Sashe 2
Mawahib Complete Hausa Novel · about 8 min read
Badan tasoba tarufe Alqur'anin,tafice daga part din nasu zuwa babban kitchen din gidan,ta dauki abincin mama Sadiya tashiga part din tareda sallama,falon nasu yatsaru Iya tsaruwa da kujeru nasu launin dark green,babu tarkace sosai Bayan kayan kallo dayake falon, Kai tsaye ta wuce dinning dinsu ta ajiye abincin, sannan tashige dakin Nabiha,tana zuwa tazube akan gadon ta tace"sarkin danna waya,kina Nan kina sana'ar taki"
Nabiha tayi murmushi tace"to saina zauna shiru dan Allah? aigara indinga danna wayata"
Mawahib tace"hakane Kam,Nima yanzu tunda mungama exam ai yanzu zan maidata qawata"
Nabiha tace"Mawahib yaushe Yaya Ashraf zai dawo?"
Saida ta juya idanunta Mai kamadana Masu Jin bacci sannan tace"wallahi bansaniba Nabiha,jiyama bayan munfuto daga last paper nayi masa flashing, amma bai kirani ba,kikirashi mana idan magana zakuyi"
Ajiyar zuciya Nabiha tayi,cikin ranta tana jinjina maganar Mawahib datace ta kirashi,tayaya ne zata samu qwarin gwiwar kiransa bayan bataga fuskar hakan awajansa ba?
Cikin basarwa tace"to shikkenan,babu damuwa"
Cikin sauri Mawahib tatashi tace"bari inje inkaiwa Momy kilishi abincinta karnayi laifi"
Nabiha tace"wallahi kuwa,bare keda dama kamar qiris take jira"
Sallama tayi mata ta futo daga part din, takoma kitchen dinsu ta dauki abincin hajiya Kilishi sannan tawuce part dinta,gabanta yana tsinkewa.
Da'ita taci karo tana Bude kofar falon,qiris yarage subugi juna, cikin sauri Mawahib taja baya
Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"Ina ganin ikon Allah ni kilishi, ai saiki dinga nocking kafin kishigo, idan anbaki iznin shigowa saiki shigo tunda bakida iko da part din bare kidinga shigowa Kai tsaye haka"
Ahankali ta sunkuyar da kanta qasa cikin ladabi tace"kiyi haquri momy, dama abinci ne nakawo"
Batareda ta kar6i abincin ba tace"bude nagani"
Cikin nutsuwa ta sauke kwandon dake hannunta, sannan ta bubbude mata abincin,Nan da Nan qamshin girkin yacika wajan,abincin ya tsaru kana gani, kasan girki ne nazamani.
Yatsina fuska tayi tace"wanne irin gantalallen abinci ne haka zaki debo jiki kikawo min,?da alama kema haka zakije kinayi a gidan naki mijin....,kinga koma dashi kawai"
Babu musu Mawahib tarufe abincin sannan tadauko tanufi part dinsu dashi, tanajin yanda Hajiya kilishi take rufo qofar part din nata da qarfi.
Tana zuwa part dinsu dayake babu Nisa a tsakani, anan taci karo da Mamy tana zaune tana kallo,cikin mamaki mamy ta kalleta tace"yanaga kindawo da abincin?"
"Mamy nakai mata tace in dawo dashi"
Cikin yanayi na rashin damuwa Mamy tace"to Bari inkai mata dakaina"
Mamaki yacika Mawahib, babu musu tabata kwandon abincin, mamy ta karba tafice daga nasu part din tanufi part Hajiya Kilishi.
