← Book details Mawahib Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 68

Sashe 4

Mawahib Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sun kwashi watanni a wajan Mamy,yau suyi fad'a tadinga rabiya, gobe azauna kalau ahaka har sukayi mugun sabo da'ita, komai Mamy,bakajin komai a bakin su sai maganar Mamy, ta rainesu yanda ya kamata, raino wanda zaiyi wahala yaro ya manta da uwar rainon sa.

Ganin Alqali yayi mursisi baije bikon Hajiya kilishi ba, hakan yasa tadinga yiwa yan gidansu magana har sukuma suka yiwa Alhaji Khaleed da Alhaji Isah magana, suka basu haquri akan laifin kilishi suka roqesu Alfarmar suyiwa yayansu Alqali magana akan dawowar kilishi dakinta,domin sude bazasu Iya tunkarar sa da maganar ba, domin kuwa Alqali akwai kwarjini,hakan akayi kuwa, Alhaji Isa da Alhaji Khaleed sune suka shige gaba, aka maida auren Hajiya kilishi da Alqali Ibrahim,suka sake bawa yayan nasu haquri akan katsalandan din dasuka masa, badan Alqali yaso ba, haka yayi haquri kilishi ta dawo dakinta, bayan alqawari data dauka masa cewa hakan bazata sake faruwa ba.

Mamy kuwa tayi tunanin ganin hajiya Kilishi tadawo zaisa su Ashraf su koma wajanta, saitaga yara sunyi mursisi sunqi komawa wajan Hajiya kilishi,irin murnar nan ma taganin uwa sude ba suyi ba, saida Alhaji Isah yasata tahada musu kayansu sannan yace tarakasu wajan mahaifiyar su, a lokacin data gama hada musu kayan harda kukanta, a lokacin yarinta tasa basu fahimci kukan me takeba,Ashraf ne yafara matsowa yana goge mata hawayen,amma shikam Aryan da bai Iya lallashi ba shima saiya kwanta a cinyarta yafara kuka (😂)

Haka tarakasu wajan Hajiya kilishi, tayi mata sannu da zuwa ta amsa mata da qyar, itade Mamy ahaka ta futo tabarsu tareda mahaifiyar su.
Tunda Hajiya kilishi tadawo taji suna kiran Maryam da Mamy,babu 6ata lokaci tahanasu fadar sunan, saide suce Anty, sukuma basu saba da Anty ba, da Mamy suka saba, dan dolansu babu yanda suka Iya shine suke kiranta da Anty Mamy,maimakon suce Anty kadai,sai suka hada mata duka biyun suke kiranta da Anty Mamy

Bayan wasu shekaru suna kammala primary school dinsu Mama Sadiya ta haifi yarta mace, aka sanya mata sunan Mahaifiyar su Alqali, suna kiranta da NABIHA, adede lokacin Alqali yafitar dasu qasar waje karatu,saida karatun su yayi nisa sosai sannan Allah yabawa Mamy ciki,ta haifi yarta mace mai tsananin kyau kamar balarabiya,mahaifinta ya sanya mata suna RUQAYYA,Mamy kuma take kiranta da MAWAHIB.

ma'anah (MAI YAWAN KYAUTA).

Mawahib tun tana qaramarta Allah yayi mata diri,tanada jiki mai daukan hankalin samari, tanada sanyin hali kamar Mamy, kwata kwata batada hayaniya,Allah yayi mata baiwar hips kamar ita ta sakawa kanta,saide batada cikar qirji, boobs dinta ba manya bane kuma ba qananu bane, 'yan madedetane hakan ne yasa suke a tsaye qyam....
Mamy da Abbanta sunaji da'ita,sosai Mamy take siyo mata qananun kaya daga nashan is'ka harna bacci, haka zata saka kayan ta tayi uzurinta Iya part dinsu babu wanda yake mata magana, haka 6angaren kayan kwalliya ma ba'a barta abaya ba,idan Mawahib ta dauki kwalliya babu musu zakace mata yarinyar Momy da Daddy ce,saide bahaka bane,kawai Mamyntace ta tsaya mata take shigar ta yanda taga dama, tunda samarin gidan bawani zama suke ba.

Aqasar waje su Ashraf sukai secondary school dinsu,suka dora da jami'ah,bayan sungama jami'ah suka nunawa Alqali cewa suna so suzo gida, yace su dakata suyi masters tukunnah,duk tsawon wannan shekarun Mamy tana nan a ransu, tun basa fahimtar mahaifiyar su Hajiya kilishi bata son Mamy, har suka dawo suka gane,idan suka tambaye ta awaya Ina Mamy nan da nan Hajiya kilishi zatayi kicin kicin darai ta nuna musu batason mu'amularsu da wannan matar.

