudduba sannan yaga maganin,wutar dake gefen gadon su ya kunna saida ya karanta yaga maganin menene, sannan yabashi,yaje fridge ya dauko masa gorar ruwa, cikin sauri Captain Aryan ya 6alli maganin yasaka a bakinsa, sannan yakafa gorar ruwan a bakinsa saida ya shanye shi tas, sannan yafara maida numfashi ahankali.

Ashraf ya dafashi yace"Aryan...,nayima magana kadena shan maganin nan,gara kazauna haka idan kayi mafarki shikkenan zakaji sauqin abinda yake damunka"

Captain Aryan da kansa yake sunkuye yad'ago ya kalli Ashraf yace"kullum zan zauna kenan banida aiki sai mafarki? ni bazanyi asarar abuna ba,na matata ne...."(🙈🙊)
Yaqarasa maganar cikin sigar shagwa6a kamar ba Soja ba

Dariya takama Ashraf,amma dayake yasan halin dan'uwan nasa akan wannan dariyar yanzu saiya fara yimasa masifa, saiya danne dariyarsa yayi murmushi yace"tokayi aure"

Cikin shagwa6a yace"niba wacce nakeso"

Ashraf yace"Okay...mugunta ce tasa kake rabani da 'yanmata na kenan ko? kai baka auraba niban aura ba"

Captain Aryan baice dashi uffan ba,yaja fillonsa ya rungume tareda runtse idonsa yana numfashi sama-sama har baccin wahala yadaukeshi.

Ashraf yana zaune yana kallonsa saida yaga yayi bacci sannan shima ya kwanta agefensa yayi bacci.

Dasafe bayan sungama buga ball dakinsu suka dawo kowa yayi wanka,gaba dayansu suna daure da farin towel a qugunsu sai wani d'an qarami guda d'aya kowa yana goge sumar kansa, Ashraf yad'auki wayarsa ya dokawa Mawahib Kira, a lokacin tana zaune tanashan tea tagama gyaran part dinsu kenan, har zuwa lokacin Mamy bata tashi ba kasancewar yau weekend ne bata tashi da wuri, mamaki ya kamata,kiran Yaya Ashraf da wannan safiyar lafiya? gaba daya sai taji tsoron daga wayar kartaje tunanin Nabiha yazama gaskiya idan kiranta yayi domin yafada mata yana sonta mezatace masa? haka ta kasa daukan wayar harta katse, daga nasa 6angaren yasake kira akaro na biyu,sai a lokacin ta dauka cikin ladabi tace"yaya Ashraf barka da safiya"

Saida yasaki wani murmushi najin dadi sannan yace"yawwa Mawahib idan kingama abinda kike please kizo ki gyara mana dakin nan..."

Cikin ladabi tace"to Yaya"

Daga nan yakashe wayar yad'auki mai zai fara shafawa, Captain ya
kalle shi yace"yanzu kai bakaji kunya ba?kasa yarinya agaba kana wani kashe murya saika ce kasamu wata babbar mace,wannan abun kunya har'ina "(😖)

Ashraf yayi murmushi yace"kaine kake ganinta amatsayin yarinya,amma Mawahib tanada abinda wata babbar ma batadashi,ka nemi mace kayi aure kaqi, ka dameni da juye-juye cikin dare dashan magani, kawai ka lalla6ani inbarma Mawahib,ninasan abinda nagani, kaima kuma idan ka qarewa yarinyar kallo zakasan akwai kayan alatu"

Captain Aryan yasaki wani irin tsaki,cikin 6acin rai yace"Ash...nifa yarinyar nan batada wani abu wanda zangani har inji sha'awarta"

Ashraf yabi Captain Aryan da kallon mamaki,to kodai saboda rashin zuwansa gida akai-akai shiyasa baisan yaya Mawahib din take ba? girgiza kansa yayi, da alama dan'uwan nasa baisan yarinyar ba.

Captain Aryan yace"kuma a'irin wannan yanayin nawa kwanaki wani me magani yakai office dinmu, a lokacin inajin kasala,bana yin gym kamar yanda nasaba"

Ashraf ya zauna abakin gadon nasu yaci gaba da shafa mai a jikinsa,shikuma Captain Aryan yana goge jikinsa da dan qaramin towel din hannunsa,cikin aji kamar bayaso yaci gaba da fadin"naji me maganin yana cewa da maiqo da zaqi da kasala duk maganin yana yi,to nima inajin kasala, sainayi tunanin nima irin nasu ne,nakar6a nasha,inashan maganin nan daga nan labari yafara sauyawa,nakifa kaina qasan table sai hada gumi nake,na riqe mara,da farko nafara jurewa, danaga abun bana qare bane ahaukace naje wajan mai magani najashi gefe,nafada masa abinda nakeji,shine yacemin ai yayi tunanin inada aure, maganin masu aure ne, yaje yanemo min wani abu kamar goro, nide ban tsaya na tantance menene ba nafara ci,shine naji dama dama..."

Ashraf ya kwashe da dariya,yace"tokaima kawai daga ganin suna shan magani kaima saika sha?"
Chapter 8 · 0% Book details