Tana zuwa tatura kofar falon tashiga bakinta dauke da sallama,falo ne har falo,yaji kayan qawata gida da lafiyaiyun kujeru milk color,tareda kafet Mai mutuqar laushi dawani daddadan qamshi dayake tashi gamida sanyin esi,can gefe inda dinning yake, anan ta hangi Hajiya Kilishi tana qoqarin hada tea, Kai tsaye ta nufi wajanta tace"yaya ga abincin angama, Mawahib tacemin kince adawo dashi, kiyi haquri Yaya yau dinne munsamu marasa lafiya a asbiti dayawa,Ina shirin tahowa aka kawo wata mata tana naquda,nice natsaya nakula da'ita harta haihu,sannan nataho gida shiyasa na Makara bandawo da wuri nayi abincin ba, amma kiyi haquri Yaya"
Hajiya Kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni Kilishi,nace kinyi wani laifi ne Maryam?kawai abincin naki ne yau bazanci ba,kinyi wata shinkafa haka a tsatstsaye bata dahuba,kiyi mana abincin da muka saba Namu na gargajiya kinqi, saina ki na Yan zamani, kega ma'aikaciya,wannan naman gandar daga ganinsa ko silala baiyi ba bare ayi batun dahuba"
Cikin ladabi tace"kiyi haquri Yaya, me kikeso nadafa miki yanzu?"
Hajiya Kilishi ba tace komai ba, tajuya tabar mamy a tsaye a wajan tashiga dakinta,mamy tasaki ajiyar zuciya ta wuce takai abincin dinning, sannan ta futo daga part din.
Tana komawa part dinsu taga Mawahib a zaune tanashan farfesun data gama a hankali cikin yanga kamar batason ci,Wanda a zahiri ba yanga takeba,haka cin abincin yake, hankalinta yana kan TV, tana ganin shigowar mamy, ta ajiye plate din dake hannun ta takoma kusa da ita ta zauna, ta dora hannayen ta akan cinyar mamy, sannan ta kalleta cikin damuwa tace"Mamy, Wai dan Allah meyasa Momy Kilishi bata sona?menayi mata Mamy?"
Cikin kwantar da hankali mamy taqarewa 'yartata kallo tana ganin tsantsar yanda take kama da mahaifinta, a hankali tace"tana sonki mana,itace tace miki bata sonki?"
"Mamy bata sona,dazu har cewa tayi wai itakam taga irin mijinda zan aura...,Mamy ahaka zamuci gaba da zama ne komai akai kinayin shiru?har cemin fa tayi wai nima ahaka zan qare danawa mijin idan nayi aure"
Cikin sauri mamy tace"insha Allahu ba'ahaka zaki qareba,mijinda zaki aura lafiya kalau zaki zauna, ba zakiyi irin wannan rayuwar ba"
Ahankali Mawahib tasaki ajiyar zuciya Jin furucin mahaifiyar tata,sannan tace"to Mamy meyasa ke bata sonki?"
"Wai waye yace miki bata sona? Kawai halintane haka, banason tambaya Mawahib,kitashi kije ki kwanta"
fan's ya kwana biyu?🤔
Amnah is back💃🏼
Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼
Zaki turo 500 ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034
Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034
Amnah El Yaqoub✍🏻
[7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗
(Hot luv)
Writing By Amnah El Yaqoub
3&4
Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin samun Audio Novel's👇🏻
https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels
____
Ba dabi'arta ce yin musu da mahaifiyar tata ba,danhaka babu musu tatashi ta dauke sauran farfesun datake ci takai d'an qaramin kitchen dinsu dake cikin falonsu,sannan ta futo tazo dining tazuba wata uwar madara a cup, tazuba ruwan zafi kad'an, tad'auki cornflakes d'in dake gefe tazuba acikin madarar, sannan ta wuce dakinta.
Mamy tana ganin shigarta daki tasaki ajiyar zuciya,yanzu har Mawahib yarinya 'yar shekara sha takwas tagane tsanar da Hajiya kilishi tayi mata harta fara sata agaba tana tambayarta dalili? Itakam meta tsarewa matar nan ne? aikin gomnatin datake ne yazama matsala? kokuma wannan ne sakayyar dazata mata bayan rainon yaranta datayi mata Abaya?
Labarinsu:
GIDAN ALQALI....,sunan da ake Kiran gidan dashi Kenan.
