Sashe 12
Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ranar nan ya dawo daga makaranta na tafi da guduna na rungume shi ina masa oyoyo, ya ciro alawar da ya siyo min da kudin taran sa, wadda yasan in dai ya shigo babu ita to sai nayi masa rigima, na karba nace "Nagode Sadauki" ya kamo kunnena yace "daga yau hamma Sadauki suna na" na gyada kai ina murza kunnen da yaja, Ummah ta harare shi tace "sai son girma kamar gwambo, ga kuma mugunta" ni dai na wuce dakin Inna da sauri na kai mata sweet din nace ta bude min. Ta karba tana tambayata "waye ya baki?" Nace "hamma Sadauki ne" ta kamo kunnena da sauri tana daga muryarta yadda Ummah zata ji daga waje tace "hamma wa? A gidan uban wa ya zama hammanki? Babu hadin danga da garafuni kar in kara jin kince masa hamma" na saka kuka saboda zafin da kunnen yake min nace "na daina Inna" ta sake ni na fita da gudu gurin Ummah ina share hawaye na, ta dauke ni ta dora akan cinyarta ta bude min alawar tana rarrashina. Daga ranar ban kuma cewa Sadauki hamma ba shima kuma bai kuma cewa in gaya masa ba
Shekarar da aka saka ni primary Sadauki ya shiga secondary, dan haka a lokacin Baffa ya siya masa keke yake zuwa akai. Ni kuma Baffa ne da kansa yake kaini a motarsa tunda makarantar mu babu nisa kafin ya fita amma ranar nan sai na saka rigima nace ni a keken Sadauki zan ke tafiya, nan take Sadauki yace "Baffa ka barta, kaga hanya daya ne sai in ajiyeta in an taso kuma in biya in dauke ta" Inna tace "kaji mugunta, salon kake kayar da ita a hanya kullum? In banda mugunta ga motar ubanta sai ace ta hau keke? To ba zata hau din ba" na makale kafafa ina kakalo hawaye, Baffa ya tsaya yana kallon Inna saboda yaji zafin maganar ta amma saboda muna gurin sai kawai yace "bishi ku tafi, Allah ya kiyaye hanya" Ummah tace "ka bi a hankali, kar kaje kana wannan rawar kan naka ka jefa ta a kwata" ni kuwa sai tsalle da murna, ya dora ni a gaban sa ya saka na rike kan keken sannan ya taka keken muka tafi. Muna barin layin mu na saki kan keken na fara kokarin mikewa tsaye, ya rike ni da hannu daya yace "ki zauna Diyam, zaki fadi fa" na ture hannunsa "ka tsaya kaga abinda zamuyi, irin na titanic, nice rose kaine jack" na mike na bubbude hannayena, ai kuwa kafin yayi managa na zame zan fadi, garin rikeni shima ya biyo ni sai gamu a kasa a kan kwalta, guiwowina duk sun daddauje goshina ma haka. Na dage kuwa tun karfina na ringa zunduma ihu, yayi rarrashin duniyar nan naki inyi shiru, haka ya dauko ni da hannu daya ya jawo keken da daya hannun muka taho gida.
A bakin gate muka tarar da Baffa yana shirin fita. Yana ganin mu ya taho da saurin sa ya karbe ni a hannun Sadauki ya dora ni a saman mota yana duba ciwon da naji. Tun kafin Sadauki ya bada labarin abin da ya faru sai ga Inna ta jiyo kuka na ta fito da sauri tana cewa "ai dama sai da na fada, yaron nan babu komai a zuciyarsa sai zallah mugunta, gashi nan yaje ya jefar min da yarinyar ya cuce ni" Baffa ya juya kanta shima da nasa fadan sukayi tayi, basu san sanda Ummah ta fito ta dauke ni ta wankemin ciwon da naji ba ta chanza min kaya sai ji sukayi tace "baban Diyam ko zaka kaita chemist a duba ciwon sosai?" Baffa ya juyo yana kallonta yace "Allah yayi miki albarka Zainab" tayi murmushi tace "ameen, Nagode". Sannan ta cewa Sadauki "kaima sai ka bisu a duba hannunka" sai a lokacin duk muka lura cewa shima yaji ciwo a hannunsa yana ta jini, yayi saurin nuna jarumta ta hanyar cewa "babu komai" amma Baffa ya tilasta masa sai da ya bimu.
