← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 112

Sashe 6

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Lecturer yana fita ya juyo gaba-daya gurinta yace "so, miss Nigeria, you are from Yobe state, right?" Ta dan bata rai tana kallonsa tace "Yobe kuma?" Yace "eh, rannan kince min sunan ki Haleema Usman Kollere, and I know Kollere is in damagum local government, yobe state" tayi dariya tana rike baki tace "you are amazing" yayi murmushi proudly yace "I know my geography" ta mike tsaye tana zuba kayanta a jaka, shima ya mike, tace "You surely do, but I am not from Yobe. Kamar yadda na fada ranar nan ni yar kano ce, yes, my grandparents na uwa da uba duk fulanin Kollere ne amma ni a kano aka haifeni, kano ne a birth certificate dina dan haka kano nake amfani dashi" suka jera suna fita daga ajin tace "so you are from Abuja, where in Abuja are you from?" Yace "somewhere" ta tsaya a waje tana kallonsa tace "wayo ko? Wato ni na bude baki na gaya maka daga inda nake shine kai kuma zaka wani ce min somewhere ko?" Yace "a,a ke fa kawai kince min ke yar kano ce, kano ai tana da girma" direct tace masa "Municipal. Yakasai. Kai fa?" Ya sosa kai yana kallonta, taga bashi da niyyar fada tayi gaba tace "ohhh, I hate stingy people" ya biyo ta da sauri yace "I don't want to lie to you, kinfi karfin haka. And I also don't want to tell you yet" tace "saboda me?" Ya sake yin shiru. Ta karkata kai tana kallonsa tace "someone as shiny as you must have come from the Villa, not less" yayi dariya yace "You are wrong, ko kusa da Villa ban kai ba" tace "where then?" Ya kalli surrounding din gurin yace "ina zamuje ne naga mun fito waje" ta gane so yake ya chanja maganar tace "cafeteria, yunwa nake ji, I over slept har na makara kuma munyi fada da Murjanatu taki tashina" yayi dariya yace "me ya hadaku?" Tace "girl's stuff, you won't understand" ya rungume hannunsa a kirji yana kallonta yace "stingy, are we?" Tayi dariya tace "ba zaka gane ba fa" yace "okay, let's go. Nima banyi breakfast ba".

Shi yayi musu order abinci, bacon and eggs, da coffee. Suka fara ci sannan yace "so, how did a Fulani girl daga rugar Kollere ta samu kanta a Oxford?" Ba tare data kalleshi ba tace "luck" yace "hmmm?" ta ajiye chokalin hannunta tana kallonsa tace "you talk about kaddara ranar nan ko? To ita ta kawo ni nan, I was destined to be here and here I am. How about you? How did a guy from somewhere in Abuja find himself here" shima yace "luck" ta daga gira daya sama tana kallonsa sannan yace "okay, I was lucky to be born into a wealthy family" tayi murmushi tace "Villa?" Yace "definitely not" sukayi dariya baki daya.

Ranar kusan tare sukayi komai, har suka tashi daga school suka kuma tafi tare, sai daya rakata har bakin block dinsu sannan yayi mata sallama ya tare cab zuwa gurin aikinsa. Yana jin zuciyarsa fari kal kamar takarda, duk wani bacin rai da stress duk ya gushe daga ransa. He is finally finding happiness.

Diyam kuma tana shiga parlon su ta yarda jakarta ta kwanta ta lumshe ido, tana jin Judith ta shigo parlon tana yi mata magana amma sai tayi pretending kamar bacci take yi nan kuwa idonta biyu, lissafi kawai take yi a ranta. Most of the time shi yasa tafi son zaman makaranta saboda in tana can tana mantawa ne da duk wasu problems dinta amma tana zuwa gida sai taji kamar damuwowinta jiranta suke yi a bakin kofa. Jiya da daddare sukayi rigima da Murjanatu, kuma ita tasan Murjanatu gaskiya take gaya mata, tasan yaudarar kanta kawai take yi taki admitting hakan. Ta dauko wayarta tana kallon hoton dake kan screen din tana murmushi, sai kuma ta shiga cikin ta fara kallon pictures tana ta dariya ita kadai. She missed Nigeria sosai, but wannan zaman da take, wannan karatun da take, shine kadai solution dinta a yanzu. Me yasa mutane including Murjanatu suka kasa fahimtar hakan?