Duk unguwar inde kace gidan Alqali to kowa yasan cewa gidansu Mawahib ake nufi,Alqali mutun ne shi mai ra'ayi d'aya, baya magana biyu,yanada dattako,kowa nasa ne, yanada faram-faram da mutane,kowa shedar kirki yake masa,amma duk da wannan sakin fuskar tasa hakan bai hana yakasa gudanar da gidansa yanda yakeso ba,shine yake kafa doka agidan,duk abinda yabada umarni shi akebi,kasancewar shine babba a gidan,sai qannansa guda biyu Alhaji khaleed dakuma qaramin su Alhaji Isah.
Alqali fari ne tas,zaka Iya cewama ba bahaushe bane, amma bahaushe ne cikakke mutumin garin kano, yanada sauqin kai, kuma baya goyon bayan rashin adalci,tun yana qaramin ma'aikaci yake kokarin yin aikinsa da gaskiya da amanah,har Allah yabashi matsayin Alqali,wanda yazama abun koyi a wajan sauran Alqalai,babu ruwansa da kar6ar cin hanci, aiki kawai....🤗
su uku ne rak a wajan iyayensu wanda suka mutu suka bari,Alqali Ibrahim shine babba,da matarsa daya tun auren saurayi da budurwa wato HAJIYA KILISHI,lokacin da akayi auren sunsha surutun mutane ganinta fara tas kamar ba yar hausawa ba, shima kuma fari, wannan yace anhada kyau da kyau za'a ga irin yaran dazasu haifa,ire iren wannan surutun tun yana damunsu harya dawo yazame musu jiki, suna zaune lafiya tsawon wasu shekaru,Hajiya kilishi itace take kula da duka gidan zatayi girki Alhaji khaleed da Alhaji Isah zasuzo suci abincin su sutafi harkar gabansu.
Tsawon lokaci shiru shiru babu haihuwa, tun 'yan gulma suna saka ran ganin abinda zasu haifa har suka haqura, saida aka dauki wasu shekaru kafin ubangiji ya azurtasu da samun haihuwa, karon farko Hajiya kilishi ta haifi yaranta 'yanbiyu dukansu maza,lokacin da akayi haihuwar kai tsaye Alqali yace a dinga 6oye yaran,saboda Allah yayi musu kyau kamar 'ya'yan larabawa,Kuma bakin mutane wani bazai furta Alkhairi ba, sun dauki kyan uwa dakuma na uba sun hada waje daya, sunada mutuqar shiga rai babu wanda zai gansu baiji aransa yana qaunar yaran ba, ranar suna aka sakawa babban sunan mahaifinsu Alqali wanda yarasu,sai suke kiransa da ASHRAF,sai qaramin wanda aka sanya masa sunan mahaifin Hajiya Kilishi, suna kiransa da ARYAN....
Tun lokacin da kilishi ta haihu,take nan-nan da yaranta,kwata kwata batason abinda zai ta6a mata lafiyar 'yanbiyun ta, tanaji dasu kamar ranta,musanman ARYAN, wanda yaci sunan mahaifinta,ta dauki duk wani hope d'inta, ta dorashi akan ARYAN,idan har ta yiwa Alqali laifi to ta hanyar yaran yake hukuntata, saboda yariga yagano cewa yaran nata sune weakness dinta,tun suna zama Hajiya kilishi take gane-gane, yau taga maciji gobe kunama,idan d'aya yana kuka tad'aukeshi tana lallashinsa shima dayan saiya fara kuka,tarasa yanda zatayi ta lallashe su duka su biyun saboda haka saita ajiye d'aya idan d'ayan yayi shiru saita lallashi d'ayan,to duk ranar datayi hakan abincin gidan baya ciyuwa,haka zata dinga sakawa abinci wuta qarshe saide ayi asarar sa,data gane saitake had'asu duka su biyun take lallashin su,d'aya abaya,daya a hannu, daga lokacin bata sake ganin kunama ba,sai lokacin dasuke rarrafe idan sukai ta'adi tad'an dakasu alamun abinda sukai ba daidai bane,tana barin wajan taga wata baqar kunama,sai wata aminiyarta tabata shawara akar6o musu abincin maqota azuba musu akan murfin tukunya bazata sake ganin komai ba,haka akayi kuwa taje maqota takar6o abinci, tadauko murfin tukunya zata zuba musu Alqali yace karta fara, wannan duk canfi ne na mutane, Allah ne kawai yake kawo kunama amma ba yayansa ba,duk surutun mutane ne.
