Sashe 89
Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ta lura Murjanatu duk ta daga hankalinta sai ta zaunar da ita tace "kar ki wani damu kanki da fushinsa, zai sauko na gaya miki ki barni da shi kawai" Murjanatu tace "baki san halinsa ba, zai iya raba ni da makarantar nan fa wallahi. Akwai abinda ya taba yi min a gida Canada akan wani saurayi na an gaya masa bad abubuwa akan sa sai yace min kar in kara kula shi ni kuma na cigaba da kulashin. Ashe yasa a saka masa ido a kaina sai gashi an tura masa da videon mu tare a gurin cin abinci. Ba wani abin muke ba kawai muna hirar mu muna dariya. Akan haka ya karbe wayata kuma yayi grounding dina a gida for three months ko kofar gida bana fita. Papa da Mama kuma suka biye masa yanzu ma kuma nasan duk abinda yace biye masa zasuyi" Diyam tace "ba zai ce komai ba, ki barni dashi".
Suka duba suka tabbatar suna da abubuwan da suke bukata, abinda basu da shi kuma sai sukayi order online da niyyar a kawo musu da sassafe. Sai kuma suka shiga website din airport suka duba flights schedules na gobe, anan suka ga time din da jirgi zai sauka from Nigeria. Sai yamma. Wannan yasa suka yi baccinsu sosai sannan suka tashi a tsakane suka yi komai tare har da Judith itama ta taya su, suka ci abincin su sannan suka yi wanka aka zauna kuma yin kwalliya a shafa wancan a goga wannan a ja wancan suna ta rigima har aka gama sannan aka yi dressing aka kuma bi da turare. Murjanatu ce ta dauko hijab da kanta ta bawa Diyam tace "gwara ki saka tun kafin yayi ball damu tun daga airport har gida".
Tare suka tafi airport din a mota, suka bar Judith a gida tana gyara musu gidan. A hanya duk sukayi shiru kowa tana lissafe lissafen ta sannan Diyam tace "Murjanatu a tunanin ki ta yaya Aliyu yasan ina kula Bassam?" Murjanatu ta daga kafada tace "yaya Aliyu ne fa, ya iya bincike ta karkashin kasa I guess wani ya saka ya saka masa ido akan mu. The guy might have saw you two together and reported to him" Diyam tayi shiru tana tunani, she will have to talk to him about that, hakan kamar rashin yarda ne. Murjanatu ta katse mata tunanin ta ta hanyar cewa "there is nothing between the two of you, is there?" Diyam ta harare ta tace "in kina son shi just say so, sai in hada ku" Murjanatu ta tabe baki tace "bai yi min ba, he is definitely not my type. Daga ganin sa nasan lady's man ne, Allah kadai yasan yawan yammatan sa" Diyam tayi dariya tace "wai dama kura tana iya cewa da kare maye? Ke ma Allah ne kadai yasan yawan samarinki" Murjanatu ta yi murmushi ta fara bata labarin new catch din da tayi a school last week.
Suna tsaye suna jira jirgin ya iso, Diyam tana ta jujjuya hannun ta feeling nervous dan bata san da wacce zai zo ba sannan kuma ga zuciyarta da take neman betraying dinta saboda dokan tuwa da tayi gurin son ganinsa after almost three months of not seeing him. And then suddenly sai idonta ya sauka a kansa, yayi kyau sosai fuskarsa tayi fes gashinsa na fulani da sajensa sun kwanta lufluf suna daukan ido. The freshness of his dark skin alone zai tabbatar maka da cewa he is taking good care of his body, yanayin takunsa kuma da posture dinsa sun nuna yawan ziyarar da yake kaiwa gym. Their eyes locked, and everything in her stopped except bugun zuciyarta da yayi doubling. He walk straight to gabanta ya tsaya one hand inside pocket, his expression unreadable yace "hello Madam".
Ta bude baki zatayi magana amma sai taji duk rehearsal din da tayi na abinda zata ce masa ya gudu ya barta. Yayi mata kwarjini da yawa, and the fact that he called her madam have added to that. Sai ya dauke idonsa daga kanta ya mayar da dubansa kan Murjanatu da take kusa da ita tana mishi murmushin dole, suna hada ido tace "sannu da zuwa yaya, ya flight din?" "Fine" yace mata in short sannan ya zagaye su yayi hanyar fita, Murjanatu taja hannun Diyam da sauri suka bishi a baya. Suna fita suka ga cab tayi packing a gabansa Murjanatu tayi saurin cewa "ga mota munzo da ita fa" ya juyo yana kallon Diyam yace "thank you" sai ya shige suka ja suka barsu a wajen.