Haka sukai haquri basuzo gidaba saida suka kammala karatun su kamar yanda Alqali yakeso, sannan suka dawo gida, anan sukaga an sauya tsarin gidan, ansake masa fasali, anyi masa get biyu,gida yakoma gidan zamani ankashe masa dukiya, a wannan lokacin Alqali yayi ritaya,yana zaune agida yana hutawa,duk wani nauyin kula da gidan yakoma kan Alhaji Khaleed mahaifin Nabiha, saikuma Alhaji Isah mijin Mamy, gida de ya sauya, saide halin Yan gidan dabai canja ba(😂),tunda suka dawo Ashraf yaga Nabiha da Mawahib shikkenan yake jansu a jikinsa, musanman Mawahib din Mamy, yana bawa Mawahib kulawa yanda ya kamata, jinta yake aransa kamar me,duk abinda takeso nan da nan zakaga yaje yasiyo mata,amma kwata kwata baya bawa Nabiha wannan damar, tsakanin sa da'ita saide gaisuwa amma fuska asake yake amsawa, shikuwa gogan ko a jikinsa, daga Mawahib din,har Nabihan, gaba dayansu baya shiga sabgarsu, kwata kwata baya son raini, suma su Mawahib da sukasan halinsa koda wasa basa shiga harkar sa.

Bayan sunyi bautar qasa Ashraf yasamu aiki a NNPC dake Rivers state,shikuma Aryan dama burinsa yasamu aikin soja,kuma yasamu, har yakai matakin CAPTAIN,shiyasa su Mawahib suke kiransa da YAYA CAPTAIN, yana aikinsa a Abuja,bai cika zuwa gida sosai ba, Ashraf ya fishi zuwa gida.

Kamarsu daya da Ashraf sak,zaiyi wahala ka banbance su idan suka saka komai iri daya,suna fad'a ajunansu,saide fad'an nasu babu inda yake zuwa nan da nan zasu shirya, idan Ashraf yayi budurwa shima Aryan yana ganinta zaiji yana sonta, daga dawowar su daga qasar waje zuwa yanzu dasuke aiki Ashraf yayi 'yanmata dayawa, amma wai irin ya nunawa dan'uwansa sabuwar budurwar da yayi, sai shima Aryan din yace wallahi sonta yake (😲)

Babu yanda Ashraf zaiyi saide ya haqura da yarinyar tunda bazai iyu su auri mace daya ba, sunyi haka yakai sau biyar,kuma shima Ashraf din dan masifa kamar anyi masa dole muddin yasamu budurwa saiya nunawa Aryan ita,shikuma yana ganinta kai tsaye zai fada masa wallahi Shima yana sonta,haka Ashraf din zaiyi haquri yabar masa yarinyar kokuma su barta duka su biyun,shikuma captain Aryan baya kula yanmata bare ayi tunanin zai samo wata, yana zaune saide in dan'uwan yasamu, yace shifa duk duniya shima wannan yarinya yakeso,haka zasu haqura da yarinyar gaba dayansu.

Ashraf yanason ruwan zafi,halinsa sak irinna Alqali, shiyasa koda yaushe yake ta'ammali da tea,kuma babu ruwansa da zafin tea dinnan haka zaisha abunsa, amma captain Aryan bahaka bane, kokadan baya hada hanya da ruwan zafi, yafison ruwan sanyi, duk sanyin da ake agari bazaiyi wanka da ruwan zafi ba, dana sanyi zaiyi, wannan dabi'arsu ce tun suna Yara.

Har zuwa wannan lokacin Hajiya kilishi bataso su ra6i Mamy,amma har yanzu suna sonta,kuma suna mu'amula da'ita dan dole Hajiya kilishi ta haqura tabarsu.

Fatan Alqali da Hajiya kilishi shine su samu mata suyi aure, Hajiya kilishi ta dauki buri ta dorawa yanbiyunta kawai so take su samo mata yanmata nagani nafada na kece raini suyi aure irin auren 'ya'yan Masu dashi dakuma 'ya'yan masu mulki, amma har yanzu basu kawo kowacce yarinya gida ba,har gara Ashraf yana dan kula Mawahib,yana Jin dadi idan yaganta, yana sakata aiki kamar gyaran dakin su,girki marar wahala,yana wasa da dariya da'ita, amma baya kula Nabiha sosai, amma ita kullum tana tasa,bata da aiki sai tambayar Mawahib yaushe Yaya Ashraf zai dawo,? Sunyi waya da Yaya Ashraf?

