← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 112

Sashe 44

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Muna zuwa muka tarar already su Alhaji Babba, kawu Isa, Aunty Fatima da kuma Saghir suna can. Tun kafin mu gama gaishe da Hardo ya fara fada. "Yanzu wato tun kafin in bar duniya har kanku ya rarrabu irin haka? Har zumuncin ku ya tarwatse har haka? Har son zuciya ta son yayanku ya rufe muku ido kun manta da yanuwantakar da take tsakanin ku? Kun manta da tarbiyyar da ni da inno muka baku?" Ni dai ina rakube dama daga can bakin kofar shiga dakinsa, na hango Saghir shima a can daya end din su kuma iyayen mu suna tsakiya. Sai daya gama fadansa sannan yace a tsara masa abinda ya faru, kawu Isa ne yayi bayanin haihuwata da rasuwar twins da kuma abinda ya sami Alhaji Babba na gobara, duk da cewa duk Hardo yasan wannan, sai kuma yayi bayanin shi Saghir abinda yace da kuma ni abinda nace, ya kara da cewa "mu abinda ya bamu haushi shine yadda Amina ta rufe idonta ta goyi bayan Diyam, bayan kowa yasan tsakanin mata da miji sai Allah babu ta yadda za'a gane mai gaskiya a cikin su. Kawai ta hana yarinyar komawa gidan mijinta ba tare da anyi bincike ba. Sannan kuma ta hada kayan ta ta bar gidan Alhaji Babba a lokacin da yake tsaka da bukatar kulawar yan uwansa, ta koma gidan marigayi ta bude ta kafa zaman kanta. Wannan ne yasa muma muka zare ta daga jikin mu".

Hardo ya hada su gaba-daya ya wanke su, yace da mai gaskiya da marar gaskiya duk a gurinsa masu laifi ne, sannan yace "ni yanzu zan yanke hukunci, sai kuma inga wanda a cikin ku zai nuna min cewa ya girma yanzu yayi ya'ya kuma ni bani da iko akan ya'yansa" ya fada yana kallon Inna data sunkuyar da kanta kasa. Ya nuna ni yace "Haleema" nace "na'am" yace "zaki koma gidan mijinki" na runtse ido hawayena yana zubo wa. Ya dora "uwani zata biku ku cigaba da zama tare kamar wancan karon. Zan gaya mata cewa ta saka ido sosai a kanka kai Saghir ko sau daya ta tabbatar da maganar Halima ni da kaina zan karbi takardar ta a hannunka. Sannan abu na gaba shine zaka saka ta a makaranta, zata karasa karatunta na secondary inta gama kuma in kun daidaita a tsakanin ku sai ta cigaba. Ka fahimta?" Saghir yayi gyaran murya yace "na fahimta Hardo, kuma ina godiya" Hardo ya juyo kaina yace "ke fa Halima? Kin fahimta?" Na gyada kaina, yace "ki bude baki kiyi magana mana?" Sai na bare baki na saka kuka. Nan take ya koreni daga dakin yace in tafi cikin gida.

Anan muka kwana, naga Inna ta dan shiga yan'uwanta suna magana sama sama. Ni kuwa babu wanda na kula ina kudundune ina zazzaɓi. Da daddare wai sai ga kira inje inji Saghir yana waje, na tashi naga duk suna kallona dan haka na saka hijab na fita, na dan tsaya a soro na bata lokaci sai na dawo gida nayi kwanciya ta.

Da safe kowa ya shirya zamu tafi, mukayi sallama da mutan gida ina fitowa waje na hango Saghir a tsaye a jikin motar dasuka zo da ita ya harde kafafu yana kada key, na dauke kaina zan wuce yace "babu gaisuwa?" Na juya baya naga kawu Isa yana kallon mu sai na gaishe shi ciki ciki, ya amsa yana murmushi yace "in kin koma gida ki shirya jibi zan zo mu tafi" na faki ido na jefa masa harara na wuce. A raina nace "munafiki".

Mun koma gida da kwana biyu kuwa sai gashi da safe wai in fito mu tafi. Na koma nayi kwanciya ta Inna tace "tashi ki dauki mayafinki ku tafi, sauran kayanki zan hado miki in aiko miki dasu" na fara kuka, sai ta zauna kusa dani ta jawo ni jikinta tace "kiyi hakuri Diyam, nasan wannan duk laifina ne dan tun farko ni na bada kofa har akayi miki auren nan, yanzu kuma babu yadda zanyi tunda igiyar auren ba a hannuna take ba. Kiyi hakuri kinji?" Sai naga kwalla a idonta, nayi saurin goge hawayena ina gyada kai, ta dauko sabuwar waya a cikin kwalinta da sim card ta miko min tace "tun ranar nan na siyo miki wata. Ki tafi da ita, duk halin da kike ciki ki kirani ko ki kira Hafsa ki gaya mana. Uwanin ma munyi waya da ita tace min itama yau zata je. Ki yi ta addu'a kina gaya wa Ubangiji kukan ki, shi kadai ne zai zaba miki abu mafi alkhairi a rayuwar ki".