Murjanatu ta juyo tana kallon Diyam tace "you kept quiet, me yasa zaki yi shiru?" Diyam tace "he called me Madam. Kin san kuwa yadda nake jin haushi in yace min Madam?" Murjanatu tayi dariya tace "to menene na jin haushi? In yace miki Madam sai kice masa Sir, ba shi kenan ba? Now we have to follow him kuma" suka shiga mota suka bi bayan cab din data dauke shi but sai suka ga sunyi wata hanyar daban ba hanyar gidan su ba, Diyam zata yi magana Murjanatu tace "gidan Papa zashi. Inda muke sauka in munzo gari" sai Diyam ta juya kan motar suka yi hanyar gidansu. Murjanatu tace "ba binsa zamuyi ba?" Diyam tace "we cooked for him, dole kuma yaci abincin da muka dafa".
Suna zuwa gidan Murjanatu ta shiga ta hado kan girkin da suka yi masa ta jera a babban basket sannan ta dawo motar suka kama hanyar wajen gari inda anan ne gidan yake. Suna packing Diyam ta tsaya tana kallon gidan a ranta tace "wow, da gaske dai Umar Mustapha Abatcha ne ya haifi Sadauki" ba mutane a gidan sai security daya bude musu gate suka shigo, amma komai na gidan tsaf yake daga alama ana zuwa aba gyaran gidan akan kari. Kofar da suka hango a bude suka dosa, suka shiga wani palo madaidaici Diyam tana iyakacin kokarinta na ganin bata yi kauyanci ba. A kan dining suka hango shi yana zaune yana kallon kofar da suka shigo. He kept his eyes on them har suka karaso Murjanatu ta ajiye basket din hannunta ta gaishe shi ya amsa tare da tambayarta karatu, sai kuma tace da Diyam bara taje ta dubo wani abu a cikin gidan.
Sai data fita sannan Diyam ta dauke idonta daga kansa ta sauke kan wata baturiya sanye da apron da hular cooks tana ta jera abinci akan dining table din gabansa. Diyam ta tako ta karaso gurin tana kallon baturiyar tace "thank you, I will take it from here" sai matar ta juya tana kallon Sadauki shi kuma ya yi mata alamar ta tafi da hannunsa sai ta juya ta bar gurin. Diyam tabi bayanta da kallo tana jin haushinta ba tare da matar tayi mata komai ba. Sai kuma ta fara tattare abincin kan table din tana ajiyewa gefe sannan ta dauko basket din da suka shigo dashi ta dora akan table din ta fito da abincin ciki ta jejjera sannan ta jawo kujera kusa dashi ta zauna. Tunda ta fara yayi folding hannayensa yake kallonta har ta gama ta zauna sannan ta jawo plate gabanta tace "banyi maka tuwon da kake so ba saboda bani da kayan hadi. Amma nayi maka something da nake tunanin zaka so" still idonsa akanta yace "how is he" ta gane maganar da yake amma sai ta cigaba da hada abincin ta, carelessly tace "how is who?" Sai ta debo abincin a spoon ta kawo bakinsa tace "ha" and she saw his lips curved in a smile amma sai ya juya fuskarsa gefe kar ta gani sai ta sake bin bakinsa da spoon din tace "ha muga ni" sai ya langwabar da kai sannan a hankali ya bude mata bakin ta saka masa abincin a ciki sai ta zauna tana kallon sa with wide opened eyes shi kuma yana taunawa a hankali sannan tace "please tell me yayi dadi. I spent hours ina shirya maka abincin nan kamar yadda nayi spending hour ina yi maka kwalliya amma gashi nan ko yaba wa ba kayi ba" ta karashe maganar kamar zata yi kuka.