Na jima da wannan tabon a goshina, duk wanda ya tambaye ni sai ince "Sadauki ne ya kayar dani a keke".
Writing......
[1/10, 9:56 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â¤ï¸ DIYAM â¤ï¸
By
Maman Maama
Episode Twelve: My Brother, My Friend.
"Diyam, ba zaki cigaba da cin abincin nan ba sai nazo ko?" Na daga kai ina kallon Inna da take zazzare min ido cike da barazana. Na debi shinkafa a chokali na kai bakina ina taunata da kyar saboda koshin da cikina yayi ji nake kamar zanyi amai. Na shawabe fuska "Inna wallahi na koshi, nasha tea, naci bread, naci kwai, bazan iya cin shinkafa ba kuma amai zanyi" tace "kiyi aman, sai ki zo ki cigaba da ci" na kalli kofa da sauri saboda motsin mutum dana gani, ta gefen labule na hango Sadauki sanye da uniform dinsa, muna hada ido yayi min alamar in taho da hannunsa, na ture abincin na sunkuci jakata zan fita Inna ta fizgoni ta dangwarar akan kujera tace "in kika fita daga dakin nan sai na yanke kafafuwanki" ta harari kofa tace "bakin munafuki, babu inda zakuje tare" ta kara dangwara min kwanon shinkafa a cinyata.
Muryar Baffa na jiyo a tsakar gida "kai kai kai, Sadauki wai baku tafi ba har yanzu? Ai kun makara, ina Diyam din?" Nayi saurin ajiye kwanon amma hararar da Inna ta jeho min yasa na dauka na cigaba da rikewa. Baffa ya leko yace "ke Diyam, ki fito ku tafi mana kin makarar dashi zaki sa a dake shi" Inna tayi charaf tace "ya tafi kawai kar a hukunta shi a makarantar su. Diyam bata gama karyawa ba" na ajiye kwanon nace "na gama Baffa, tun dazu na gama Inna ce ta hanani fitowa" na zagaya ta gefenta na fice daga dakin da sauri na rungume sadauki shi kuma ya dauke ni ya dora akan kekensa muka tafi.
Haka mukayi ta fama kullum ba fashi, kullum sai inna tayi ƙoƙarin hanani bin Sadauki ni kuma sai na nace na bishi. Shi zai kaini har class dinmu yaga na shiga sannan ya tafi tasa makarantar. A lokacin dana kara girma kuma sai ya daina dorani a keken sai dai mu tafi a kafa yana jan kekensa a hannu har sai ya kaini sannan shi kuma ya hau ya tafi tasa. Haka islamiyya ma tare za muje, in asma'u ta biyo ni sai in korata ince tabi yaran makotanmu. Sadauki shine yayana, shine abokina, shine kawata, shine abokin shawarata, duk da cewa a lokacin akwai yarinta sosai dan haka duk shawarar ta shirme ce, shima kuma tunda ba wani girmata yayi sosai ba haka zai bani amsar shiririta.
Duk kawayena, na boko dana islamiyya sun san Sadauki, wadda bata sanshi a fuska ba kuwa to tabbas tasan sunansa saboda da wahala in muna hira in iya hada sentence guda ba tare da sunan sadauki ya fito a ciki ba. Duk kuwa sanda wani a ajin mu ko ajin gaba damu yaci zalina ko na tsokani wani ya dake ni to tabbas sai jikinsa ya gaya masa in ya shiga hannun Sadauki, wannan yasa ake shayin tabani ko a yaran unguwa sai dai in na tsokani yaro yayi hakuri dan dole dan sun san cewa sadauki ƙashi daya ne dashi.
