Sashe 33
Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina nan kwance aka yi ta shigowa da akwatinan ana jere wa a gefe, ina jin daya daga cikin yan aikin gidan da suke shigowa da kayan tace da dayar "ai ga amaryar nan a kwance" sai kuwa suka hada baki suka rangada min wata uwar guda a kaina wadda naji kamar zata tsaga min kan. Sai bayan da kowa ya watse sannan Inna ta shigo ita da Asma'u. Ta tashe ni zaune tana murmushi "tashi Diyam, tashi kiga kayan lefen ki" ta fara bubbudewa, "kinga wadannan sarkokin? Wannan zata yi miki kyau. Kinga pearls din da kike ta nacin in siya miki. Kinga wani lace? Dankari! Wannan ai na zuwa gidan biki ne. Ga takalmin can mai tsini irin wanda kike so" ni dai kallon ta kawai nake yi ko kadan banji zuciyata tayi sha'awar wani abu a cikin kayan ba, na kalli Asma'u data baje a gefe tana ta zaben kayan kwalliya wai duk tana so in bata. Sai kuma ina ta tashi ta fita ta bani guri. Na kalli kayan, akwatuna ne set hudu, pink, purple, peach da blue kowanne kuma da kyar ake rufe shi saboda kaya. Na mika hannu na na dauki wata bra ina kalla a raina nace "ko me suke tunanin zan saka a cikin wannan brazier? Na mayar da ita na ajiye na koma na kwanta na juya wa kayan baya.
Kwana biyu bayan nan ina zaune ina cin abincin da yanzu kullum sai Hajiya Babba ta girka ta aiko min dashi Inna kuma sai ta matsa min naci, sai ga Murja nan ta shigo "Diyam Alhaji yace ki shirya zamu fita yanzu gaba daya" ban kalle taba nace "babu inda zanje" ta daga hannu tace "ni dai yar aike ce". Sai kuma ga Hajiya Babba nan tazo da kanta, taci kwalliya kamar mai shirin zuwa gidan biki tace "innar Asma'u Alhaji yace Diyam tazo muje ganin gida da ita, in yaso in da akwai wani abin da take so sai ta fada a siya" tana fita Inna tace "ki tashi maza ki shirya ku tafi" na bata rai "Inna ni babu abinda nake so, in na gani ma babu abinda zan ce su kara" ta watsa min harara dole na tashi na shiga toilet na wanke fuskata na fito na saka hijab tace "kuma ko dan mai ba zaki shafa ba?" Na dawo na lakuci mai na shafa na juya tace "au dan nace mai shine kika shafa man shi kadai?" Nayi kamar zanyi kuka tace jeki.
Ina fita na tarar da yayan gidan suna ta shiga mota, matan gidan kuma suna gefe a tsaye suna hira. Na tsaya daga gefe ina kallon compound din, na kalli dai dai inda muka tsaya da Sadauki rannan sai naji ina ma dai ranar zata dawo in sake ganin sa at least koda sau daya ne. Na kalli gurin motoci sai idona ya sauka a kansa, cikin normal shigarshi ta dogayen kaya yayi kyau sai kyalli yake yi amma fuskar nan babu annuri ko digo a cikinta. Kallo daya nayi masa naji kamar duniyar ce take kara kuntatamin dan haka na juya na bar gurin na tafi inda yara suke shiga mota sai kuma naji kira da muryar Hajiya Babba "Diyam, ki dawo nan tare zamu tafi dake" na juya kamar zanyi kuka na koma, sai naga sun doshi motar da yake tsaye a kusa da ita, anti amarya tace "Diyam shiga gaba mu sai mu zauna a baya" na tsaya kawai ina kallon su kamar in rufe su da duka har suka gama shiga, shima ya shiga seat din driver ya zauna ya tayar da motar, sai da suka sake yi min magana sannan na kama handle din kofar jishi a rufe ni kuwa na koma da baya na nade hannu na a kirji. Hajiya Yalwati ta leko. "Ki shigo mana Diyam, ke fa muke jira" nace "kofar a rufe take Hajiya" ina jin Hajiya Babba tana yi masa magana, ya dauke kai kamar bai jita ba sannan kuma bayan wajan minti daya sai ya bude lock din. Na bude na zauna a makale a bakin kofa ba tare dana ko kalli side din da yake ba.