A hankali yace "waye yace miki ban yaba ba?" Ta turo baki tace "you called me Madam, kuma kaki shiga mota ta" ya danyi murmushin daya tsaya a iyakacin idonsa yace "to ba Madam din bace ba ke?" Tace "I am not Madam, in ka kara gaya min kuma nima Sir zan ke ce maka" and his smile widen to his lips. Ta sake dauko wata lomar ta kuma cewa "ha" ya bude ta saka masa yana ci ya kuma cewa "how is he?" Ta gyara fuskarta zuwa serious one tace "kana magana akan Bassam ko?" Ya daga kafada yace "bansan sunansa ba and I don't want to know" tace "he was fine as of yesterday, bansan ya yake yau ba. Kamar yadda bansan me yasa kake wani tunani akan sa ba. He is just my friend, department din mu daya muna lectures tare and he is a Nigerian" ya bata fuska yace "shi yasa kuke cin abinci tare?"
Suka duba suka tabbatar suna da abubuwan da suke bukata, abinda basu da shi kuma sai sukayi order online da niyyar a kawo musu da sassafe. Sai kuma suka shiga website din airport suka duba flights schedules na gobe, anan suka ga time din da jirgi zai sauka from Nigeria. Sai yamma. Wannan yasa suka yi baccinsu sosai sannan suka tashi a tsakane suka yi komai tare har da Judith itama ta taya su, suka ci abincin su sannan suka yi wanka aka zauna kuma yin kwalliya a shafa wancan a goga wannan a ja wancan suna ta rigima har aka gama sannan aka yi dressing aka kuma bi da turare. Murjanatu ce ta dauko hijab da kanta ta bawa Diyam tace "gwara ki saka tun kafin yayi ball damu tun daga airport har gida".
Tare suka tafi airport din a mota, suka bar Judith a gida tana gyara musu gidan. A hanya duk sukayi shiru kowa tana lissafe lissafen ta sannan Diyam tace "Murjanatu a tunanin ki ta yaya Aliyu yasan ina kula Bassam?" Murjanatu ta daga kafada tace "yaya Aliyu ne fa, ya iya bincike ta karkashin kasa I guess wani ya saka ya saka masa ido akan mu. The guy might have saw you two together and reported to him" Diyam tayi shiru tana tunani, she will have to talk to him about that, hakan kamar rashin yarda ne. Murjanatu ta katse mata tunanin ta ta hanyar cewa "there is nothing between the two of you, is there?" Diyam ta harare ta tace "in kina son shi just say so, sai in hada ku" Murjanatu ta tabe baki tace "bai yi min ba, he is definitely not my type. Daga ganin sa nasan lady's man ne, Allah kadai yasan yawan yammatan sa" Diyam tayi dariya tace "wai dama kura tana iya cewa da kare maye? Ke ma Allah ne kadai yasan yawan samarinki" Murjanatu ta yi murmushi ta fara bata labarin new catch din da tayi a school last week.
Suna tsaye suna jira jirgin ya iso, Diyam tana ta jujjuya hannun ta feeling nervous dan bata san da wacce zai zo ba sannan kuma ga zuciyarta da take neman betraying dinta saboda dokan tuwa da tayi gurin son ganinsa after almost three months of not seeing him. And then suddenly sai idonta ya sauka a kansa, yayi kyau sosai fuskarsa tayi fes gashinsa na fulani da sajensa sun kwanta lufluf suna daukan ido. The freshness of his dark skin alone zai tabbatar maka da cewa he is taking good care of his body, yanayin takunsa kuma da posture dinsa sun nuna yawan ziyarar da yake kaiwa gym. Their eyes locked, and everything in her stopped except bugun zuciyarta da yayi doubling. He walk straight to gabanta ya tsaya one hand inside pocket, his expression unreadable yace "hello Madam".
Ta bude baki zatayi magana amma sai taji duk rehearsal din da tayi na abinda zata ce masa ya gudu ya barta. Yayi mata kwarjini da yawa, and the fact that he called her madam have added to that. Sai ya dauke idonsa daga kanta ya mayar da dubansa kan Murjanatu da take kusa da ita tana mishi murmushin dole, suna hada ido tace "sannu da zuwa yaya, ya flight din?" "Fine" yace mata in short sannan ya zagaye su yayi hanyar fita, Murjanatu taja hannun Diyam da sauri suka bishi a baya. Suna fita suka ga cab tayi packing a gabansa Murjanatu tayi saurin cewa "ga mota munzo da ita fa" ya juyo yana kallon Diyam yace "thank you" sai ya shige suka ja suka barsu a wajen.
