Sashe 85
Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dare sannan Inna ta dawo daga unguwar tata. Lokacin kwanciya bacci yayi muka je muka kwanta ni da Murjanatu dan tun zuwanta na mayar da Subay'a dakin su Inna. Muna kwance Murjanatu tana ta chatting da sisters dinta da samarinta. Na dauki wayata ina ta jujjuyawa a hannu na. Sam bana jin dadin rabuwar da mukayi da Sadauki dazu, amma kuma banji dadin abinda ya gaya min ba akan wai ina son fito da Saghir ne saboda ina so sa. Zuciyata tana son in kira shi in ji muryarsa kuma in bashi hakuri amma kuma wani barin yana nuna min cewa shi me yasa ba zai kira ni ba? Na ajiye wayar nayi tsaki na kwanta na juya bayana, kusan awa daya ina kwance babu bacci babu dalilinsa, har Murjanatu ta gama yin wayoyinta da chatting dinta naji tayi addu'a ta kwanta. Sai na kuma dauko wayata na nemo number dinsa nayi dialing a raina ina cewa ba lallai ne ta shiga ba, amma sai ta shiga din, bugu dayakuma ya dauka sai kuma muka yi shiru gabaki daga muna sauraron numfashin juna.
Nace "I tot ba zaka dauka ba" yayi ajjiya zuciya yace "ni na isa. Bayan kin hana ni bacci" nace "ta yaya zan hana ka bacci ina miles away from you" yace "yes, miles away but so close" sai na lumshe ido na ina jin dadi a raina, naji duk bacin raina yana gushe wa zuciyata tayi fes. Nayi murmushi nace "ko?" Yace "ke ma kin sani ai, ko sai na maimaita miki. Haliman nan dai ita ce a kirjin Aliyu. Itace a jininsa ita ce a tsokar jikinsa. Bana jin akwai abinda zakiyi min in ki daukan wayarki" a hankali nace "kayi hakuri. Na bata maka rai na sani amma tawa zuciyar tafi bakanta a kan taka" yace "nima na bata miki ai. I shouldn't have said what I said about Saghir. Matsalata ina kishinki da yawa Diyam" nace "Amma ka yarda cewa bana sonsa kai nake so?" Yayi dariya yace "kara fada min inji?"
Mun jima muna hira har credit din yawa ta ya kare. Sai ya kira muka cigaba. Yana ta bani labarin rayuwar sa a Canada da University din da yayi. Sanyin da naji gari yayi yasa na fahimci dare ya ja sosai. Da kyar nayi masa sallama. "Zaka je office fa gobe" sannan dai yayi min sallama ya kashe. Ina yin addu'a ko minti daya ban kara ba nayi bacci.
Da safe Murjanatu ta tashi tana ta jera hamma. "An hana ni bacci jiya da I love You I Love You" na jefa mata pillow nace "zaki koma kwana a palo" tayi dariya tace "wai su yaya Aliyu an iya soyayya. Lallai in na koma gida akwai labari" sai na tambayeta in tana ganin Papa zai amince, ta bata rai tace "why not?" Nace "ni na taba aure. Aliyu kuma bai taba yi ba" tace "and so what?" Bazan iya miki describing Papa ba, but duk randa kuka hadu you will feel ashamed in kika tuna cewa kinyi min wannan tambayar".