a hankali rayuwa taci gaba da tafiya 'yanbiyu suka fara tafiya har suna fita kofar gida wasa,ba'a Isa adakesu ba yanzu Hajiya kilishi zata sa6a mayafi koda sanin Alqali ko babu saninsa,zataje har gidan yaron daya dukar mata 'yanbiyu tarama musu, sannan takamo 'ya'yanta sudawo gida, wannan halaiyar kwata kwata Alqali bayajin dadinta.
Amma hajiya kilishi inde akan yaran nan ne, to zaka Iya Jin kanta dakowa, kasancewarta yar sarauta idan aka taba su Ashraf,mantawa take ita yar sarauta ce taje ayi wacce za'a yi,kokadan batason abinda zai ta6a mata lafiyar su,lokacin da aka haifeta, a lokacin a kayiwa mahaifinta sarauta, shiyasa mahaifinta ya Sanya mata suna KILISHI.
tashin datayi a gidan sarauta yasa take wa kowa kallon raini da Kuma nuna Isa da taqama da izza,kana ganin yanda take gudanar da al'amuranta zakasan cewa jinin sarauta yana yawo a jikinta,ahakan ma saboda Alqali a tsaye yake agidansa, shiyasa take rissinawa.
Nabiha tayi murmushi tace"to saina zauna shiru dan Allah? aigara indinga danna wayata"
Mawahib tace"hakane Kam,Nima yanzu tunda mungama exam ai yanzu zan maidata qawata"
Nabiha tace"Mawahib yaushe Yaya Ashraf zai dawo?"
Saida ta juya idanunta Mai kamadana Masu Jin bacci sannan tace"wallahi bansaniba Nabiha,jiyama bayan munfuto daga last paper nayi masa flashing, amma bai kirani ba,kikirashi mana idan magana zakuyi"
Ajiyar zuciya Nabiha tayi,cikin ranta tana jinjina maganar Mawahib datace ta kirashi,tayaya ne zata samu qwarin gwiwar kiransa bayan bataga fuskar hakan awajansa ba?
Cikin basarwa tace"to shikkenan,babu damuwa"
Cikin sauri Mawahib tatashi tace"bari inje inkaiwa Momy kilishi abincinta karnayi laifi"
Nabiha tace"wallahi kuwa,bare keda dama kamar qiris take jira"
Sallama tayi mata ta futo daga part din, takoma kitchen dinsu ta dauki abincin hajiya Kilishi sannan tawuce part dinta,gabanta yana tsinkewa.
Da'ita taci karo tana Bude kofar falon,qiris yarage subugi juna, cikin sauri Mawahib taja baya
Cikin 6acin rai Hajiya kilishi tace"Ina ganin ikon Allah ni kilishi, ai saiki dinga nocking kafin kishigo, idan anbaki iznin shigowa saiki shigo tunda bakida iko da part din bare kidinga shigowa Kai tsaye haka"
Ahankali ta sunkuyar da kanta qasa cikin ladabi tace"kiyi haquri momy, dama abinci ne nakawo"
Batareda ta kar6i abincin ba tace"bude nagani"
Cikin nutsuwa ta sauke kwandon dake hannunta, sannan ta bubbude mata abincin,Nan da Nan qamshin girkin yacika wajan,abincin ya tsaru kana gani, kasan girki ne nazamani.
