← Book details Mawahib Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 68

Sashe 53

Mawahib Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alqali ya kalli Ashraf yayi shiru,sai yanzu yagane dalilin dayasa jikinsa yayi sanyi lokacin da Aryan din yatafi, ashe su akwai abinda suka 6oye.

Yajuya ya kalli Mamy "waye yafada mata cewa antura shi yaqi?"

Mamy tace"Yaya wallahi bansani ba,ihun ta muka jiyo daga daki muna zuwa saitake fada mana, da alama awaya taji labarin"

Girgiza kansa yayi yace"insha Allahu zamuyi abinda yadace,ubangiji Allah yakare shi aduk inda yake"

Gaba dayansu suka amsa da "Amin"

Tun daga ranar Alqali da sauran qannansa suka yiwa limaman unguwar magana idan aka idar da kamsa salawat ake saka shi acikin kowacce Addu'ah.
Duk gidan kowa idonsa yanakan wayarsa ko zaiga kiran Captain kokuma saqon sa,tun suna zuba idon ganin wayarsa har tsoro yagama wanzuwa a zukatansu, ganin sati na hudu kenan ya shude babu labarin Captain, babu dalilinsa.

Mawahib duk ta rame sai fari kawai,hatta hips dinta saida suka ragu, haka breast dinta,idan tasaka riga da siket wanda abaya kamata yake, yanzu zuruf siket yake wucewa.
Mamy tana lura da'ita amma babu yanda zatayi da'ita kullum cikin haquri take bata,dakuma lallashi.

Idan ta tuna da maganganun daya fada mata adaren dasukai first night dinsu saide taji hawaye yazubo mata.
Acikin sati na biyar ne cikin dare tana bacci tafarka takasa komawa baccin, ahankali tatashi tafuto daga dakin ko tsoro bataji kai tsaye tawuce dakinsu Captain,dakin yana rufe tun ranar da Abba ya dauketa yakai ta part din Hajiya kilishi,tsaf dakin yake a gyare ,rigar jikinta tacire tabude kayansa ta dauki jallabiyarsa tasaka, Sanna ta kwanta akan gadon tareda rungume fillo tanajin kamar Yaya Captain ne,ta dade tana juyi tana tuno irin yanda ya sangartata da daddadar soyayyarsa, ahaka wani bacci me dadi ya dauketa.

Da asuba Mamy taga bata nan, taduba toilet dinta taga bata ciki,cikin sauri tafuto tazo dakinsu Captain anan taga Mawahib tana bacci cikin kwanciyar hankali jikinta Sanye da kayan Captain,murmushi tayi tarufe mata dakin ba tareda ta tashetaba saboda rashin isasshen bacci datake fama dashi.

Tun daga ranar tadena kwana a dakinta tadawo kwana dakinsu Captain,tun mutanan gidan basu ganeba har suka gane,wani lokacin ma da Hajiya kilishi da Mamy da Mama Sadiya idan suna compound din gidan a zaune a kujerun roba haka zatazo ta wuce su tashige dakin tayi kwanciyar ta,Hajiya kilishi saide tayi murmushi,tasan shima rasa kunyar dayana nan haka zai qetare su yashige dakin tunda harya Iya kasa haquri da jarabarsa ya lalla6a ya danne yarinya acikin gidansu.(🙊)

Haly JASHERU venture's,munada kayayyaki masu kyau da inganchi ba algus da ha'inci, kayanmu daga Ethiopian ne, prdct dinmu muna Ethiopian magic hair oil, anti dandruff shampoo serum, bdy cream, hand cream, magungunan chuttuka da na mata masu inganchi da qara lfy ajikin dan
adam ga number kmr hk 07046665338 ko 07061664264 munada distributor ako Ina afadin kasarnan da ketare muna koya harkokin kasuwnchinmu ga masu bukata akan 5000 kacal

sannan munada tsuntsaye na kasashen waje tattabaru game bukata ko koya akwai riba kwarai aharkar mebuqata yasiya koya koya seyanemeni a number na kamar haka 07046665338 ko 07061664264, ku antayo ayi tafiyar daku,yar'uwa kikoyi sana'ah akan wannan farashi me sauqi kema ki kafa kanki💃🏼

******

yauda tatashi da asuba tayi sallah adakin, komawa bacci tayi, bata tashi ba sai qarfe tara na safe,tashiga toilet din dakin tagyara shi,sannan tadawo dakin shima tafara share shi,wata takarda ta sharo aqasa gado ta tsaya da sharar ta duba taga kamar takardar Yaya Captain ce, tadora takardar akan gado, sannan taci gaba da shara saida tagama ta kunna turaren wuta adakin tajuya zata fita,ta hango wannan takardar data bari akan gado, tadawo ta dauketa tabude bedside drower zata sakata aciki,bindiga tagani aciki,ahankali ta tsugunna ta dauki bindigar tafara jujjuyata tana gani, bata ta6a riqe bindiga a hannunta ba sai yau, saide tahangeta daga nesa-nesa awajan Yaya Captain.