A mota na tarar dashi a zaune yana jin kida, na kai hannu zan bude baya sai ya danna lock ya rufe, dole na na shiga gaba yaja motar ba tare daya ce min komai ba. Ina ta kuka na kasa kasa har mukayi nisa muka kusa unguwar sannan yace "wallahi ko kiyi shiru da kukan nan ko kuma in sauke ki a gurin nan" nayi shirun tunda nasan ba karamin aikinsa bane ya saukeni a wajen.

A bakin gate ya ajiye ni, ina fitowa ya ja motarsa yayi gaba. Na shiga gidan ni kadai kamar mayya. Maigadi ya taso ya muka gaisa na bude palo na ganshi kamar wanda akayi yakin badar a ciki, kaca kaca, ga used plates nan ko'ina duk sun bushe. Bedrooms ne kadai masu dan kyau suma bawai gyarawa akayi ba amma dai ba'a bata su ba. Na lura cewa abubuwa da yawa were missing a gidan, daga dukkan alamu kayan gidan su suka koma source of income na Saghir. Na kunna tv naga lafiyar ta kalau,na fara tattara gidan kenan naji a tv an sako wakar Westlife ta coast to coast "my Love"

An empty street, An empty house, A hole inside my heart, I'm all alone The rooms are getting smaller. I wonder how, I wonder why, I wonder where they are, The days we had, The songs we sang together Oh yeah
And all my love I'm holding on forever, Reaching for the love that seems so far, So I say a little prayer, And hope my dreams will take me there, Where the skies are blue To see you once again, my love, Over seas from coast to coast, To find the place I love the most Where the fields are green To see you once again, my love
To hold you in my arms, To promise you my love, To tell you from my heart You're all I'm thinking of. And reaching for the love that seems so far........

Sai naji kamar dani suke a wakar with Sadauki as my faraway love. Na zauna akan kujera na kama sana'ar tawa ta kuka. Ina cikin yi uwani tayi sallama ta shigo, sai na tashi da gudu naje na rungume ta.

Tare muka gyara gidan gaba-daya, sannan uwani ta fitar da kudi daga aljihunta ta bawa maigadi yayo mana cefane mukayi girki. Muna gamawa sai ga Saghir yazo ya zauna a palo suna gaisawa da uwani sannan ya ce min "kawo min abinci" Sai na juya ina mamakin karfin hali irin na Saghir, kai da baka bada kudin cefane ba ina kai ina neman abinci? Ina kallonsa ya dauki wayata ya duba, sai naga ya daddanna ya ajiye. Da dare na fito daga wanka ina shirin kwanciya waya ta tayi kara. Na dauka ina duba number din dan number inna da ta Mama kawai nsyi saving dazu a gurin uwani. Na dauka naji muryar Saghir "ki kawo min ruwa dakina" na ajiye wayar nayi tsaki. Har zan kwanta sai kuma na saka hijab dina na dauko ruwan naje na kai masa. Yana kwance ya kashe fitila ya rufa da bargo, na ajiye ruwan ba tare dana ce masa komai ba. Zan fita yace "Diyam" na juyo ina kallonsa ya nuna kusa dani a kan gado yace "come here" na watsa masa harara na juya yace "kin san dai hakkina ne ko?" Na juyo nace "kai wanne daga cikin hakkokin ka ka sauke?" Yace "ki bani chance ki gani. Kuma nasan so far I have been trying my best" na fara tunanin wanne ne best din nasa. Sai ji nayi yace "zanyi Allah ya isa in baki zo ba" na juya da sauri ina kallonsa nace cikin mamaki "are you for real?" Ya daga kafada yace "bani da wani choice ai, ina bukatar ki kin ki bani, bazan iya miki dole ba so my only choice is to do Allah ya isa, ta rago" na juyo kamar wadda aka saka wa remote ina tunanin yadda aljanna ta take kasan kafarsa amma a lokacin babu abinda nake so irin in shake kyakykyawan wuyansa har sai ya daina numfashi. Na zauna a bakin gado na juya masa baya ina jin hawayena yana zuba a cinyoyi na, ina jinsa ya matso ya zare rigata sannan ya jawo ni zuwa jikinsa, ina jinsa yayi duk abinda yake ganin zai iya yayin da ni kuma kukana yake kara tsananta har ya gama abinsa. Ya sake ni yana mayar da numfashi. Na mike zaune na jawo rigata na saka ba tare dana kalleshi ba na mike sai ji nayi yace "shikenan kuma? Ko dan curdle din nan ma, irin falling asleep together din nan na masu aure babu, na juyo ina kallonsa da kumburarrun idanuwana, yayi murmushi nace "shima in banzo ba Allah ya isan zaka yi?" Yace "well, yes" na juyo na dawo na kwanta. Ya matso da pillon sa kusa dani ya jawo ni jikinsa sannan ya jawo bargo ya rufe mu.
[2/7, 4:27 PM] +234 706 813 0709: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Thirty Seven : Abatcha Motors
Chapter 44 · 0% Book details