A hanya naji Hajiya Babba tana yiwa kishiyoyinta bayani "kunsan halin Saghir da rashin son hayaniya, wai shi ba zai zauna a cikin gari ba saboda kar mutane su dame shi, nace to kai me kanne da yawa? Namiji tilo a cikin mata? Ai dole ko gari ka bari sai kannenka sunje gidan ka, shine Alhaji ya biye masa aka siya masa gidan a can wajen gari, unguwar tokarawa acan zasu zauna" a raina nace 'wato yadda zai samu damar kasheni hankali kwance' ni a lokacin ban ma san unguwar ba sai dai naga mun dau hanyar barin gari, sai da muka wuce 'yan kaba sannan muka sauka daga titi muka shiga unguwar dana lura kamar sabuwar unguwa ce. Tun daga nesa na gane gidan. A house fit for the only son of Alhaji Babba amma ko kadan banji kyan gidan ya burge ni ba. Mukayi packing kusan a tare dasu Murja, na fita na tafi gurin su muka shiga tare amma sai na zame na zagaya bayan gidan nayi zamana akan veranda r backdoor din gidan. Ina jiyo su suna ta hayaniya da iface ifacen su alamar suna cikin nishadi amma ko sha'awar inje inga gidan banyi ba, addu'a nake a raina kar Allah yasa ina da rabon ganin cikin gidan nan in dai a matsayin matar Saghir ce. Naji wata irin kewar Sadauki ta taso min, sau dubu gwara ace in zauna da Sadauki a gidan kasa me yoyo akan in zauna da Saghir a wannan gidan.
Kamshin turare naji, na daga kai sai na ganshi a tsaye yana kallon gefe da alama bai san ma ina gurin ba. Fuskar nan kamar an aiko masa da mutuwa. Nayi saurin share hawayen fuskata saboda bana son ko kadan yaga weakness dina ballantana ya kara rainani. Motsin da nayi ne yasa ya juyo ya kalli inda nake, sai kuma naga ya tako cikin gadara yazo gabana ya tsaye ya kara tamke fuska yace "ke! Me na gaya miki rannan? Ba zaki je ki gaya musu ba sai kin je kin daukowa kanki abinda ba zaki iya ba ko?" Na mike tsaye na karkade hijab dina na juya zan bar masa gurin, ya damko hijab dina ya juyo dani yace cikin barazana "ba dake nake magana ba?" Na zabga masa hararar da nasan ba'a taba yi masa irinta ba nace "su wadanda kake magana a kansu ai sunfi kowa sanin cewa bana sonka, sunfi kowa sanin ina da wanda nake so wanda kuma yake sona, asalima dan su raba ni dashi ne suke neman makalamin kai"
The Game Has Began
It is such a long episode ko?
[1/28, 10:58 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â? DIYAM â?
By
Maman Maama
Episode Twenty Eight: Destiny
Kafin mu cigaba please let us all take a moment and pray for Maryam Sanda and then pray for ourselves. Allah ya sa wannan hukuncin da aka yanke mata ya zamar mata alkhairi a duniya da kuma a lahirar ta, mu kuma Allah ya kare mu daga mummunar kaddara, Allah ya kare mu daga sharrin shaidan da sharrin zuciya, Allah yasa mu fi karfin zukatan mu a kodayaushe.
