← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 112

Sashe 76

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Na sunkuyar da kaina ina lissafa fingers dina shi kuma yana kallona yace "my God, you really are beautiful" na dago na kalle shi and he smiled. Nace "ga abinci nan inji Inna" yace "thank you. Dama kinga azumi nake yi" nayi shiru ina tunanin ban taba ganin Saghir yana azumi ba in ba Ramadan ba. Sai yace "ya kika ga sabon gida na? Yayi kyau?" Na kalli surrounding din gurin nace "nan ba gidan ka bane ba Saghir. I am going to get you out of here" yayi dariya yace "how? Zaki saka ni a jaka ne mu tafi gida tare?" Nayi shiru. Yace "nasan maybe, just maybe, zaki iya convincing your lover boy ya yafe min kudinsa, but zaki iya kamo Kabir ki danka shi a hannun hukuma ki saka yayi confessing cewa shi yayi framing dina?" Nace "maybe, just maybe, zan iya convincing Sadauki ya yafe maka, sannan in saka shi yayi amfani da power dinsa to get you out. Nigeria ce fa, with few phone calls an gama komai".

Yayi dariya "not even in your dreams. Ba zaiyi ba. Mutumin da yake son ganin baya na ta yaya zai taimaka min?" Nayi shiru, nima kaina bansan ta inda zan bullowa wannan lamari ba but i am going to try.

Yace "I really did mess up ko? Nayi messing up auren mu. It would have been a great one" nace "not 'you' but 'we'. Tare muka hadu muka rusa auren mu. Ina fatan kuma zaka yafe min my part of the mess" yace "oh, you mean the closed doors ko?" Nayi murmushi. Na juya hannunsa yace "na yafe" nace "thank you".

Sai ya saka hannu a aljihu ya fito da takardu guda biyu yana kallona sarcastically yace "ya sunan ki ma? Ke ce Halima ko kece Fauziyya?" Bance komai ba sai ya miko min daya, naga sunana baro baro a jiki na bude na karanta

Ni Saghir Muhammad Kollere na saki matata Halima Usman Kollere saki daya, in ta samu miji tayi aure

Na dago ina kallonsa yace "daya ne ba yawa, in kika hada da wancan sun zama biyu kenan. Ni kuma na rike daya a gurina with hope that maybe, just maybe, zaki zauna ki jira ni" nayi murmushi yace "not even in my weirdest dream ko? I will just have to keep hoping".

Mutumin daya rako shi ya matso yace "time up" na gyada kaina na mike kamar zan tafi sai kuma na dawo na tsaya a gabansa nace

"For raping me, na yafe maka. For the twins, na yafe maka. For everything, na yafe maka. And I am going to get you out of here"

Yayi murmushi yace "thank you. Goodbye Halima".

Sai na juya da sauri na fita daga gurin, na kuma fita daga cikin prison din, hannuna rike da takarda ta.

Na fara tafiya a kafa ina jin iskar yanayin damina tana ratsani. Wani abu naji ya yaye daga ƙwaƙwalwa ta. I felt a sense of freedom wanda rabon da inji shi tun ranar da aka aura min Saghir. Hatta hanjin cikina ji nayi yana warwarewa tamkar da a nannade yake a guri daya, wani abu daya tokare a makogwarona naji ya sauka at last ina shaƙar numfashi freely.

And I decided that I am going to do the right thing.
[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Fifty Seven: Moving On

A hankali nake tafiya, enjoying my own company, feeling as free as a bird. Wannan feeling din da banji ba lokacin da Saghir yayi min sakin farko sai yanzu nake jinsa. Nayi murmushin da ya shiga har cikin zuciyata sannan a hankali na fara tariyo rayuwar auren mu da Saghir a kaina.

Shi dai Saghir, babban abinda yayi dooming rayuwar sa har ya kai shi ga stage din da yake ciki a yanzu shine rashin tarbiyya. Makauniyar soyayyar da iyayensa suka nuna masa tun yana jariri ita ce silar komai. Sai ya taso a matsayin sangartacce, mai son kansa kuma marar yawo saboda bai san yadda zaiyi ya kula da kannasa ba kwata kwata ballantana har ya kula wani, that including su kansu iyayen nasa. Rashin yawon sa shine ya bawa Sadauki da kuma Kabir damar kai shi inda yake a yanzu.

