← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 112

Sashe 91

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A lokacin suka kai karshen gidan sai suka juyo suna retracing steps dinsu sai yace "sanda zaku taho Papa cewa yayi ku zauna a nan gidan, but sai na nuna masa cewa yayi nisa zaku ke shan wahalar transportation. But ni personally ba wai dan haka na samo muku wancan gidan ba, ni a ganina you are my responsibility kuma nan ba gida na bane ba bana son matar gidan ko sauran siblings dina suzo gidan suyi miki wani kallo, gwara can nawa ne babu mai daga miki kai" tayi murmushi tace "bansan sauran ba amma Murjanatu tana da kirki sosai" ya gyada kai yace "tana da kirki, suma duk basu da problem amma hausawa sunce maganin kar ayi kar a fara".

Sai da sukayi sallar isha sannan suka bar gidan. Zuciyoyin su tas kamar takarda. Suna zuwa gida sukayi wanka suka yi shirin kwanciya saboda duk sun gaji. Diyam ta kwanta tana bitar maganganun su da Sadauki. Yes, ta karbi shawarar Bassam, Sadauki baya son tana maganar Saghir dan haka ta daina amma bawai ta bar maganar bane ba, zata jira taga if he will come around and do the right thing da kansa.

Watarta tayi kara ta dauka tana murmushi. Bai gaji da hirar ba kenan. Ta dauka da sallama yace "so nake in taho nan kin yarda?" Tace "nan kuma? Me zaka yi anan din?" Yace "hira zan yi miki kadai" tace "to kayi min a wayar mana, ai ina jinka a haka" yace "nafi son inke ganin ki as ina miki maganar. Nafi son in yi miki joke kiyi min murmushi in gani. Nafi son in tsokane ki ki harare ni in gani. Nafi son in fada miki sweet sweet words inga kin rufe fuskarki kina jin kunyata" sai taja abin rufa ta rufe fuskarta. Tace "ni dai kar kazo zuwa zakayi kayi ta sakani jin kunya" sai kuma tace "amma bada gaske kake ba zancen daurin aure jibi ba ko?" Yace "in da zan samu yadda nake so da ko gobe nema ina so. But nasan ba zan samu ba, Papa zai ce abokansa da sauran mutanen sa, Mama zata ce zasuyi biki, and you, I want you to have all the wedding things da baki samu ba ada. So, I will wait. Kinsan ni am a patient bird. Yanzu ki gaya min duk abubuwan da kike so for the wedding" ta lumshe ido tana tunanin childhood dreams dinta, but those are only dreams kuma yanzu sun zama past, dan haka tace "ni bana son komai fa. Sai dai ko in kai kana son wani abu" yace "ni ke nake so. I want only you, and that's the only thing that matters" taji ta tamkar tana narkewa tana shigewa cikin katifar da take kwance. Is it possible to love someone this much?

Suka cigaba da hirarsu mai ratsa zuciya, tana bashi labarin makaranta da yadda tayi adapting, shima yana bata labarin lokacin da yake tasa makarantar. She told him about Bassam abinda ya hada su da yadda rayuwar su ta kasance tare but sai taki gaya masa cewa Bassam ya fara sonta. She told him yace ya taba ganinsa yaje daurin auren brother dinsa. Sai a lokacin yace "Abuja? Last year you said?" Tace "eh" ya danyi tunani yace "naje daurin auren gidan sarki. Maybe can yake". Sai da yaji alamar ta fara jin bacci sannan yace "kiyi addu'a ki rufe idonki. I will talk to you sai kinyi bacci saboda ina son kiyi mafarki na"

Took my hand, Touched my heart, Held me close. You were always there, By my side. Night and day, Through it all. Baby, come what may.
Swept away on a wave of emotion, Oh, we're caught in the eye of the storm. And whenever you smile, I can hardly believe that you're mine, Believe that you're mine.
This love is unbreakable. It's unmistakable. And each time I look in your eyes, I know why.This love is untouchable. A feeling my heart just can't deny. Each time I look in your eyes, Oh, baby, I know why This love is unbreakable.
Shared the laughter, Shared the tears. We both know We'll go on from here. 'Cause together we are strong. In my arms: That's where you belong.
I've been touched by the hands of an angel. I've been blessed by the power of love. And whenever you smile, I can hardly believe that you're mine.
This love is unbreakable. Through fire and flame. When all this is over, Our love still remains.
This love is unbreakable. (Lyrics by Westlife)
Washegari Sunday, Diyam tayi baccin safenta sosai sannan ta tashi. Tana mikewa ta jawo wayarta ta tura masa message cewa tana gayyatarsa breakfast. Ta fita ta tarar duk su Murjanatu suma babu wanda ya tashi dan haka ta zarce kitchen ta fara shirya abinci. Tana cikin aikin Judith ta shigo suka cigaba tare har suka kammala sannan ta tafi ta tashi Murjanatu ita kuma ta shiga tayi wanka ta shirya sannan suka fito kusan a tare da Murjanatu. A palo suka hadu suka baje kayan breakfast suna yi sai gashi ya shigo. Suka gaishe shi gaba-daya ya amsa da sakakkiyar fuska tana bude warmers din gurin. "Me aka shirya mana ne?" Murjanatu ta tashi tana serving dinsa yayinda Judith tayi musu sallama ta fita. Ya jingina da kujera yana shan tea yana kallon Diyam yace "kin yi kyau sosai" ta sunkuyar da kanta tace "thank you".