Bashi da surutu sam, he is a good listener rather than a talker, ko a gida in dai kaji yana hira to dani ne, ko da Baffa, amma ko Ummah basu cika zama suyi doguwar hira ba. Yana da zuciya da fada in an taba shi ko an taba ni, amma ni din ko daga min murya baya iyayi balle yayi min fada. Kuma duk zuciyar Sadauki, bai taba daga kai ya kalli Inna in tana gayawa Ummah magana ba, sai dai ka gani a fuskarsa cewa ransa ya baci amma ba zai mayar mata ba. Yana da kazar kazar sosai kuma baya zama guri daya, in har baya makaranta to yana gareji in kuma baya can to yana gida yana aiyuka, zai share gidan mu tas ya gyara wa Baffa dakinsa ya wanke masa mota. Watarana nace masa "Sadauki kai baka gajiya ne? Ka kwanta ka huta mana" Sai yace "wa kika taba gani yayi achieving wani abu a kwance? In kana son wani abu you have to work hard to earn it".
Shekarar da aka saka ni primary Sadauki ya shiga secondary, dan haka a lokacin Baffa ya siya masa keke yake zuwa akai. Ni kuma Baffa ne da kansa yake kaini a motarsa tunda makarantar mu babu nisa kafin ya fita amma ranar nan sai na saka rigima nace ni a keken Sadauki zan ke tafiya, nan take Sadauki yace "Baffa ka barta, kaga hanya daya ne sai in ajiyeta in an taso kuma in biya in dauke ta" Inna tace "kaji mugunta, salon kake kayar da ita a hanya kullum? In banda mugunta ga motar ubanta sai ace ta hau keke? To ba zata hau din ba" na makale kafafa ina kakalo hawaye, Baffa ya tsaya yana kallon Inna saboda yaji zafin maganar ta amma saboda muna gurin sai kawai yace "bishi ku tafi, Allah ya kiyaye hanya" Ummah tace "ka bi a hankali, kar kaje kana wannan rawar kan naka ka jefa ta a kwata" ni kuwa sai tsalle da murna, ya dora ni a gaban sa ya saka na rike kan keken sannan ya taka keken muka tafi. Muna barin layin mu na saki kan keken na fara kokarin mikewa tsaye, ya rike ni da hannu daya yace "ki zauna Diyam, zaki fadi fa" na ture hannunsa "ka tsaya kaga abinda zamuyi, irin na titanic, nice rose kaine jack" na mike na bubbude hannayena, ai kuwa kafin yayi managa na zame zan fadi, garin rikeni shima ya biyo ni sai gamu a kasa a kan kwalta, guiwowina duk sun daddauje goshina ma haka. Na dage kuwa tun karfina na ringa zunduma ihu, yayi rarrashin duniyar nan naki inyi shiru, haka ya dauko ni da hannu daya ya jawo keken da daya hannun muka taho gida.
A bakin gate muka tarar da Baffa yana shirin fita. Yana ganin mu ya taho da saurin sa ya karbe ni a hannun Sadauki ya dora ni a saman mota yana duba ciwon da naji. Tun kafin Sadauki ya bada labarin abin da ya faru sai ga Inna ta jiyo kuka na ta fito da sauri tana cewa "ai dama sai da na fada, yaron nan babu komai a zuciyarsa sai zallah mugunta, gashi nan yaje ya jefar min da yarinyar ya cuce ni" Baffa ya juya kanta shima da nasa fadan sukayi tayi, basu san sanda Ummah ta fito ta dauke ni ta wankemin ciwon da naji ba ta chanza min kaya sai ji sukayi tace "baban Diyam ko zaka kaita chemist a duba ciwon sosai?" Baffa ya juyo yana kallonta yace "Allah yayi miki albarka Zainab" tayi murmushi tace "ameen, Nagode". Sannan ta cewa Sadauki "kaima sai ka bisu a duba hannunka" sai a lokacin duk muka lura cewa shima yaji ciwo a hannunsa yana ta jini, yayi saurin nuna jarumta ta hanyar cewa "babu komai" amma Baffa ya tilasta masa sai da ya bimu.
Na jima da wannan tabon a goshina, duk wanda ya tambaye ni sai ince "Sadauki ne ya kayar dani a keke".
Writing......
[1/10, 9:56 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: â¤ï¸ DIYAM â¤ï¸
By
Maman Maama
Episode Twelve: My Brother, My Friend.