Na tuno ranar daya ce min bararoji a palon Hajiya, na tuno sanda ya shigo daki a gaban Inna yace baya sona, na tuno abinda ya faru a first night din mu da kuma abinda ya biyo baya, na tuno haihuwar twins, zama na a gida da kuma komawa ta gidansa. Inda ace zan zauna zan iya lissafa sau nawa muka yi magana ni shi inus our first year of marriage. Har zuwa haihuwar Subay'a bata chanja zani ba. Na tuno da yawan comments din da yake yi akaina cewa bani da body parts din daya ke so a gurin mace, year after year, then suddenly lokaci daya ya chanja after ya gama gasa ni for about seven years sai kuma ya dawo yana bani kulawa always commenting on my beauty and the so called body parts din daya ke so wadanda a lokacin na fara developing dinsu. A duk lokacin da naga yana wannan care da comments din nasan inda maganar zata kare, his bed. I remember yadda yake yawan comment cewa I tasted different than sauran matan da yake sharing bed dinsa dasu. And then he said he loves me.

But that got me thinking, it that really love? I mean zaka iya cutar da wanda kake so? Ka dake shi ka aibatashi a gaban mutane ka aibata iyayensa masu rai da marasa rai sannan kace 'you are really beautiful' ka ja shi zuwa gadonka? It that love or something else?

Duk wanda yace baya sonka, ya wulakanta ka a lokacin da baka da physical appearance din daya ke so, sai daga baya kuma daka samu sannan yazo yake kulaka, to me that is not love, that is lust.

Nasan so kuma I don't think I can hurt wanda nake so intentionally. Ko a gurin da ake aibata shima ba zan iya zama ba ballantana ni inyi da kaina. In na bata masa ransa kuwa to tabbas akan wani abu ne da nasan is for his own good. Kamar abinda na kudurce a raina cewa ina so yayi.

A tsakar gida na tarar da Inna da Asma'u suna ta gyaran gida saboda tashin su Maman Iman shekaran jiya. Na gaida ta sannan na mika mata takardar da Saghir ya bani na shige daki, ina jinta ta saka Asma'u ta karanta mata. Sai na zauna a gaban kujerar da Subay'a take kwance a kai ina kallonta a raina ina lissafin whats next a rayuwar mu ni da ita, Allah ne kadai masani amma ni nasan zanyi duk abinda ya kamata inyi a matsayi na na uwa dan ganin cewa ta samu farin ciki koda kuwa hakan yana nufin yin gibi ga nawa farin cikin. The first thing da zanyi shine in mayar da ita school, already tayi missing term guda gashi har anyi hutu ana shirin komawa sabon session. Dan haka na yanke shawarar nema mata school a arear gidan mu in saka ta wadda nasan Inna zata iya biya dan ni koboless nake a yanzu, hatta kudin recharge card ma bani akeyi.

Inna ta shigo ta zauna tana kallona da takardar a hannunta tace "na kira Hajiya Yalwati na gaya mata, nace ta gaya wa su Alhaji" na gyada kai kawai, sai kuma tace "Allah yasa hakan shi yafi miki alkhairi Allah kuma yasa karshen wahalar ki kenan" nace "ameen Inna. Nagode".

Washegari da wuri Asma'u ta fita saboda tana ta harkar neman admission, ina jinsu suna waya da yayanta da sassafe a raina nace "kaga masu business trip". Bayan ta fita nima na fita naje nayi mana register ni da Subay'a a islamiyyar bayan layin mu wadda ake yi safe da yamma. Sai a lokacin nayi dana sani dana yi jamb din nima maybe da yanzu nima ina neman admission din amma yanzu ya wuce ni sai next year. Bayan na dawo ne na tarar da bakuwa a palo tana jirana. Fauziyya. Sai naga duk ta chanja duk babu gayun nan, ga hijab a jiki, the first time da naga Fauziyya da hijab. Daga yanayin fuskarta na gane itama ta karbo tata takardar sai na maze muka gaisa tana ta yiwa Subay'a wasa, ni kuma sai na kira Subay'a na aike ta gurin Inna dan yanzu sam bana son yin hira a gabanta.
Chapter 76 · 0% Book details