← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 112

Sashe 9

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tana fita ta tari cab, since ta kasa sanin wanne mataki zai dauka ita zata dauki nata matakin da kanta. Bata san hotel din da Bassam yake ba dan haka direct mall din da yake aiki ta tafi. Tana kallon irin kallon da mutanen gurin suke yi mata kuma tasan yana da alaka da dogon hijab din da ta saka amma bata kula su ba ta cigaba da harkokin gabanta. Customer care ta tafi ta tambayi matar gurin agame da ma'aikacin su mai suna Sadiq Abubakar Sadiq. Daga farko kin bata wani information tayi a kansa for security reason, sai da tayi mata karyar ita friend dinsa ce ta yi loosing phone dinta ne kuma tana nemansa emergency concerning harkar karatunsu, sai da matar tayi checking taga sunan makarantar da kuma department din da Diyam din ta gaya mata yayi tallying da information din Bassam sannan ta gaya mata cewa bai shigo yau ba, amma ta gaya mata sunan hotel dinsa. Godiya Diyam tayi mata ta fita ta nufi address din da aka bata. A reception ta tsaya tasake yi musu bayani irin yadda tayi wa waccan matar amma suma suka hana ta hawa sama instead sai suka kira dakinsa through intercom, yana dauka Diyam ta karbi phone din tace "Bassam? Diyam ce. Can you come down for a minute? Ina son magana da kai please" daga can barin Bassam bai ce komai ba dan ji yake kamar in yayi maganar ma voice dinsa ba zai fito ba, sai kawai ya ajiye wayar. Diyam ta ajiye itama a ranta tana kissima cewa yayi fushi ne shima. Amma sai ta kasa fita, sai ta samu guri ta zauna tayi folding hannayenta ta zuba idanunta akan kofar lifter da take ta sunturin kai mutane sama da sauko dasu. Tafi minti sha biyar a zaune sannan ta mike cikin sanyin jiki da niyyar fita, a lokacin ne kofar lifter ta bude ya fito. Sweater ce a jikinsa mai hade da hula wacce ya jawo ya rufe kusan rabin fuskarsa dan haka ta kasa karantar emotions dinsa amma sai taga a idonta kamar ya dan rame kadan. Ya tsaya a gabanta ba tare daya ce komai ba, tana jujjuya hannayenta tace "Bassam magana nake so muyi please in babu damuwa" ya danyi gyaran murya sannan direct yace "are you married? A yanzu nake nufi" da sauri ta girgiza kanta tace "of cause am not" ya gingina kai sannan yayi hanyar waje ba tare daya kuma cewa komai ba ita kuma ta bishi a baya.

Baya suka zagaya, suka jera suna tafiya a tare, suna taka kafafuwansu a tare, amma daga ka gansu kasan akwai tension a tsakanin su. Wani garden suka shiga sannan suka je cikin wata rumfa suka zauna, gurin very quite duk da cewa akwai mutane jefi jefi suna hutawa a gurin, can kuma dan nesa dasu kadan swimming pool ne a zagaye ta fitulu mutane suna wanka a ciki. Ta daga ido tana kallonsa taga shima itan yake kallo, suna hada ido yace "uhumm? Ina jin ki, kince kina son magana dani" tayi kasa da nata idon tace "Bassam am so sorry ban gaya maka all these before ba, nayi haka ne saboda banyi tunanin da akwai bukatar in gaya maka din ba, yanzu kuma nace zan gaya maka ne saboda ka fahimci dalilina na daina kula ka, kasan cewa am doing it for you" ya katse ta "for me? How is that so?"

Ta bude baki zata yi magana wayar ta tayi kara. Ta dauka tana dubawa wa, "Inna" ta danyi murmushin takaici ta ajite wayar, of cause Inna, of cause gurin Inna zashi ya shirya mata wata dramar kuma, tun dazu abinda take tunani ga amsar ta bayyana yanzu. Tasan wannan ba kiran Inna ba ne ba dan tun da tazo kasar nan Inna bata kiranta dan tace ita bata gane wannan lissafin lokutan dan haka sai dai ita Diyam ta rinka kiransu ko kuma in Asma'u tana gida sai ta kira.