Bayan haka ina kira ga matan aure manyan mu da kananan mu, please idan kin tabbatar your marriage is not working, idan kin tabbatar kin je limit dinki na hakuri a gidan auren ki, please walk out of the marriage. Allah ya halatta saki for a reason, wani lokacin rabiwar tafi alkhairi akan cigaba da zaman. It is better a kiraki da bazawara then ki kasance in maryam sanda's shoes.
Sannan iyayen mu dan Allah ku dube mu da idon rahama, ku tausaya mana, dan Allah idan yarinya tazo gida tace ta gaji da zaman auren ta please ku bincika sosai, idan tana da gaskiya kuyi supporting dinta, kar ku tura yarku ga halaka, karku tura yarku zuwa wuta.
Now, let's continue with labarin Diyam maybe anan ma da akwai darasin da zamu dauka.
Da mamaki karara fuskarsa yake kallona, maybe bai taba tsammanin zan iya mayar masa da magana haka ba. Yace "ke? Kin san dawa kike magana kuwa? Ni din ne ma kike cewa za'a makala miki?" Na cigaba da kallon sa cikin ido duk a cikin kokari na na nuna masa cewa bana jin tsoronsa, amma zuciyata in banda lugude babu abinda take yi. Ya daga hannu da niyyar wanka min mari sai kuma ya kalli gidan inda hayaniya take fitowa daga tagogin sama, ya fahimci yana dukana zan tara masa jama'a dan haka sai ya dunkule hannunsa sannan ya sauke, ya nuna ni da dan yatsa yace "in kika sake kika shigo gidan nan sai na karya ki" na fusge hijab dina daga hannunsa nace "not today, kuma ni bani zan shiga gidan ka ba sai dai a shigo dani dan dole" na juya na tafi na barshi anan ina jin dadi a zuciyata, ashe dai Sadauki bai tafi da dukkan Strength din nawa ba, ko kuma maybe a time din wannan hug din ne yayi passing some of his strength and courage to me.
Muna komawa gida na wuce direct zuwa dakin inna, na gaisheta tana ta washe baki tace "kun dawo? Ya gidan?" Na tashi ina ninke hijab din dana cire nace "lfy lau" tace "lfy lau? Shikenan abinda zaki ce? Bayanin gidan zaki yi min inji dame dame aka saka kuma menene ba'a saka ba" nace "Inna ban sani ba nikam, ban shiga ciki ba a waje na zauna" nan fa takama fada, ni kuma nayi shiru har saida ta gama sannan nace "Inna yace inna shiga gidan sa sai ya kashe ni" sai ta girgiza kai tace "fada kawai yake yi, shima fushi yake yi saboda an matsa masa akan maganar nan, daga ke har shi ba kwaso amma abinda mu iyayenku muka hango ku ba zaku hango shi yanzu ba sai nan gaba zaku fahimta".
Kwana biyu bayan nan ina zaune ina cin abincin da yanzu kullum sai Hajiya Babba ta girka ta aiko min dashi Inna kuma sai ta matsa min naci, sai ga Murja nan ta shigo "Diyam Alhaji yace ki shirya zamu fita yanzu gaba daya" ban kalle taba nace "babu inda zanje" ta daga hannu tace "ni dai yar aike ce". Sai kuma ga Hajiya Babba nan tazo da kanta, taci kwalliya kamar mai shirin zuwa gidan biki tace "innar Asma'u Alhaji yace Diyam tazo muje ganin gida da ita, in yaso in da akwai wani abin da take so sai ta fada a siya" tana fita Inna tace "ki tashi maza ki shirya ku tafi" na bata rai "Inna ni babu abinda nake so, in na gani ma babu abinda zan ce su kara" ta watsa min harara dole na tashi na shiga toilet na wanke fuskata na fito na saka hijab tace "kuma ko dan mai ba zaki shafa ba?" Na dawo na lakuci mai na shafa na juya tace "au dan nace mai shine kika shafa man shi kadai?" Nayi kamar zanyi kuka tace jeki.
