Sashe 16
Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yace "to Sadauki ne yace kike buya a sama?" Na gyada kaina, yace "kuma sai shima yake zuwa kuke zama tare a saman?" Na kuma cewa "eh" yace "to me kuke yi a saman?" Nace "games muke yi" yace "wanne irin game?" Nace "ko chess ko lido ko whot ko kuma...." Sai kuma nayi shiru, Yace "ko kuma me? Kinsan dai kinyi min alkawarin zaki gaya min gaskiya ko?" Nace "ko kuma muyi ta labari" yace "wanne irin labari?" Nace "ko ya bani labarin gareji ko makarantar su nima sai in bashi labarin makarantar mu da kawayena" yayi shiru yana jinjina kai sannan yace "to yanzu ina dankalinki da hijab dinki?" Na nuna sama da hannuna, yace "ya akayi kika cire su?" Nace "hijabin cirewa nayi dan kar yayi squeezing, dankwalin kuma bansan ya zame ba" yace "to me yasa kika sauko da gudu dazu, fada kukayi?" Na girgiza kaina sai kuma nayi murmushi ina tuno kalaman sadauki, Baffa ya sake maimaita tambayarsa yana nazarina, nace "na fada mukayi ba, kunyarsa nake ji shine na rufe idona shi kuma yace sai na bude masa yagani" Baffa ya dan bata fuska yace "me yasa kike jin kunyarsa?" Na dan rufe fuskata alamar kunya Nace "cewa yayi I am the only star in his sky" Baffa ya bude baki da mamaki yace "shi Sadaukin?" Na gyada kaina ina murmushi. Ya jima yana kallona sannan yace "to sai wanne wasan kuma kukeyi a saman?" Innocently na daga hannuna nace "shikenan" ya kuma yin shiru yana kallon na, sai kuma ya gyada kai yace "to yanzu kingakinyi wa innarki dani baffan ki laifi, an tura ki islamiyya kinki zuwa, me zaki ce mana?" Na durkusa a gabansa nace "Baffa kayi hakuri" ya kama hannuna yace "na hakura, saura Inna".
A zaune muka sameta, idonta akan tv amma daga gani ba kallon take yi ba, hallonta daya akan Asma'u tana shafa kanta a hankali ita kuma tana bacci. Na rakube daga bakin kofa ina kallonta, Baffa yaje ya zauna akan kujerar da take kusa da ita sannan ya kirawo ni da hannu yace "me kika cewa innarki?" Na durkusa nace "Inna kiyi hakuri, na tuba, bazan kara buya ba inkin kuma tura ni islamiyya" ta watsa min harara tace "kuma ba zaki kara kula Sadauki ba?" Na sunkuyar da kaina nayi shiru. Baffa yace "tashi ki tafi dakin ku ki kwanta" na tashi babu musu na shiga na kwanta, sai kawai naji ina tunanin koya Sadauki yake ji a jikinsa? Dan nasan ba karamin dokuwa yayi a gurin Inna ba.
A palo bayan na wuce Inna tace "shikenan? Shikenan maganar nan ta wuce? Shikenan ba zaka dauki mataki akan yaron nan da yake neman ya lalata maka yarinya ba?" Baffa yace "nayi magana da Diyam, abinda kike tunani ba haka bane ba. Tabbas shi ya hanata zuwa makaranta saboda wai ance za'a dake ta in taje akan laifin da shine ya aikata ba ita ba. Tabbas Sadauki yayi laifi kuma zan zauna inyi magana dashi kamar yadda nayi da Diyam. Zan fahimci inda yake da kuskure in nusar dashi, inda kuma yayi laifi inyi masa fada" hawaye ya zubo daga idon inna tace "shikenan abinda zakayi masa?" Yace "to gaya min me kike so inyi masa?" Tace "ka mayar dashi gidan ubansa tun kafin yalalata mana yarinya ya cuce mu" ya girgiza kansa yace "Sadauki ba zai lalata Diyam ba, in ma hakan ta faru to mune zamu kasance masu laifi fiye dashi. Yanzu in tambayeki? Me yasa da Diyam ta gudo daga makaranta batazo gurinki a matsayin ki na mahaifiyarta ba sai ta tafi gurin Sadauki?" Da sauri inna tace"saboda ya cinye kurwarta bata ganin kan kowa da gashi sai nashi" Baffa ya girgiza kai yace "saboda a gurinsa take ganin zata samu maslaha in ta zo gurinki problem zata karawa kanta. Yarinyar nan dududu shekarunta goma da watanni a duniya, yanzu ne ya kamata ace kin kara jawo ta jikin ki kin koyar da ita lamurran duniya, amma me? Diyam tsoron ki take ji, komai tayi gani takeyi kamar laifi zatayi a gurinki. Yanzu da ace ma lalata tan yakeyi kamar yadda kika yi tunani ta yaya zaki sani? Kince ba kya son taje dakin Zainab, amma ke kin gaza yi mata abinda Zainab din take yi mata har take nacin zuwa dakin nata, wasa da dariya, kulawa, nuna soyayya, wannan shine kadai abinda Diyam take bukata daga gurinki a wannan lokacin. Ke kika haife ta, dan haka in kika sakar mata fuska zakiyi mamakin yadda zata sake dake itama".