Har wayar ta katse bata dauka ba a take kuma aka sake kira, Bassam ne ya daga wayar ya ga sunan da yake kira yace mata "ain't this important? Ba innar ki bace?" Ta karbi wayar ta daga kiran, sai kuma ta saka a handsfree yadda Bassam zaiji abinda ake cewa, maybe abinda zai ji ya taimaka masa wajan fahimtar ta. Tayi sallama, daga daya barin inna tace "Haleema ya karatun? Ya 'yar'uwar taki?" Diyam tace "lfy lau muke inna ya kuke?" Inna tace "uhmm. Ni ina naga lfy kuwa? Kullum hankalina a tashe, ni dai har yanzu zuciyata bata kwanta da wannan karatun naki a kasar turawa ba Diyam" Diyam ta lumshe idonta tace "Inna ba mun gama wannan maganar ba tun kafin in taho? Inna ke da bakinki kika nuna hakan da nayi shine dai dai, yaushe kuma kika chanza ra'ayinki " Inna tace "zancen lokacin da na chanza ra'ayi duk ba shine mai muhimmanci ba, abu mai muhimmanci shine na chanja ra'ayin nawa. Ni ban yarda da zamanki a kasar waje ke kadai babu miji ba, dan haka cikin biyu zaki zabi daya, ko dai ki hakura da karatun ki dawo gida ki zauna a gaba na ina kallonki har lokacin da kuka shirya auren naku ko kuma a daura auren yanzu in yaso ya taho kuyi ta zaman tare, tunda shima yana da nasa harkokin a nan kasar". Diyam ta shafa fuskarta ta taji ta dauki zafi kamar mai zazzabi, ta kalli Bassam taga ita yake kallo shima fuskarsa cike da tambayoyi. Inna tace "kina jina shine kika yi shiru ko?" Diyam tace "Inna bashi wayar muyi magana" Inna tace "wa?" Diyam tace "nasan yana nan a gabanki Inna saboda kalmomin da kika fada ba kalmomin ki bane ba, nasa ne, shi yazo ya gaya miki su, to gwara ni ya gaya min a kunne na inji" Inna tace "au, wato abinda Ingilan ta koya miki kenan? Tun yanzu Diyam?" sai kuma suka ji muryar wani a background, can kuma sai ga muryarsa fes ta fito, very deep and very clear, yace "yes, I am here" Diyam ta hadiye wani abu a makogoronta cikin rarrauniyar murya tace "this is not the agreement, ba haka muka yi alkawari ba" yace "ba haka mukayi alkawari ba and yet you broke the promise" da sauri tace "I didn't, believe me I didn't" yace "we will see about that, tomorrow" daga nan suka ji shiru ya kashe wayar.
[1/8, 10:49 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Ten : The Beginning

Diyam ta dauke kanta tana kallon wani mai yankan fulawa da yake ta aikin gyara flowers din gurin suna kyau. Amma sam hankalinta ba'a kansa yake ba, hankalinta yana gurin yadda zata fita daga wannan trap din ne, a hankali tace "not again, not now" Bassam yace "what?" Ta juyo tana kallonsa kamar yanzu ta fara ganinsa kafin tace "Bassam. What do you understand by the word Love?" Ya karkata kai yana kallonta sai kuma yayi dan murmushi yace "that is a one million dollars question" tace "just answer it, kai me kake tunanin shine love" yayi shiru tsahon minti biyu yana tunani sannan yace "feelings. Love is a feeling of deepest desire for something. Like kaji kana son kasancewa tare da wanda kake so din" ta gyada kanta tana murmushi tace "yes you are right, love can be that but lust can also be that. Sometimes mutane suna zama confused akan bambancin love the lust. To me zan iya cewa abinda ka fada is just one aspect of love. Ta gyara zama tana kallonsa cikin ido tace "zan baka labari na Bassam, maybe a karshe you will understand the true meaning of love, you will understand kuma abinda yasa nake son yanke alaka ta da kai sannan kuma maybe it will help you find redemption". Ta koma ta jingina da jikin kujera tana kallon yadda ruwa yake tsiri a wani fountain kusa dasu. A hankali ta fara tariyo rayuwar ta.

Sunana Haleema Usman Kollere. Wannan shine labari na.

Kamar yadda na gaya maka asalin iyayena yan rugar Kollere ne dake karamar hukumar damagum ta jihar Yobe. Inna ta da baffana 'yanuwa ne, kakanin su daya. Da kakana na wajen uba da kakata ta wajen uwa uwarsu daya ubansu daya. Innar mu su biyu ne kacal agurin mahaifiyar su daga ita sai kanwarta Yakumbo Hafsatu sai tarin 'yan uba da suke dasu kasancewar mahaifinsu yayi aure aure da yawa, kusan sa'anni ne su biyun kuma tun suna yara Allah yayi wa mahaifiyarsu rasuwa ta tafi ta barsu a hannun kishiyoyi su kuma sukayi caa a kansu suka mayar dasu bayinsu, ganin ana neman hallakasu yasa kakana na gurin uba, Hardon rugar mu, ya karbo su a gurin ubansu ya kawo su gidansa gurin matarsa Inno wadda itace kakara ta gurin uba kuma ita kadai ce matarsa ta hada su ya yayanta ta rike.
Chapter 9 · 0% Book details