Ina fita na tarar da yayan gidan suna ta shiga mota, matan gidan kuma suna gefe a tsaye suna hira. Na tsaya daga gefe ina kallon compound din, na kalli dai dai inda muka tsaya da Sadauki rannan sai naji ina ma dai ranar zata dawo in sake ganin sa at least koda sau daya ne. Na kalli gurin motoci sai idona ya sauka a kansa, cikin normal shigarshi ta dogayen kaya yayi kyau sai kyalli yake yi amma fuskar nan babu annuri ko digo a cikinta. Kallo daya nayi masa naji kamar duniyar ce take kara kuntatamin dan haka na juya na bar gurin na tafi inda yara suke shiga mota sai kuma naji kira da muryar Hajiya Babba "Diyam, ki dawo nan tare zamu tafi dake" na juya kamar zanyi kuka na koma, sai naga sun doshi motar da yake tsaye a kusa da ita, anti amarya tace "Diyam shiga gaba mu sai mu zauna a baya" na tsaya kawai ina kallon su kamar in rufe su da duka har suka gama shiga, shima ya shiga seat din driver ya zauna ya tayar da motar, sai da suka sake yi min magana sannan na kama handle din kofar jishi a rufe ni kuwa na koma da baya na nade hannu na a kirji. Hajiya Yalwati ta leko. "Ki shigo mana Diyam, ke fa muke jira" nace "kofar a rufe take Hajiya" ina jin Hajiya Babba tana yi masa magana, ya dauke kai kamar bai jita ba sannan kuma bayan wajan minti daya sai ya bude lock din. Na bude na zauna a makale a bakin kofa ba tare dana ko kalli side din da yake ba.
A hanya naji Hajiya Babba tana yiwa kishiyoyinta bayani "kunsan halin Saghir da rashin son hayaniya, wai shi ba zai zauna a cikin gari ba saboda kar mutane su dame shi, nace to kai me kanne da yawa? Namiji tilo a cikin mata? Ai dole ko gari ka bari sai kannenka sunje gidan ka, shine Alhaji ya biye masa aka siya masa gidan a can wajen gari, unguwar tokarawa acan zasu zauna" a raina nace 'wato yadda zai samu damar kasheni hankali kwance' ni a lokacin ban ma san unguwar ba sai dai naga mun dau hanyar barin gari, sai da muka wuce 'yan kaba sannan muka sauka daga titi muka shiga unguwar dana lura kamar sabuwar unguwa ce. Tun daga nesa na gane gidan. A house fit for the only son of Alhaji Babba amma ko kadan banji kyan gidan ya burge ni ba. Mukayi packing kusan a tare dasu Murja, na fita na tafi gurin su muka shiga tare amma sai na zame na zagaya bayan gidan nayi zamana akan veranda r backdoor din gidan. Ina jiyo su suna ta hayaniya da iface ifacen su alamar suna cikin nishadi amma ko sha'awar inje inga gidan banyi ba, addu'a nake a raina kar Allah yasa ina da rabon ganin cikin gidan nan in dai a matsayin matar Saghir ce. Naji wata irin kewar Sadauki ta taso min, sau dubu gwara ace in zauna da Sadauki a gidan kasa me yoyo akan in zauna da Saghir a wannan gidan.
Kamshin turare naji, na daga kai sai na ganshi a tsaye yana kallon gefe da alama bai san ma ina gurin ba. Fuskar nan kamar an aiko masa da mutuwa. Nayi saurin share hawayen fuskata saboda bana son ko kadan yaga weakness dina ballantana ya kara rainani. Motsin da nayi ne yasa ya juyo ya kalli inda nake, sai kuma naga ya tako cikin gadara yazo gabana ya tsaye ya kara tamke fuska yace "ke! Me na gaya miki rannan? Ba zaki je ki gaya musu ba sai kin je kin daukowa kanki abinda ba zaki iya ba ko?" Na mike tsaye na karkade hijab dina na juya zan bar masa gurin, ya damko hijab dina ya juyo dani yace cikin barazana "ba dake nake magana ba?" Na zabga masa hararar da nasan ba'a taba yi masa irinta ba nace "su wadanda kake magana a kansu ai sunfi kowa sanin cewa bana sonka, sunfi kowa sanin ina da wanda nake so wanda kuma yake sona, asalima dan su raba ni dashi ne suke neman makalamin kai"
The Game Has Began
It is such a long episode ko?