Ranar ma inna ta sake fita unguwa. And I stated to suspect something. Har yamma bata dawo ba, a lokacin ne kuma Sadauki yazo. Na bude masa palon da yake a matsayin na baki muka zauna a ciki. Sai a lokacin na samu courage din yi masa tambayar da take raina nace "Sadauki baka gaya min labarin yaya ladi ba" yayi murmushi yace "sai yanzu kika tuna da ita? Na gaya mata ai nace kin manta da ita gashi kuma kin kwace mata miji" na zaro ido nace "tana raye? Tana ina? I tot ta rasu ne kuma bana son tuno maka da old painful memory, you are already bitter ba sai na kara maa wani ciwon ba" yace "tana nan. Tana damagun gurin wata cousin dinta. Bayan na tafi Canada ta tafi can ita kuma, kuma tunda na dawo taki dawowa gurina tana can sai dai inje in ganta, one day zamu je tare as a couple" na ture maganar gefe nace "baka kuma fada min ba, tuwo na na ranar nan, ka ci? Na jima ina son inji ko kaci ko baka ci ba" sai naga ya bata rai kamar ba zaiyi magana ba sannan yace "naci, sai da safe amma. I drove throughout the night"
Muna cikin hira aka kira shi da kamar ba zai dauka ba kuma sai ya dauka yana cewa "Inna ce" naji sun gaisa sai yace "ina gidan ma. Okay bara in fito sai inzo" na yi masa alamar tambaya da hannuna sai yace "Inna ce tace inje in same ta a gidan Kawu Isa" ina jin haka nasan magana tace, amma ya inna zata yi min haka bayan mun gama magana da ita na roke ta kar ta shiga maganar?
Sai dare inna ta dawo. Bata ce min komai ba sai ta shiga harkokin ta nima kuma ban tambaye ta ba amma sai na kira Sadauki na tambayeshi. Ya kukayi a gidan Kawu Isan?" Yace "babu komai. In tayi tsami zakiji ne ai" amma ni kuma ai bana son tayi tsamin. Nafi so in samu maganar a fresh dinta yadda zan iya tackling dinta. Amma Sadauki yaki gaya min.
Da weekend Murjanatu ta koma gida. Sai naji duk babu dadi saboda na saba da ita a kwanakin da tayi a tare damu. Bayan tafiyar Murjanatu kamar yadda nayi wa Subay'a alkawari na shirya ta muka tafi central prison gurin Saghir. Amma sai da muka samu ganin sa sannan nayi nadamar zuwa gurin cos it really broke my heart to see him a wannan condition din. Ya rame sosai fatarsa tayi baki ta lalace. Yayi datti. Uniform dinsa na prisoners wandon ya yage daga gwuiwa. Sai na tuno wancan Saghir din dan gayu mai iya daukar wanka da kwalliya yana kyalli kamar tarwada.
Ya dauki Subay'a ya daga ta sama ya rungume a jikinsa irin yadda yakeyi mata a gida. Sai ta kankame shi tana cewa "Daddy ka dawo gida gurin mu dan Allah" ya sauke ta yana lakuce mata hanci yace "Daddy zai dawo gida kinji princess, ki ringa yiwa Daddy addu'a kullum in kika yi sallah" sai ya juyo yana kallona yace "look at you. Kinyi wata kiba kamar wata Hajiya. Me Inna take baki kike ci ne?"
Sun jima suna hira shida yarsa, tana bashi labarin sabuwar makarantar ta da sababbin kawayenta. Sai da zamu taho yace "Diyam ya labarin alkawarin mu? Wannan alkawarin da kika yi min shi kadai ne yake keeping dina going a gurin nan. The hope that one day zan fita shi yasa har yanzu banyi loosing sanity dina ba".
Na dauka Subay'a zatayi kuka amma sai naga bata yi ba. Muna zuwa gida tace min "Daddy yace zaki saka uncle Sadauki ya fito dashi ko?" Nace "mommy da uncle Sadauki zasuyi iyakacin kokarin su, amma sai kinyi min alkawarin kin daina maganar, ba zaki kara yiwa kowa maganar ba kuma ba zaki kara yin kuka ba".
Da yammacin ranar nayi baki. Kawu Isa aunty Fatima da Mama. Ina ganinsu naji hankalina ya tashi dan nayi guessing maganar data kawo su. Basu jima da zama ba sai ga Sadauki shima yazo, naji haushinsa for not telling me abinda ake shiryawa. A gaishe su, shima ya gaishe su sannan sai na gaishe shi sama sama.