Cigaban labari:

Dasafe Mamy tagama shirinta tsaf domin tafiya wajan aiki, tashiga dakin Mawahib taganta a kwance a gadon ta tayi d'aid'ai tana bacci,dogon gashin kanta duk ya barbaje akan katifar,tana sanye cikin wata yar 6ingilar rigar bacci gaba daya rigar iyakarta rabin cinyarta,hakanne yasa fararen cinyoyinta suka futo muraran,babu bra ajikinta amma yan madaidaitan boobs dinta suna nan a tsaye cak har kana Iya hango tsinin nipples dinta.

Mamy bata damu da kayan dayake jikin Mawahib ba, asalima itace take siyo mata su,tana duba agogon dake daure a hannun ta,mai mutuqar tsada, sannan tasaki dan qaramin tsaki tace"Mawahib tashi daga baccin nan haka, kina sana'ar taki ta bacci ko gidan baki gyaraba"

Cikin shagwaba tace"Mamy ramuwar baccin exam nake fa..."

"kitashi haka kiyi break fast kar yunwa ta kamaki,akwai kudi agefen gadona Abban ki yace ki dauka kije gyaran jiki,karki yarda kidawomin gida da wannan gashin naki babu gyara"

Idonta a lumshe tace"to Mamy saikin dawo"

Bayan Mamy tafita a hankali tazuro qafafunta qasa, tashafa shafaffan cikinta,sannan ta wuce toilet tayi brush, ta futo ta gyara musu part din nasu, ta kunna turaren wuta, ko'ina yadauki qamshi, sannan takoma daki tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga Abaya,wadda ta bude daga qasa, daga sama kuma ta fitar da shape din qirjin rigar, abincin tazuba tafara ci a hankali kamar bataso, adede lokacin Alhaji Isah Yafuto cikin shirin fita aiki,cikin sauri ta gaida shi, cikin mamaki yace"a a,karfe nawa yanzu baki tashi kinci abinciba sai yanzu kike break fast? meyake damunki ne Ruqayya? "

Saitayi wani sororo kamar bada ita yake magana ba,saboda ita kanta mantawa take Sunanta Ruqayya, saboda Mawahib din da'ake fada mata ya6oye Ruqayyan.

Cikin shagwaba tace"Abba bacci nakeji sosai shiyasa"

Kansa ya girgiza yace"kiyi sauri kifuto Ina jiranki saina saukeki kafin in wuce"

Bai jira amsar taba yawuce, cikin sauri tahada tea tasha, sannan tadauko hand bag dinta yar qarama mai kyau, tazuba kudin da Abban yabata, sannan ta futo, key tasa tarufe part din nasu, sannan ta wuce part din Hajiya Kilishi kamar yanda Mamy takafa mata doka kullum taje part din kowa ta gaishe su, tun kafin ta qarasa part din taji wani qamshi mai dadi ya bugi hancinta,a hankali ta lumshe Idonta, sannan ta bude, qamshin yayi mata dadi, cikin nutsuwa tatura kofar falon tashiga, dashi tafara yin tozali da alama saukar dare yayi, shiyasa batasan da zuwan sa ba,kyakykywan saurayi ne mai kyau da aji kana ganinsa kasan zaikai shekara 37,sumar kansa sai wani sheqi take,ga wani saje daya sake qawata farar fuskar sa,yanada dan qaramin lips launin ja.

tun kafin tagama qarasowa cikin falon Hajiya kilishi tafara watsa mata wani irin mummunan kallo,duk da tana shakkar Hajiya Kilishi, hakan baisa ta 6oye murmushin ganin Yaya Ashraf ba, cikin ladabi ta tsugunna tace"Momy Ina kwana?"

Daqyar Hajiya kilishi ta amsa,murya can ciki tace"lafiya..."
ta amsa tana qarewa surar jikinta kallo, shikuwa Ashraf kamar wanda tatafi da imanin sa tana shigowa haka yabita dawani irin mayen kallo,shi kansa baisan lokacin dayabita da wannan kallon ba,da alama yama manta da'inda yake zaune(😲)

Tun kafin Mawahib ta gaida Ashraf,Hajiya kilishi tace"Ina ganin ikon Allah ni kilishi.....ke Kuma irin tarbiyar da uwar taki take baki kenan? bazaki Iya jira akaiki gidan miji ba tun a titi zaki fara nunawa duniya jikinki? Kuma ahakan kuke neman miji nagari ko? banga sallaman man dazai kwasa ba...."(😢)

Cikin sauri Ashraf ya runtse idonsa,bayason wannan furucin datake yiwa Mawahib,bayajin dadinsa ko kadan.
Chapter 4 · 0% Book details