Ranar wuni sukayi tare, ya dauke su a motar Diyam suka fita yawon zaga gari. Sai dare suka gama suka dawo gida ya ajiye su shi kuma ya tafi da motar. A daren Diyam ta kira Inna dan rabon da suyi waya tun sanda ta kira ta suna tare da Bassam. Inna ta dauka suka gaisa suka kuma gaisa da Asma'u da Subay'a. Sannan Inna ta karba tace mata "ya bakon naku?" Diyam tace "lafiya lau Inna" Inna tace "ya gaya miki abinda yayi? Naji bakiyi mana magana ba" Diyam taji gabanta ya fadi, me kuma yayi? Sai ta dake tace "me yayi kuma Inna? Ni bai gaya min komai ba" Inna tace "nasan dama bai gaya miki ba, na dauka zai gaya miki yanzu da yazo. Ya kwashe dabbobin nan daga gidan Alhaji Babba ya mayar dasu bayan gari tun kusan sati biyu da suka wuce. An buge katangar tsakiyar gidan Alhaji yace ya bar masa gurin kyauta".

Ga breakfast, ayi enjoying tare da oga.
[3/17, 12:15 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Sixty Seven: The Inheritance

Diyam ta ajiye wayar tana tunani, sati biyu da suka wuce Inna tace anyi relocating gidan gonar, sati biyu da suka wuce lokacin Sadauki bai ma yi winning bet dinsu ba. This means yayi abinda yayi ne on his own account ba wai dan yayi winning bet din ba. Shin hakan yana nufin Saghir yana da hope?

Washegari Sadauki ya koma Nigeria. A airport Diyam ta marairaice masa kamar zatayi kuka shi kuma ya rikice. "Ki taho mu tafi. Sai ki dawo next week" tace "school kuma fa?" Yace "share school din nan, ai baku fara exams ba" sai ta tuna sanda yake hanata zuwa islamiyya, tace "so kake ayi min bulalar fashi ko?" Yace "waye zaiyi miki bulalar? Gaya min shi in fara yi masa tun kafin yayi miki" tayi dariya kawai tana tuno jibgar da ta sha a gurin Saghir, sai tace "ni yanzu mai duka na ai sai dai ruwan sama, ruwan saman ma sai na tsaya" yayi kasa da murya yace "in kin tsaya din ma I will shield you from it, like an umbrella" sai ta tuno sanda Inna ta kama su suna saukowa daga sama tazo zata dake su ya kare ta shi akayi ta dukan sa. He had been shielding her all his life. Ya katse mata tunanin ta ta hanyar langwabe kai yace "Please kizo mu tafi" ta makale kafada tace "naki, sai dai ka zauna anan" yace "ai kinsan maganar da zata mayar dani Nigeria. So nake fa ayi lokacin hutun ku sai mu dawo tare" ta rufe fuskarta da hannunta tana murmushi, sai kuma tace "Inna ta gaya min zancen Alhaji Babba. An gode madallah Allah ya kara arziki" yace "ameen" sai kuma ya dauke kansa gefe kamar yana tunani yace "ina yammatan gidan? Su Murja kawarki wadanda kika yi min maganar su rannan akan har yanzu basuyi aure ba?" Diyam tace "suna nan. Muna waya da Murja ma. Wani abin ne?" Yace "ya maganar auren nasu" tace "suna jira dai. Last wayar da muka yi tace min zata tura saurayinta gurin Baba Sa'idu (mijin anty Fatima)" yace "idan kun sake waya kice mata zakiyi musu kayan daki, ita da sisters dinta" ta bude baki tana kallon sa yace "ke ba yayarsu bace ba, ke zakiyi musu kayan daki ai" ya dauke kai yace "in place of their brother".

A kano bayan Sadauki yaje gurin Mama yaje ya gaya mata sun daidaita da Diyam, sai kuma ya nemi shawarar ta akan abinda ya dace yayi next. Sai ta nuna jin dadin ta sosai tace "ko ku fa, ai hakan yafi muku akan wannan zaman jiran da da kuka ce zaku yi" ya shafa kai yana murmushi. Tace "to yanzu abinda za'ayi shine zanje ni da kaina in samu Alhaji Babba, in yaso sai ya fadi ranar da za'a je a same su kai kuma sai ka fada a can gida sai su zo" yace "da nayi tunanin ko Kawu Isa, saboda kar a samu matsala da Alhaji Babba" Mama ta girgiza kai tace "babu matsala insha Allah. Shine Babba dan haka dole a bashi girman sa in ya karba shikenan in bai karba ba in yaso sai a je wani gurin a nema" suna cikin maganar sai Mukhtar yazo, suka yi hannu da Sadauki, Sadauki yace "ka yar dani Mukhtar, ko nema na bakayi" Mukhtar yayi dariya yace "ai ka zama yallabai ne yanzu, ka zama hukuma sai da lallashi" Sadauki yayi murmushi yace "sharri zaka yi min kenan ko? Zan samu time zaka ganni har gidanka".
Chapter 91 · 0% Book details