Inna ta kalleshi tace "dama na sani, nasan duk yadda zakayi ka juya maganar nan ta koma kamar laifina ce sai kayi, ni kumana riga na sani, nasan cewa kafi son Sadauki akan Diyam, kafi son agola akan yar data fito daga jikin ka, kamar yadda ka fi son zainabu akai na ni uwargidan ka kuma yar uwarka ta jin, kuma uwar yayanka na gaskiyai" Baffa ya mike tsaye yana girgiza kai yace "Diyam ni na haifeta, Sadauki kuma nina rike shi tun yana cikin tsumman sa dan haka dukkan su yaya nane, babu banbanci. Maganar tsakanin ki da Zainab kuma ke kike ganin haka, ke kika saka haka a ranki. Amma ina son ki bude idonki ki kalli gabanki sosai zaki fahimci ke kadai kike fadanki babu wanda yake amsa miki"
Har ya kai bakin kofa tace "ina neman alfarma guda daya a gurinka" ya juyo amma bai ce komai ba, tace "ina son idan har Diyam ta kammala primary a kaita boarding school" yace "Allah ya nuna mana lokacin".
Writing......
[1/14, 8:43 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â¤ï¸ DIYAM â¤ï¸
By
Maman Maama
Episode Sixteen: My Love
Washegari Baffa da kansa ya tisa keyar mu daga ni har Sadauki muka je islamiyya, ya saka muka bada hakuri sannan shima ya bayar, ya kuma ce duk sanda wani abu makamancin wannan ya sake faruwa su sanar dashi shi kuma zai dauki mataki akan mu. A take kuma yayi Asma'u register ya ce kullum tare zamu ke zuwa da ita . Wannan ya kawo karshen gudun islamiyya ta amma kuma ya kawa hauhawar kiyayyar Sadauki a gurin Inna, yanzu yakasance ko gaisheta yayi bata amsawa shi kuma bai fasa gaishetan ba kullum. Takance "shegen naci irin na uwa, kamar tsohon maye".
A karshen term din muka rubuta jarabawar common entrance. A lokacin shi kuma Sadauki ya rubuta jarabawar shiga ss3, qualifying exam, kuma dukkanin mu munyi nasara. Naci makarantar day science ta nan garin kano. Ina karbowa na taho gida da murnata na kuma yi sa'a Baffa yana gida, suna palon sa shida Sadauki suna lissafe lissfen da suka shafi gareji. Na durkusa na gaishe shi sannan namika masa takardar, ya karba ya karanta yana murmushi yace "very good Inno. Kinyi kokari sosai Allah yasa albarka a cikin karatun ki" nace "ameen Baffa" yace "sai dai ba day science zaki tafi ba, nayi magana da wani abokina wanda yake malami ne makarantar kwana ta yammata dake garin Taura a jahar Jigawa, yace in kaiki zasuyi miki interview in kinci sai a kaiki can" na taba rai cike da confusion nace "taura? Gari ne haka din? Makarantar kwana?" Sai na juya na kalli Sadauki wanda shima Baffa yake kallo yace "Baffa boarding fa kace, Diyam? Baffa Diyam bata da girma manyan dalibai zasu ke cin zalinta kuma...." Sai ya hadiye sauran maganar saboda kallon da Baffa yayi masa, Baffa ya miko min takardar yace "ki kaiwa innarki ta adana miki, gobe da safe ki shirya zamuje kiyi interview din" na karba jikina a sanyaye na wuce dakin inna. Na kai mata ta bude tana gani fuskarta da murmushi duk kuwa da cewa ba wai sanin abinda aka rubuta tayi ba. Na zauna a kusa da ita nace "Inna naci day science, makarantar su Rumaisa" ta ninke takardar ta ajiye tace "Rumaisa ai jeka ka dawo take yi, ke kuma makarantar kwana zakiyi" na fara hawaye nace "Inna Baffa yace wai gobe za'a kaini a gwada ni, inna ni bana son zuwa dan Allah kiyi masa magana kar a kaini" tana kallona tace "saboda me?" Na rike hannunta nace "bana son barin gida Inna bana son rabuwa daku" sai ta zame hannunta daga nawa tace "ko dai bakya son rabuwa Sadauki? Ni kuma saboda shime nake son akaiki makarantar kwanan ko hankalina ya kwanta, kuma idan ba kya ganinsa a hankali zaki manta dashi. Kafin Allah ya taimake mu ya tattara ya koma gidan ubansa" jin haka yasa na fahimci bani da hope a gurin Inna, ba zata rokar min Baffa ya fasa kaini boarding ba.