Yatsina fuska tayi tace"wanne irin gantalallen abinci ne haka zaki debo jiki kikawo min,?da alama kema haka zakije kinayi a gidan naki mijin....,kinga koma dashi kawai"
Babu musu Mawahib tarufe abincin sannan tadauko tanufi part dinsu dashi, tanajin yanda Hajiya kilishi take rufo qofar part din nata da qarfi.
Tana zuwa part dinsu dayake babu Nisa a tsakani, anan taci karo da Mamy tana zaune tana kallo,cikin mamaki mamy ta kalleta tace"yanaga kindawo da abincin?"
"Mamy nakai mata tace in dawo dashi"
Cikin yanayi na rashin damuwa Mamy tace"to Bari inkai mata dakaina"
Mamaki yacika Mawahib, babu musu tabata kwandon abincin, mamy ta karba tafice daga nasu part din tanufi part Hajiya Kilishi.
Tana zuwa tatura kofar falon tashiga bakinta dauke da sallama,falo ne har falo,yaji kayan qawata gida da lafiyaiyun kujeru milk color,tareda kafet Mai mutuqar laushi dawani daddadan qamshi dayake tashi gamida sanyin esi,can gefe inda dinning yake, anan ta hangi Hajiya Kilishi tana qoqarin hada tea, Kai tsaye ta nufi wajanta tace"yaya ga abincin angama, Mawahib tacemin kince adawo dashi, kiyi haquri Yaya yau dinne munsamu marasa lafiya a asbiti dayawa,Ina shirin tahowa aka kawo wata mata tana naquda,nice natsaya nakula da'ita harta haihu,sannan nataho gida shiyasa na Makara bandawo da wuri nayi abincin ba, amma kiyi haquri Yaya"
Hajiya Kilishi tace"ina ganin ikon Allah ni Kilishi,nace kinyi wani laifi ne Maryam?kawai abincin naki ne yau bazanci ba,kinyi wata shinkafa haka a tsatstsaye bata dahuba,kiyi mana abincin da muka saba Namu na gargajiya kinqi, saina ki na Yan zamani, kega ma'aikaciya,wannan naman gandar daga ganinsa ko silala baiyi ba bare ayi batun dahuba"
Cikin ladabi tace"kiyi haquri Yaya, me kikeso nadafa miki yanzu?"
Hajiya Kilishi ba tace komai ba, tajuya tabar mamy a tsaye a wajan tashiga dakinta,mamy tasaki ajiyar zuciya ta wuce takai abincin dinning, sannan ta futo daga part din.
Tana komawa part dinsu taga Mawahib a zaune tanashan farfesun data gama a hankali cikin yanga kamar batason ci,Wanda a zahiri ba yanga takeba,haka cin abincin yake, hankalinta yana kan TV, tana ganin shigowar mamy, ta ajiye plate din dake hannun ta takoma kusa da ita ta zauna, ta dora hannayen ta akan cinyar mamy, sannan ta kalleta cikin damuwa tace"Mamy, Wai dan Allah meyasa Momy Kilishi bata sona?menayi mata Mamy?"
Cikin kwantar da hankali mamy taqarewa 'yartata kallo tana ganin tsantsar yanda take kama da mahaifinta, a hankali tace"tana sonki mana,itace tace miki bata sonki?"
"Mamy bata sona,dazu har cewa tayi wai itakam taga irin mijinda zan aura...,Mamy ahaka zamuci gaba da zama ne komai akai kinayin shiru?har cemin fa tayi wai nima ahaka zan qare danawa mijin idan nayi aure"
Cikin sauri mamy tace"insha Allahu ba'ahaka zaki qareba,mijinda zaki aura lafiya kalau zaki zauna, ba zakiyi irin wannan rayuwar ba"
Ahankali Mawahib tasaki ajiyar zuciya Jin furucin mahaifiyar tata,sannan tace"to Mamy meyasa ke bata sonki?"