Ajiye bindigar tayi anan taga wata farar takarda da rubutu ajiki takardar tana bude ba'a ninke taba.
Zama tayi awajan tadauka tafara karantawa, tun lokacin da idonta yakai inda taga yasa RUQAYYA gabanta yafara faduwa.
Cikin sauri tafara karanta abinda ya rubuta "RUQAYYA kiyi haquri,antura ni yaqi zan maye gurbin Captain shu'aib,kiyi min Addu'ah,idan Allah yasa nadawo shikkenan, idan ban dawo ba kici gaba dayimin Addu'ah,naso ace nabarki har sai nadawo zuwa lokacin idan Addu'ah ta takar6u may be kinfara sona,to amma bazan iyaba...,inason koda sau daya ne nima na kasance da matata naji abinda sauran maza masu aure sukeji,ayau zan kar6i haqqina a wajanki,nadade inashan magungunan da likita yabani saboda matsalar rashin haihuwa ta, idan Allah yasa kafin nadawo kinsamu ciki idan namiji kika haifa asaka masa sunan ASHRAF,idan mace kika haifa asaka mata sunanki, saboda keda Ashraf kune mutum biyu danake so duk duniya sama da kowa bayan Momy na, kiyafemin..."

Yana kawowa nan rubutun yaqare,zuwa wannan lokacin da Mawahib take karanta wannan takardar, tuni takarda ta jiqe da hawaye.

Dama magungunan dataga yanasha na matsalar sane?
takardar ta cukwikwiye tarufe idonta da'ita tana wani irin kuka mecin rai,sosai take kuka kamar anyi mata albishir da mutuwa.
Mamy da taji shiru Mawahib batazo tayi breakfast ba tafuto zuwa dakin cikin damuwa,Hajiya kilishi data futo daga kitchen taga Mamy tana sauri zata wuce tace"maryam lafiya kuwa?"

Mamy ta kalleta"Yaya Mawahib ce naji shiru bata futo ba,har zan fita aiki banga tazo tayi breakfast ba,shine zan duba"

Cikin damuwa itama tace"muje,yarinyar nanfa saimun tashi tsaye akanta"

Suna zuwa dakin suka sameta tana rusa kuka,idanunta sunyi jajir,cikin sauri suka qarasa Hajiya kilishi ta zauna abakin gadon ita Kuma Mamy ta tsugunna taja Mawahib jikinta tana bubbuga bayanta alamun lallashi, cikin rawar murya kamar zata fashe da kuka itama Mamyn tace"kiyi haquri mana,Mawahib Addu'ah zaki masa ai"

Cikin kuka ta nunawa Mamy takardar tace"Mamy wasiyya ya barmin fa....,yanzu Ina shara nagani,dama yasan tafiya zaiyi yabarni bazai dawo ba meyasa bazai tafi dani ba?"
ta qarasa maganar idonta yana tsiyayar da hawaye.
Hawaye yazubo daga idon Mamy takasa cemata komai tadaiyi kokarin rungume ta ajikinta.
Hajiya kilishi ta dauki takardar ta karanta lokaci daya itama tafara kuka,tasaka gefen zaninta tana share hawayen,cikin kuka tace"kimasa Addu'ah Mawahib...."

daga haka takasa cewa komai tafuto daga dakin tana ruskar kuka.
Mamy da Mawahib kuwa sun dade adakin babu mai lallashin wani,sannan Mamy tasamu qwarin gwiwar goge hawayen ta takamo Mawahib din suka futo daga dakin.

Tundaga wannan ranar saiya kasance abincin ma tadaina ci,saide ruwan shayi,idan ta zauna ba zatayi magana ba saide tayi shiru tana tunani,har Mamy tafara tsoro kar cutar damuwa ta kamata.

Da daddare Mamy tahanata zuwa dakin Captain Aryan tadawo da'ita dakinta suna kwana tare,acikin kwanakin dasuke itada Mamy kullum basa bacci sai sun gabatar da nafila cikin dare sunyi addu'o'i sannan Mamy ta kwanta, Mawahib kuwa idonta biyu ras bata jin bacci,shiru take tana tuna irin rayuwar dasuke a Abuja itada Yaya Captain.
Har akira sallar asuba idonta biyu,gari yawaye amma ko gyangyadi batayi, Mamy data lura bata Iya bacci hakan yasa take yimata allurar bacci,shine zata dade tana bacci har asamu qwaqwalwar ta tahuta.