Kawu Isa ya fara magana. "Diyam innarki ta same ni da maganar ki da yaron nan. Tace yazo yana neman aurenki amma ke kin dauko wasu sharadai marasa tushe kin gindaya masa. Menene dalilinki nayin hakan?" Na dago kai ina son hada ido da Sadauki amma ya sunkuyar da kansa. Na fahimci lallai ni ake jira inyi magana amma kuma ban fahimci me ake so ince din ba. Shin wai su basa ganin abinda nake gani? Sai dai na fahimci akwai banbanci a tsakani na dasu, su basu san gadar zaren da Sadauki ya saka wa Saghir ba, su basu san maganar siyan gida da motar Saghir da Sadauki yayi dan ya taimaka wa Kabir wajen guduwa da kudin da Saghir ya sata ba. Nace "ni ba cewa nayi bazan aure shi ba Kawu. Ni cewa nayi ya yafewa Saghir kuma ya taimaka masa yayi clearing case din drugs dinsa" Mama ta kara da cewa "Sannan kuma ya bashi aiki ko?" Sadauki yayi sauri ya dago kai ya kalle ni, shi baisan da wannan part din ba ma. Nayi niyya ne sai Saghir ya fito sannan zan gabatar masa da wannan kudirin. Na dauke kaina daga kallonsa yayinda Kawu Isa ya rufe ni da fada ta inda yake shiga bata nan yake fita ba. Ni mamaki yake bani sosai musamman saboda nasan ba wai dan zumunci yake yin wannan abin ba, yana yi ne dan ya batawa Alhaji Babba rai kuma dan ya tabbatar da zaman Saghir a prison saboda abinda yayi wa suwaiba. Sai na tambayi kaina "anya kuwa akwai family din daya kai namu lalacewa?"
Sai daya gama yi min fadan sannan yace "kuma yaron nan yana iyakacin kokarin sa gurin ganin an fito da Saghir, jiya ma sai da muka je tare dashi har ofishin commissioner of police, kuma sun gaya mana suna iyakacin kokarin su akan maganar amma akwai rudani a cikin maganar sosai. Sunce zai fito amma sai ya dauki lokaci" Ya juya yana kallon Sadauki yace "shekara nawa ma suka ce mana?" Sadauki yayi gyaran murya yace "drug case is complicated. Kamar five years haka zuwa sama. Amma zai fito".
Mama tace "to alhamdulillah. Wanda ake tunanin ya tafi kenan kuma aka zo aka samu sassaucin da har za'a saka ran fitowarsa? Ai babu abinda zamuyi sai godiya ga Allah. Kai kuma Sadauki Allah ya biya ka" suka ce ameen. Aunty Fatima tace "ai wannan commissioner Ahmad Muhammad yana kokari sosai" suka ci-gaba da hirarrakin su yayinda ni kuma hankali na ya tafi wani gurin daban.
Nace "I tot ba zaka dauka ba" yayi ajjiya zuciya yace "ni na isa. Bayan kin hana ni bacci" nace "ta yaya zan hana ka bacci ina miles away from you" yace "yes, miles away but so close" sai na lumshe ido na ina jin dadi a raina, naji duk bacin raina yana gushe wa zuciyata tayi fes. Nayi murmushi nace "ko?" Yace "ke ma kin sani ai, ko sai na maimaita miki. Haliman nan dai ita ce a kirjin Aliyu. Itace a jininsa ita ce a tsokar jikinsa. Bana jin akwai abinda zakiyi min in ki daukan wayarki" a hankali nace "kayi hakuri. Na bata maka rai na sani amma tawa zuciyar tafi bakanta a kan taka" yace "nima na bata miki ai. I shouldn't have said what I said about Saghir. Matsalata ina kishinki da yawa Diyam" nace "Amma ka yarda cewa bana sonsa kai nake so?" Yayi dariya yace "kara fada min inji?"
Mun jima muna hira har credit din yawa ta ya kare. Sai ya kira muka cigaba. Yana ta bani labarin rayuwar sa a Canada da University din da yayi. Sanyin da naji gari yayi yasa na fahimci dare ya ja sosai. Da kyar nayi masa sallama. "Zaka je office fa gobe" sannan dai yayi min sallama ya kashe. Ina yin addu'a ko minti daya ban kara ba nayi bacci.