"Wai waye yace miki bata sona? Kawai halintane haka, banason tambaya Mawahib,kitashi kije ki kwanta"
fan's ya kwana biyu?🤔
Amnah is back💃🏼
Mawahib littafin kudi ne,zaki biya naira 500 kacal,ki karanta abinki cikin kwanciyar hankali,sayan nagari maida kudi gida 💃🏼
Zaki turo 500 ta wannan account din
0164549488
Amina muhammad
GTbank
Kokuma katin MTN ta wannan number 08033300034
Tareda shedar biya ta wannan number 08033300034
Idan kina buqatar a tallata miki hajarki a Facebook page dinmu,da whtspp,da status,farkon shafi ko tsakiya,ko qarshan shafi, duka akan farashi me sauqi,ki tuntu6eni ta wannan number 08033300034
Amnah El Yaqoub✍🏻
[7/9, 9:20 AM] AMINA KABIR CAPS: 💗MAWAHIB💗
(Hot luv)
Writing By Amnah El Yaqoub
3&4
Please🙏🏻kuyi Subscribe YouTube Channel dina,domin samun Audio Novel's👇🏻
https://youtube.com/@Amnahelyaqoubnovels
____
Ba dabi'arta ce yin musu da mahaifiyar tata ba,danhaka babu musu tatashi ta dauke sauran farfesun datake ci takai d'an qaramin kitchen dinsu dake cikin falonsu,sannan ta futo tazo dining tazuba wata uwar madara a cup, tazuba ruwan zafi kad'an, tad'auki cornflakes d'in dake gefe tazuba acikin madarar, sannan ta wuce dakinta.
Mamy tana ganin shigarta daki tasaki ajiyar zuciya,yanzu har Mawahib yarinya 'yar shekara sha takwas tagane tsanar da Hajiya kilishi tayi mata harta fara sata agaba tana tambayarta dalili? Itakam meta tsarewa matar nan ne? aikin gomnatin datake ne yazama matsala? kokuma wannan ne sakayyar dazata mata bayan rainon yaranta datayi mata Abaya?
Labarinsu:
GIDAN ALQALI....,sunan da ake Kiran gidan dashi Kenan.
Duk unguwar inde kace gidan Alqali to kowa yasan cewa gidansu Mawahib ake nufi,Alqali mutun ne shi mai ra'ayi d'aya, baya magana biyu,yanada dattako,kowa nasa ne, yanada faram-faram da mutane,kowa shedar kirki yake masa,amma duk da wannan sakin fuskar tasa hakan bai hana yakasa gudanar da gidansa yanda yakeso ba,shine yake kafa doka agidan,duk abinda yabada umarni shi akebi,kasancewar shine babba a gidan,sai qannansa guda biyu Alhaji khaleed dakuma qaramin su Alhaji Isah.
Alqali fari ne tas,zaka Iya cewama ba bahaushe bane, amma bahaushe ne cikakke mutumin garin kano, yanada sauqin kai, kuma baya goyon bayan rashin adalci,tun yana qaramin ma'aikaci yake kokarin yin aikinsa da gaskiya da amanah,har Allah yabashi matsayin Alqali,wanda yazama abun koyi a wajan sauran Alqalai,babu ruwansa da kar6ar cin hanci, aiki kawai....🤗
su uku ne rak a wajan iyayensu wanda suka mutu suka bari,Alqali Ibrahim shine babba,da matarsa daya tun auren saurayi da budurwa wato HAJIYA KILISHI,lokacin da akayi auren sunsha surutun mutane ganinta fara tas kamar ba yar hausawa ba, shima kuma fari, wannan yace anhada kyau da kyau za'a ga irin yaran dazasu haifa,ire iren wannan surutun tun yana damunsu harya dawo yazame musu jiki, suna zaune lafiya tsawon wasu shekaru,Hajiya kilishi itace take kula da duka gidan zatayi girki Alhaji khaleed da Alhaji Isah zasuzo suci abincin su sutafi harkar gabansu.