Hakan yasa washegari Mamy taje part din Hajiya kilishi,ta tarar har Alqali ma yana nan, bata 6oye musu komai ba akan matsalar Mawahib tafada musu komai,anan Alqali yace zaisa ayi mata rubutu ko Allahu zaisa tadawo hayyacinta takuma fauwalawa Allah komai, sannan yace Mamy ta matsa mata akan Addu'ah dakuma karatun qur'ani.

Mamy taji dadin maganganun Alqali,koba komai itama Hajiya kilishi asamu tadawo nata hayyacin, tunda daga ita har Mawahib din ansara gwara gwara a cikinsu.

Kwana biyu dayin wannan maganar Mamy tana zaune afalo itada Abba da Mawahib suna ganin labarai, Mawahib da Alqur'ani a hannunta tana karantawa,kwata kwata hankalinta baya kan abinda su Mamy suke gani,tana Sanye cikin hijab, Abba da Mamy kuma suna ganin Labaran, saide kowa yayi shiru da alama suma kawai kallon sukeyi gudun karsuyi tunani.

Ashraf da Hajiya kilishi da Alqali suka shigo falon,Mamy tayi musu sannu da zuwa, Mawahib ta Kalle su tace"ina kwananku?"

Alqali ya amsa mata cikin murmushi, zama sukai Alqali ya kalli Abba yabashi wata gora cikeda ruwan Addu'ah na rubutu yace"isah wannan na Ruqayya ne,ta dinga sha safe da yamma"

Cikin girmamawa Abba ya kar6a yace"to Yaya insha Allahu za'a bata,ai jikin nata naga da sauqi ma, tunda gatanan tadena zaman daki da'ita muke zama afalo saboda kada ta yawaita tunani..."

Kafin Alqali yayi magana gidan talavision din dasuke watso labari suka sako photunan wasu sojoji guda uku,cikon na hudun kuwa Yaya Captain ne,Mawahib da idonta yakai kan Sojojin nan tana ganin fuskar Yaya Captain ta ajiye qur'anin hannunta tazubawa tv ido gabanta yana faduwa,gaba daya suma su Alqali sai suka maida hankalin su kan labaran, inda me bada labarin yake cewa"rundunar Sojojin Nigeria wadda aka tura yaqi domin qwato dubban mutanan da yan ta'adda sukai garkuwa dasu sun samu nasara akan yan ta'addan inda suka qwato dukkan mutanan, sannan suka kashe mafi yawan yan ta'adda bisa jagorancin Captain Aryan I. Alqali,kada mutane su manta ba qaramin yaqi bane wannan, musanman dajin da wannan Yan ta'adda suke ciki,shide wannan daji ya kasance mafi munin daji acikin dajujjukan damuke dasu afadin qasar nan,tsawon wata uku kenan da'aka tura Captain Shu'aibu tareda rundunar sojin Nigeria,inda Allah yayi qarar kwanan sa a wannan daji, daga baya gwamnatin Nigeria tabada umarnin atura wasu Sojojin inda hukumar Sojan qasan Nigaria tatura mutane hudu,daga cikinsu akwai Captain Aryan I. Alqali, wanda muke samun labarin mutuwar sa yanzu haka daga majiya mai qarfi inda yasamu harbi agefen zuciyarsa, har yanzu de hukumar Sojojin Nigeria takafa ta tsare wajan ganin......"

Dif idanun Mawahib ya rufe tadena ganin komai sai duhu,ahankali Hajiya kilishi ta lumshe idonta tafara qoqarin maida qwallar dazata zubo mata,bataso kokadan tayi kuka,wani abu mai tauri yazo ya tsaya mata a maqoshi tana so taja numfashi amma takasa, saide har lokacin tahana kanta zubar da hawaye ko daya.

Ashraf yasaka hannu yagoge hawayen idonsa kansa aqasa ya gagara dagowa bare ya kalli fuskar dan'uwan nasa da'ake nunawa.

Alqali yatashi tsaye ya goge gumin fuskarsa ya kalli Abba da idanunsa sukai jajir yace"isah muje musamu khaleed saimu wuce Abujan"

Cikin sauri Abba yagyada kansa amma yakasa cewa komai saboda yana bude bakinsa kuka zai Iya qwace masa.

Shiru falon yayi bakajin motsin kowa sai kukan Mamy data kasa riqe kukanta ta sunkuya ta dora kanta akan hannun kujera tana kuka kamar ranta zai fita.
Chapter 53 · 0% Book details