Dakin Ummah na tafi ina sharar kwalla, ta rike ni tana tambayata, "Diyam lafiya? Wani abu ne yake yi miki ciwo?" Na zauna ina kara sautin kukana nace "Ummah wai boarding za'a kaini inji Baffa, dan Allah Ummah ki bawa Baffa hakuri" tayi ajjiyar zuciya tace "Diyam, ai ba laifi kikayi masa ba ballantana in bashi hakuri, zai kaiki boarding ne saboda yana ganin hakan shi yafi dacewa dake" nace "to ni yanzu Ummah me zanyi? Me zanyi ya fasa kaini?" Tana shafa kaina tace "kiyi addu'a, kiyi fatan Allah ya sa hakan shi yafi miki alkhairi"
A zaune muka sameta, idonta akan tv amma daga gani ba kallon take yi ba, hallonta daya akan Asma'u tana shafa kanta a hankali ita kuma tana bacci. Na rakube daga bakin kofa ina kallonta, Baffa yaje ya zauna akan kujerar da take kusa da ita sannan ya kirawo ni da hannu yace "me kika cewa innarki?" Na durkusa nace "Inna kiyi hakuri, na tuba, bazan kara buya ba inkin kuma tura ni islamiyya" ta watsa min harara tace "kuma ba zaki kara kula Sadauki ba?" Na sunkuyar da kaina nayi shiru. Baffa yace "tashi ki tafi dakin ku ki kwanta" na tashi babu musu na shiga na kwanta, sai kawai naji ina tunanin koya Sadauki yake ji a jikinsa? Dan nasan ba karamin dokuwa yayi a gurin Inna ba.
A palo bayan na wuce Inna tace "shikenan? Shikenan maganar nan ta wuce? Shikenan ba zaka dauki mataki akan yaron nan da yake neman ya lalata maka yarinya ba?" Baffa yace "nayi magana da Diyam, abinda kike tunani ba haka bane ba. Tabbas shi ya hanata zuwa makaranta saboda wai ance za'a dake ta in taje akan laifin da shine ya aikata ba ita ba. Tabbas Sadauki yayi laifi kuma zan zauna inyi magana dashi kamar yadda nayi da Diyam. Zan fahimci inda yake da kuskure in nusar dashi, inda kuma yayi laifi inyi masa fada" hawaye ya zubo daga idon inna tace "shikenan abinda zakayi masa?" Yace "to gaya min me kike so inyi masa?" Tace "ka mayar dashi gidan ubansa tun kafin yalalata mana yarinya ya cuce mu" ya girgiza kansa yace "Sadauki ba zai lalata Diyam ba, in ma hakan ta faru to mune zamu kasance masu laifi fiye dashi. Yanzu in tambayeki? Me yasa da Diyam ta gudo daga makaranta batazo gurinki a matsayin ki na mahaifiyarta ba sai ta tafi gurin Sadauki?" Da sauri inna tace"saboda ya cinye kurwarta bata ganin kan kowa da gashi sai nashi" Baffa ya girgiza kai yace "saboda a gurinsa take ganin zata samu maslaha in ta zo gurinki problem zata karawa kanta. Yarinyar nan dududu shekarunta goma da watanni a duniya, yanzu ne ya kamata ace kin kara jawo ta jikin ki kin koyar da ita lamurran duniya, amma me? Diyam tsoron ki take ji, komai tayi gani takeyi kamar laifi zatayi a gurinki. Yanzu da ace ma lalata tan yakeyi kamar yadda kika yi tunani ta yaya zaki sani? Kince ba kya son taje dakin Zainab, amma ke kin gaza yi mata abinda Zainab din take yi mata har take nacin zuwa dakin nata, wasa da dariya, kulawa, nuna soyayya, wannan shine kadai abinda Diyam take bukata daga gurinki a wannan lokacin. Ke kika haife ta, dan haka in kika sakar mata fuska zakiyi mamakin yadda zata sake dake itama".