"Diyam, ba zaki cigaba da cin abincin nan ba sai nazo ko?" Na daga kai ina kallon Inna da take zazzare min ido cike da barazana. Na debi shinkafa a chokali na kai bakina ina taunata da kyar saboda koshin da cikina yayi ji nake kamar zanyi amai. Na shawabe fuska "Inna wallahi na koshi, nasha tea, naci bread, naci kwai, bazan iya cin shinkafa ba kuma amai zanyi" tace "kiyi aman, sai ki zo ki cigaba da ci" na kalli kofa da sauri saboda motsin mutum dana gani, ta gefen labule na hango Sadauki sanye da uniform dinsa, muna hada ido yayi min alamar in taho da hannunsa, na ture abincin na sunkuci jakata zan fita Inna ta fizgoni ta dangwarar akan kujera tace "in kika fita daga dakin nan sai na yanke kafafuwanki" ta harari kofa tace "bakin munafuki, babu inda zakuje tare" ta kara dangwara min kwanon shinkafa a cinyata.
Muryar Baffa na jiyo a tsakar gida "kai kai kai, Sadauki wai baku tafi ba har yanzu? Ai kun makara, ina Diyam din?" Nayi saurin ajiye kwanon amma hararar da Inna ta jeho min yasa na dauka na cigaba da rikewa. Baffa ya leko yace "ke Diyam, ki fito ku tafi mana kin makarar dashi zaki sa a dake shi" Inna tayi charaf tace "ya tafi kawai kar a hukunta shi a makarantar su. Diyam bata gama karyawa ba" na ajiye kwanon nace "na gama Baffa, tun dazu na gama Inna ce ta hanani fitowa" na zagaya ta gefenta na fice daga dakin da sauri na rungume sadauki shi kuma ya dauke ni ya dora akan kekensa muka tafi.
Haka mukayi ta fama kullum ba fashi, kullum sai inna tayi ƙoƙarin hanani bin Sadauki ni kuma sai na nace na bishi. Shi zai kaini har class dinmu yaga na shiga sannan ya tafi tasa makarantar. A lokacin dana kara girma kuma sai ya daina dorani a keken sai dai mu tafi a kafa yana jan kekensa a hannu har sai ya kaini sannan shi kuma ya hau ya tafi tasa. Haka islamiyya ma tare za muje, in asma'u ta biyo ni sai in korata ince tabi yaran makotanmu. Sadauki shine yayana, shine abokina, shine kawata, shine abokin shawarata, duk da cewa a lokacin akwai yarinta sosai dan haka duk shawarar ta shirme ce, shima kuma tunda ba wani girmata yayi sosai ba haka zai bani amsar shiririta.
Duk kawayena, na boko dana islamiyya sun san Sadauki, wadda bata sanshi a fuska ba kuwa to tabbas tasan sunansa saboda da wahala in muna hira in iya hada sentence guda ba tare da sunan sadauki ya fito a ciki ba. Duk kuwa sanda wani a ajin mu ko ajin gaba damu yaci zalina ko na tsokani wani ya dake ni to tabbas sai jikinsa ya gaya masa in ya shiga hannun Sadauki, wannan yasa ake shayin tabani ko a yaran unguwa sai dai in na tsokani yaro yayi hakuri dan dole dan sun san cewa sadauki ƙashi daya ne dashi.
Bashi da surutu sam, he is a good listener rather than a talker, ko a gida in dai kaji yana hira to dani ne, ko da Baffa, amma ko Ummah basu cika zama suyi doguwar hira ba. Yana da zuciya da fada in an taba shi ko an taba ni, amma ni din ko daga min murya baya iyayi balle yayi min fada. Kuma duk zuciyar Sadauki, bai taba daga kai ya kalli Inna in tana gayawa Ummah magana ba, sai dai ka gani a fuskarsa cewa ransa ya baci amma ba zai mayar mata ba. Yana da kazar kazar sosai kuma baya zama guri daya, in har baya makaranta to yana gareji in kuma baya can to yana gida yana aiyuka, zai share gidan mu tas ya gyara wa Baffa dakinsa ya wanke masa mota. Watarana nace masa "Sadauki kai baka gajiya ne? Ka kwanta ka huta mana" Sai yace "wa kika taba gani yayi achieving wani abu a kwance? In kana son wani abu you have to work hard to earn it".