Tsawon lokaci shiru shiru babu haihuwa, tun 'yan gulma suna saka ran ganin abinda zasu haifa har suka haqura, saida aka dauki wasu shekaru kafin ubangiji ya azurtasu da samun haihuwa, karon farko Hajiya kilishi ta haifi yaranta 'yanbiyu dukansu maza,lokacin da akayi haihuwar kai tsaye Alqali yace a dinga 6oye yaran,saboda Allah yayi musu kyau kamar 'ya'yan larabawa,Kuma bakin mutane wani bazai furta Alkhairi ba, sun dauki kyan uwa dakuma na uba sun hada waje daya, sunada mutuqar shiga rai babu wanda zai gansu baiji aransa yana qaunar yaran ba, ranar suna aka sakawa babban sunan mahaifinsu Alqali wanda yarasu,sai suke kiransa da ASHRAF,sai qaramin wanda aka sanya masa sunan mahaifin Hajiya Kilishi, suna kiransa da ARYAN....
Tun lokacin da kilishi ta haihu,take nan-nan da yaranta,kwata kwata batason abinda zai ta6a mata lafiyar 'yanbiyun ta, tanaji dasu kamar ranta,musanman ARYAN, wanda yaci sunan mahaifinta,ta dauki duk wani hope d'inta, ta dorashi akan ARYAN,idan har ta yiwa Alqali laifi to ta hanyar yaran yake hukuntata, saboda yariga yagano cewa yaran nata sune weakness dinta,tun suna zama Hajiya kilishi take gane-gane, yau taga maciji gobe kunama,idan d'aya yana kuka tad'aukeshi tana lallashinsa shima dayan saiya fara kuka,tarasa yanda zatayi ta lallashe su duka su biyun saboda haka saita ajiye d'aya idan d'ayan yayi shiru saita lallashi d'ayan,to duk ranar datayi hakan abincin gidan baya ciyuwa,haka zata dinga sakawa abinci wuta qarshe saide ayi asarar sa,data gane saitake had'asu duka su biyun take lallashin su,d'aya abaya,daya a hannu, daga lokacin bata sake ganin kunama ba,sai lokacin dasuke rarrafe idan sukai ta'adi tad'an dakasu alamun abinda sukai ba daidai bane,tana barin wajan taga wata baqar kunama,sai wata aminiyarta tabata shawara akar6o musu abincin maqota azuba musu akan murfin tukunya bazata sake ganin komai ba,haka akayi kuwa taje maqota takar6o abinci, tadauko murfin tukunya zata zuba musu Alqali yace karta fara, wannan duk canfi ne na mutane, Allah ne kawai yake kawo kunama amma ba yayansa ba,duk surutun mutane ne.
a hankali rayuwa taci gaba da tafiya 'yanbiyu suka fara tafiya har suna fita kofar gida wasa,ba'a Isa adakesu ba yanzu Hajiya kilishi zata sa6a mayafi koda sanin Alqali ko babu saninsa,zataje har gidan yaron daya dukar mata 'yanbiyu tarama musu, sannan takamo 'ya'yanta sudawo gida, wannan halaiyar kwata kwata Alqali bayajin dadinta.
Amma hajiya kilishi inde akan yaran nan ne, to zaka Iya Jin kanta dakowa, kasancewarta yar sarauta idan aka taba su Ashraf,mantawa take ita yar sarauta ce taje ayi wacce za'a yi,kokadan batason abinda zai ta6a mata lafiyar su,lokacin da aka haifeta, a lokacin a kayiwa mahaifinta sarauta, shiyasa mahaifinta ya Sanya mata suna KILISHI.
tashin datayi a gidan sarauta yasa take wa kowa kallon raini da Kuma nuna Isa da taqama da izza,kana ganin yanda take gudanar da al'amuranta zakasan cewa jinin sarauta yana yawo a jikinta,ahakan ma saboda Alqali a tsaye yake agidansa, shiyasa take rissinawa.