Inna ta kalleshi tace "dama na sani, nasan duk yadda zakayi ka juya maganar nan ta koma kamar laifina ce sai kayi, ni kumana riga na sani, nasan cewa kafi son Sadauki akan Diyam, kafi son agola akan yar data fito daga jikin ka, kamar yadda ka fi son zainabu akai na ni uwargidan ka kuma yar uwarka ta jin, kuma uwar yayanka na gaskiyai" Baffa ya mike tsaye yana girgiza kai yace "Diyam ni na haifeta, Sadauki kuma nina rike shi tun yana cikin tsumman sa dan haka dukkan su yaya nane, babu banbanci. Maganar tsakanin ki da Zainab kuma ke kike ganin haka, ke kika saka haka a ranki. Amma ina son ki bude idonki ki kalli gabanki sosai zaki fahimci ke kadai kike fadanki babu wanda yake amsa miki"
Har ya kai bakin kofa tace "ina neman alfarma guda daya a gurinka" ya juyo amma bai ce komai ba, tace "ina son idan har Diyam ta kammala primary a kaita boarding school" yace "Allah ya nuna mana lokacin".
Writing......
[1/14, 8:43 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â¤ï¸ DIYAM â¤ï¸
By
Maman Maama
Episode Sixteen: My Love
Washegari Baffa da kansa ya tisa keyar mu daga ni har Sadauki muka je islamiyya, ya saka muka bada hakuri sannan shima ya bayar, ya kuma ce duk sanda wani abu makamancin wannan ya sake faruwa su sanar dashi shi kuma zai dauki mataki akan mu. A take kuma yayi Asma'u register ya ce kullum tare zamu ke zuwa da ita . Wannan ya kawo karshen gudun islamiyya ta amma kuma ya kawa hauhawar kiyayyar Sadauki a gurin Inna, yanzu yakasance ko gaisheta yayi bata amsawa shi kuma bai fasa gaishetan ba kullum. Takance "shegen naci irin na uwa, kamar tsohon maye".
A karshen term din muka rubuta jarabawar common entrance. A lokacin shi kuma Sadauki ya rubuta jarabawar shiga ss3, qualifying exam, kuma dukkanin mu munyi nasara. Naci makarantar day science ta nan garin kano. Ina karbowa na taho gida da murnata na kuma yi sa'a Baffa yana gida, suna palon sa shida Sadauki suna lissafe lissfen da suka shafi gareji. Na durkusa na gaishe shi sannan namika masa takardar, ya karba ya karanta yana murmushi yace "very good Inno. Kinyi kokari sosai Allah yasa albarka a cikin karatun ki" nace "ameen Baffa" yace "sai dai ba day science zaki tafi ba, nayi magana da wani abokina wanda yake malami ne makarantar kwana ta yammata dake garin Taura a jahar Jigawa, yace in kaiki zasuyi miki interview in kinci sai a kaiki can" na taba rai cike da confusion nace "taura? Gari ne haka din? Makarantar kwana?" Sai na juya na kalli Sadauki wanda shima Baffa yake kallo yace "Baffa boarding fa kace, Diyam? Baffa Diyam bata da girma manyan dalibai zasu ke cin zalinta kuma...." Sai ya hadiye sauran maganar saboda kallon da Baffa yayi masa, Baffa ya miko min takardar yace "ki kaiwa innarki ta adana miki, gobe da safe ki shirya zamuje kiyi interview din" na karba jikina a sanyaye na wuce dakin inna. Na kai mata ta bude tana gani fuskarta da murmushi duk kuwa da cewa ba wai sanin abinda aka rubuta tayi ba. Na zauna a kusa da ita nace "Inna naci day science, makarantar su Rumaisa" ta ninke takardar ta ajiye tace "Rumaisa ai jeka ka dawo take yi, ke kuma makarantar kwana zakiyi" na fara hawaye nace "Inna Baffa yace wai gobe za'a kaini a gwada ni, inna ni bana son zuwa dan Allah kiyi masa magana kar a kaini" tana kallona tace "saboda me?" Na rike hannunta nace "bana son barin gida Inna bana son rabuwa daku" sai ta zame hannunta daga nawa tace "ko dai bakya son rabuwa Sadauki? Ni kuma saboda shime nake son akaiki makarantar kwanan ko hankalina ya kwanta, kuma idan ba kya ganinsa a hankali zaki manta dashi. Kafin Allah ya taimake mu ya tattara ya koma gidan ubansa" jin haka yasa na fahimci bani da hope a gurin Inna, ba zata rokar min Baffa ya fasa kaini boarding ba.
Dakin Ummah na tafi ina sharar kwalla, ta rike ni tana tambayata, "Diyam lafiya? Wani abu ne yake yi miki ciwo?" Na zauna ina kara sautin kukana nace "Ummah wai boarding za'a kaini inji Baffa, dan Allah Ummah ki bawa Baffa hakuri" tayi ajjiyar zuciya tace "Diyam, ai ba laifi kikayi masa ba ballantana in bashi hakuri, zai kaiki boarding ne saboda yana ganin hakan shi yafi dacewa dake" nace "to ni yanzu Ummah me zanyi? Me zanyi ya fasa kaini?" Tana shafa kaina tace "kiyi addu'a, kiyi fatan Allah ya sa hakan shi yafi miki alkhairi"