Murjanatu ta juyo tana kallon Diyam tace "you kept quiet, me yasa zaki yi shiru?" Diyam tace "he called me Madam. Kin san kuwa yadda nake jin haushi in yace min Madam?" Murjanatu tayi dariya tace "to menene na jin haushi? In yace miki Madam sai kice masa Sir, ba shi kenan ba? Now we have to follow him kuma" suka shiga mota suka bi bayan cab din data dauke shi but sai suka ga sunyi wata hanyar daban ba hanyar gidan su ba, Diyam zata yi magana Murjanatu tace "gidan Papa zashi. Inda muke sauka in munzo gari" sai Diyam ta juya kan motar suka yi hanyar gidansu. Murjanatu tace "ba binsa zamuyi ba?" Diyam tace "we cooked for him, dole kuma yaci abincin da muka dafa".
Suna zuwa gidan Murjanatu ta shiga ta hado kan girkin da suka yi masa ta jera a babban basket sannan ta dawo motar suka kama hanyar wajen gari inda anan ne gidan yake. Suna packing Diyam ta tsaya tana kallon gidan a ranta tace "wow, da gaske dai Umar Mustapha Abatcha ne ya haifi Sadauki" ba mutane a gidan sai security daya bude musu gate suka shigo, amma komai na gidan tsaf yake daga alama ana zuwa aba gyaran gidan akan kari. Kofar da suka hango a bude suka dosa, suka shiga wani palo madaidaici Diyam tana iyakacin kokarinta na ganin bata yi kauyanci ba. A kan dining suka hango shi yana zaune yana kallon kofar da suka shigo. He kept his eyes on them har suka karaso Murjanatu ta ajiye basket din hannunta ta gaishe shi ya amsa tare da tambayarta karatu, sai kuma tace da Diyam bara taje ta dubo wani abu a cikin gidan.
Sai data fita sannan Diyam ta dauke idonta daga kansa ta sauke kan wata baturiya sanye da apron da hular cooks tana ta jera abinci akan dining table din gabansa. Diyam ta tako ta karaso gurin tana kallon baturiyar tace "thank you, I will take it from here" sai matar ta juya tana kallon Sadauki shi kuma ya yi mata alamar ta tafi da hannunsa sai ta juya ta bar gurin. Diyam tabi bayanta da kallo tana jin haushinta ba tare da matar tayi mata komai ba. Sai kuma ta fara tattare abincin kan table din tana ajiyewa gefe sannan ta dauko basket din da suka shigo dashi ta dora akan table din ta fito da abincin ciki ta jejjera sannan ta jawo kujera kusa dashi ta zauna. Tunda ta fara yayi folding hannayensa yake kallonta har ta gama ta zauna sannan ta jawo plate gabanta tace "banyi maka tuwon da kake so ba saboda bani da kayan hadi. Amma nayi maka something da nake tunanin zaka so" still idonsa akanta yace "how is he" ta gane maganar da yake amma sai ta cigaba da hada abincin ta, carelessly tace "how is who?" Sai ta debo abincin a spoon ta kawo bakinsa tace "ha" and she saw his lips curved in a smile amma sai ya juya fuskarsa gefe kar ta gani sai ta sake bin bakinsa da spoon din tace "ha muga ni" sai ya langwabar da kai sannan a hankali ya bude mata bakin ta saka masa abincin a ciki sai ta zauna tana kallon sa with wide opened eyes shi kuma yana taunawa a hankali sannan tace "please tell me yayi dadi. I spent hours ina shirya maka abincin nan kamar yadda nayi spending hour ina yi maka kwalliya amma gashi nan ko yaba wa ba kayi ba" ta karashe maganar kamar zata yi kuka.
A hankali yace "waye yace miki ban yaba ba?" Ta turo baki tace "you called me Madam, kuma kaki shiga mota ta" ya danyi murmushin daya tsaya a iyakacin idonsa yace "to ba Madam din bace ba ke?" Tace "I am not Madam, in ka kara gaya min kuma nima Sir zan ke ce maka" and his smile widen to his lips. Ta sake dauko wata lomar ta kuma cewa "ha" ya bude ta saka masa yana ci ya kuma cewa "how is he?" Ta gyara fuskarta zuwa serious one tace "kana magana akan Bassam ko?" Ya daga kafada yace "bansan sunansa ba and I don't want to know" tace "he was fine as of yesterday, bansan ya yake yau ba. Kamar yadda bansan me yasa kake wani tunani akan sa ba. He is just my friend, department din mu daya muna lectures tare and he is a Nigerian" ya bata fuska yace "shi yasa kuke cin abinci tare?"