Da safe Murjanatu ta tashi tana ta jera hamma. "An hana ni bacci jiya da I love You I Love You" na jefa mata pillow nace "zaki koma kwana a palo" tayi dariya tace "wai su yaya Aliyu an iya soyayya. Lallai in na koma gida akwai labari" sai na tambayeta in tana ganin Papa zai amince, ta bata rai tace "why not?" Nace "ni na taba aure. Aliyu kuma bai taba yi ba" tace "and so what?" Bazan iya miki describing Papa ba, but duk randa kuka hadu you will feel ashamed in kika tuna cewa kinyi min wannan tambayar".
Ranar ma inna ta sake fita unguwa. And I stated to suspect something. Har yamma bata dawo ba, a lokacin ne kuma Sadauki yazo. Na bude masa palon da yake a matsayin na baki muka zauna a ciki. Sai a lokacin na samu courage din yi masa tambayar da take raina nace "Sadauki baka gaya min labarin yaya ladi ba" yayi murmushi yace "sai yanzu kika tuna da ita? Na gaya mata ai nace kin manta da ita gashi kuma kin kwace mata miji" na zaro ido nace "tana raye? Tana ina? I tot ta rasu ne kuma bana son tuno maka da old painful memory, you are already bitter ba sai na kara maa wani ciwon ba" yace "tana nan. Tana damagun gurin wata cousin dinta. Bayan na tafi Canada ta tafi can ita kuma, kuma tunda na dawo taki dawowa gurina tana can sai dai inje in ganta, one day zamu je tare as a couple" na ture maganar gefe nace "baka kuma fada min ba, tuwo na na ranar nan, ka ci? Na jima ina son inji ko kaci ko baka ci ba" sai naga ya bata rai kamar ba zaiyi magana ba sannan yace "naci, sai da safe amma. I drove throughout the night"
Muna cikin hira aka kira shi da kamar ba zai dauka ba kuma sai ya dauka yana cewa "Inna ce" naji sun gaisa sai yace "ina gidan ma. Okay bara in fito sai inzo" na yi masa alamar tambaya da hannuna sai yace "Inna ce tace inje in same ta a gidan Kawu Isa" ina jin haka nasan magana tace, amma ya inna zata yi min haka bayan mun gama magana da ita na roke ta kar ta shiga maganar?
Sai dare inna ta dawo. Bata ce min komai ba sai ta shiga harkokin ta nima kuma ban tambaye ta ba amma sai na kira Sadauki na tambayeshi. Ya kukayi a gidan Kawu Isan?" Yace "babu komai. In tayi tsami zakiji ne ai" amma ni kuma ai bana son tayi tsamin. Nafi so in samu maganar a fresh dinta yadda zan iya tackling dinta. Amma Sadauki yaki gaya min.
Da weekend Murjanatu ta koma gida. Sai naji duk babu dadi saboda na saba da ita a kwanakin da tayi a tare damu. Bayan tafiyar Murjanatu kamar yadda nayi wa Subay'a alkawari na shirya ta muka tafi central prison gurin Saghir. Amma sai da muka samu ganin sa sannan nayi nadamar zuwa gurin cos it really broke my heart to see him a wannan condition din. Ya rame sosai fatarsa tayi baki ta lalace. Yayi datti. Uniform dinsa na prisoners wandon ya yage daga gwuiwa. Sai na tuno wancan Saghir din dan gayu mai iya daukar wanka da kwalliya yana kyalli kamar tarwada.
Ya dauki Subay'a ya daga ta sama ya rungume a jikinsa irin yadda yakeyi mata a gida. Sai ta kankame shi tana cewa "Daddy ka dawo gida gurin mu dan Allah" ya sauke ta yana lakuce mata hanci yace "Daddy zai dawo gida kinji princess, ki ringa yiwa Daddy addu'a kullum in kika yi sallah" sai ya juyo yana kallona yace "look at you. Kinyi wata kiba kamar wata Hajiya. Me Inna take baki kike ci ne?"