Sai bayan la'asar Murjanatu ta dawo. Kafin nan Diyam ta shirya musu pasta saboda tasan Murjanatu tana so duk dan su shirya. Tana shigowa kallo daya tayi wa Diyam ta kara tura baki gaba ta wuce daki, sai da tayi wanka ta shirya cikin riga da wando budaddu kalar ruwan toka da suka kara wa bakar fatar ta kyau sannan ta dawo parlon ta tsaya ta rike kugu tace "shine kika taho kika barni ko? Kuma na tambaya ance min tare da wannan tsinannen Bassam din kuka taho" Diyam ta mike zaune tace "ayyah Fanna, karki tsine masa, kinsan bakin ku dafi ne dashi, kar kisa ya tambade shi da baiyi miki komai ba" Murjanatu ta zauna ta dora daya kan daya tace "tunda yake kula matar yayana ai yayi min laifi, kuma wallahi daga ke har shi ku shiga hankalinku idan ba haka ba yana zuwa next week sai na gaya masa, kuma kunsan sauran" Diyam tace "oh oh, to gaya masan mana, an gaya miki kowama tsoronsa yakeji kamar ke, ni kinsan daga ke harshi dai dai nake daku. Naci nasha tsumin fulani barebari sai dai su ganni su barni" nan kuma suka koma wasan fulani da barebari, sannan suka ci abincinsu tamkar ba sune jiya suka yi fada ba.
[1/6, 10:32 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Seven : The Phone Call

Tun daga ranar Diyam da Bassam suka hade, kullum a school suna tare duk ya daina kula friends dinsa ita kuma dama bata dasu, daga school kuma zai wuce gurin aikinsa, anan zai samu kudin kashewa gobe. Sosai yake jin dadinsa hankalinsa kwance as if bashi da wani problem.

Ranar Thursday suna lunch a cafeteria kamar kullum, Diyam ta tambaye shi "can you tell me about that not laughing situation da kace kana ciki? Because I can see yanzu kana dariyar" dariyar yayi sannan kuma ya hade rai yana jujjuya abincin gabansa yace "I got fired" ta zaro ido tana mamaki, fuskanta cike da concern tace "daga gurin aikinka? When?" Yace "no, ba daga gurin aikina ba, I got fired from my family" ta hade rai tace "your family? Ta yaya za'ayi familyn mutum su kore shi? Me kayi Bassam? What happened?" muryarta tana breaking kamar zata yi kuka ta tambaye shi, ba tare daya kalleta ba yace "nayi laifi, babban laifi, maimakon in tsaya in fuskanci hukunci na kuma sai na gudu na kama daki a hotel nayi zamana. When I did that na saka ran kwana biyu ba zasu wuce ba mami na da Daddy na zasu zo kasar nan, nayi tsammanin zasu zo har dakin da nake, nayi tsammanin karbar wadansu kyawawan mari daga Daddy na kuma yi tsammanin in samu nasiha daga mami amma shiru, basu zo ba ballantana su fada min cewa nayi ba dai dai ba ballantana su kaini gurin Aunty na da nayi wa laifi su saka ni in bata hakuri" ya dago ido yana kallonta cikin ido yace "basu zo ba ba kuma su kira ni ba, they just cut me up, basu zo ba ballantana suyi min maganin problem dina, at least ko shawara ce su bani". Tana kallonsa tace "wanne problem ne kenan? Your smoking problem?" Ya girgiza kai yace "basu san wannan ba ai" sai kuma ya bata labarin feelings dinsa for Khausar, da kuma yadda ya tarar tana dating cousin dinsa Ayan, tun daya fara bata ce komai ba har sai daya gama sannan tace "how old are you Bassam? You know nothing about love, do you? That girl doesn't love you, cigaba da jan magana tsakanin ka da ita ba abinda zai yi sai bata zumuncin dake tsakanin ku. Kuma ni a fahimtata familyn ka ba wai cutting dinka off suka yi ba, suna keeping tabs on you tabbas tunda su suka haife ka and they love you. They just want you to grow up, they want you to make the right decision by yourself daga nan sai su san hukuncin da zasu yanke maka. Kafin Mami da Daddy su zo su baka shawara ni ga tawa, ka koma gurin auntyn ka wadda kayi wa laifi kaje ka bata hakuri on your on ba wai sai ance maka kaje ba, ka bawa cousin dinka hakuri kuyi shaking hands kabar maganar Khausar, you don't know what God has planned for you".

Yayi murmushi yace "I guess you are right, maybe wadda zan samu nan gaba tafi Khausar komai" ya karashe maganar yana kashe mata ido daya. Tayi saurin dauke kanta tana jin zuciyarta tana bugawa da karfi. A take taji abincin ya fita daga kanta, ta ture plate din ta mike tace masa zata je class in ya gama ya same ta a can, ya bita da kallo har ta fita yana mamakin me ya chanja mata mood.
Chapter 6 · 0% Book details