[1/28, 10:58 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â? DIYAM â?
By
Maman Maama
Episode Twenty Eight: Destiny
Kafin mu cigaba please let us all take a moment and pray for Maryam Sanda and then pray for ourselves. Allah ya sa wannan hukuncin da aka yanke mata ya zamar mata alkhairi a duniya da kuma a lahirar ta, mu kuma Allah ya kare mu daga mummunar kaddara, Allah ya kare mu daga sharrin shaidan da sharrin zuciya, Allah yasa mu fi karfin zukatan mu a kodayaushe.
Bayan haka ina kira ga matan aure manyan mu da kananan mu, please idan kin tabbatar your marriage is not working, idan kin tabbatar kin je limit dinki na hakuri a gidan auren ki, please walk out of the marriage. Allah ya halatta saki for a reason, wani lokacin rabiwar tafi alkhairi akan cigaba da zaman. It is better a kiraki da bazawara then ki kasance in maryam sanda's shoes.
Sannan iyayen mu dan Allah ku dube mu da idon rahama, ku tausaya mana, dan Allah idan yarinya tazo gida tace ta gaji da zaman auren ta please ku bincika sosai, idan tana da gaskiya kuyi supporting dinta, kar ku tura yarku ga halaka, karku tura yarku zuwa wuta.
Now, let's continue with labarin Diyam maybe anan ma da akwai darasin da zamu dauka.
Da mamaki karara fuskarsa yake kallona, maybe bai taba tsammanin zan iya mayar masa da magana haka ba. Yace "ke? Kin san dawa kike magana kuwa? Ni din ne ma kike cewa za'a makala miki?" Na cigaba da kallon sa cikin ido duk a cikin kokari na na nuna masa cewa bana jin tsoronsa, amma zuciyata in banda lugude babu abinda take yi. Ya daga hannu da niyyar wanka min mari sai kuma ya kalli gidan inda hayaniya take fitowa daga tagogin sama, ya fahimci yana dukana zan tara masa jama'a dan haka sai ya dunkule hannunsa sannan ya sauke, ya nuna ni da dan yatsa yace "in kika sake kika shigo gidan nan sai na karya ki" na fusge hijab dina daga hannunsa nace "not today, kuma ni bani zan shiga gidan ka ba sai dai a shigo dani dan dole" na juya na tafi na barshi anan ina jin dadi a zuciyata, ashe dai Sadauki bai tafi da dukkan Strength din nawa ba, ko kuma maybe a time din wannan hug din ne yayi passing some of his strength and courage to me.
Muna komawa gida na wuce direct zuwa dakin inna, na gaisheta tana ta washe baki tace "kun dawo? Ya gidan?" Na tashi ina ninke hijab din dana cire nace "lfy lau" tace "lfy lau? Shikenan abinda zaki ce? Bayanin gidan zaki yi min inji dame dame aka saka kuma menene ba'a saka ba" nace "Inna ban sani ba nikam, ban shiga ciki ba a waje na zauna" nan fa takama fada, ni kuma nayi shiru har saida ta gama sannan nace "Inna yace inna shiga gidan sa sai ya kashe ni" sai ta girgiza kai tace "fada kawai yake yi, shima fushi yake yi saboda an matsa masa akan maganar nan, daga ke har shi ba kwaso amma abinda mu iyayenku muka hango ku ba zaku hango shi yanzu ba sai nan gaba zaku fahimta".