Sun jima suna hira shida yarsa, tana bashi labarin sabuwar makarantar ta da sababbin kawayenta. Sai da zamu taho yace "Diyam ya labarin alkawarin mu? Wannan alkawarin da kika yi min shi kadai ne yake keeping dina going a gurin nan. The hope that one day zan fita shi yasa har yanzu banyi loosing sanity dina ba".
Na dauka Subay'a zatayi kuka amma sai naga bata yi ba. Muna zuwa gida tace min "Daddy yace zaki saka uncle Sadauki ya fito dashi ko?" Nace "mommy da uncle Sadauki zasuyi iyakacin kokarin su, amma sai kinyi min alkawarin kin daina maganar, ba zaki kara yiwa kowa maganar ba kuma ba zaki kara yin kuka ba".
Da yammacin ranar nayi baki. Kawu Isa aunty Fatima da Mama. Ina ganinsu naji hankalina ya tashi dan nayi guessing maganar data kawo su. Basu jima da zama ba sai ga Sadauki shima yazo, naji haushinsa for not telling me abinda ake shiryawa. A gaishe su, shima ya gaishe su sannan sai na gaishe shi sama sama.
Kawu Isa ya fara magana. "Diyam innarki ta same ni da maganar ki da yaron nan. Tace yazo yana neman aurenki amma ke kin dauko wasu sharadai marasa tushe kin gindaya masa. Menene dalilinki nayin hakan?" Na dago kai ina son hada ido da Sadauki amma ya sunkuyar da kansa. Na fahimci lallai ni ake jira inyi magana amma kuma ban fahimci me ake so ince din ba. Shin wai su basa ganin abinda nake gani? Sai dai na fahimci akwai banbanci a tsakani na dasu, su basu san gadar zaren da Sadauki ya saka wa Saghir ba, su basu san maganar siyan gida da motar Saghir da Sadauki yayi dan ya taimaka wa Kabir wajen guduwa da kudin da Saghir ya sata ba. Nace "ni ba cewa nayi bazan aure shi ba Kawu. Ni cewa nayi ya yafewa Saghir kuma ya taimaka masa yayi clearing case din drugs dinsa" Mama ta kara da cewa "Sannan kuma ya bashi aiki ko?" Sadauki yayi sauri ya dago kai ya kalle ni, shi baisan da wannan part din ba ma. Nayi niyya ne sai Saghir ya fito sannan zan gabatar masa da wannan kudirin. Na dauke kaina daga kallonsa yayinda Kawu Isa ya rufe ni da fada ta inda yake shiga bata nan yake fita ba. Ni mamaki yake bani sosai musamman saboda nasan ba wai dan zumunci yake yin wannan abin ba, yana yi ne dan ya batawa Alhaji Babba rai kuma dan ya tabbatar da zaman Saghir a prison saboda abinda yayi wa suwaiba. Sai na tambayi kaina "anya kuwa akwai family din daya kai namu lalacewa?"
Sai daya gama yi min fadan sannan yace "kuma yaron nan yana iyakacin kokarin sa gurin ganin an fito da Saghir, jiya ma sai da muka je tare dashi har ofishin commissioner of police, kuma sun gaya mana suna iyakacin kokarin su akan maganar amma akwai rudani a cikin maganar sosai. Sunce zai fito amma sai ya dauki lokaci" Ya juya yana kallon Sadauki yace "shekara nawa ma suka ce mana?" Sadauki yayi gyaran murya yace "drug case is complicated. Kamar five years haka zuwa sama. Amma zai fito".
Mama tace "to alhamdulillah. Wanda ake tunanin ya tafi kenan kuma aka zo aka samu sassaucin da har za'a saka ran fitowarsa? Ai babu abinda zamuyi sai godiya ga Allah. Kai kuma Sadauki Allah ya biya ka" suka ce ameen. Aunty Fatima tace "ai wannan commissioner Ahmad Muhammad yana kokari sosai" suka ci-gaba da hirarrakin su yayinda ni kuma hankali na ya tafi wani gurin daban.