← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 112

Sashe 90

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta saka masa wata lomar a baki sannan tace "and how do you know that? Wani ka saka yake spying on me? Baka yarda dani ba?" Yace "babu wanda na saka yayi spying on you. Akwai mutumin da muka yi harkar admission da registration dinku tare. He saw your pictures then. A lokacin kuma na gaya masa ke matata ce then he saw you with that boy and thought ya kamata in sani. I told him bake bace ba cos I thought you would never do it sai ya tura min da picture of you two together" ta ajiye spoon din hannunta tana kallon yadda fuskarsa take nuna bacin rai, yace "do you like him?" Ta dafe kanta tace "I just told you, Bassam is my friend. Na bashi labarin ka ma na gaya masa zaka zo yau kuma har cewa yayi zai so ku hadu. There is nothing there. Please stop looking for something that isn't there" she saw him relax a little yana kallonta yace "he is handsome" tace "really? Ni ban gani ba. He may be one of the thousands of stars in the sky amma ni duk bana ganinsu, only one star shines brightly a ido na, you. Kai kadai nake gani a matsayin mai kyau sauran duk dusudusu nake ganin su. You are the only star in my sky".

And he smiled. This time genuine smile yayi mata ya lumshe idonsa ya bude yace "I always remember that night duk sanda naga starry sky" ta sunkuyar da kanta kasa tace "me too".

Sai ya saka dogayen fingers dinsa guda biyu ya dago fuskarta yana kallon cikin idonta yace "feed me" ta hadiye wani abu a makogwaron ta amma taji yaki tafiya, sai ta yi sauri ta dauke idonta daga cikin nasa ta dauki spoon with shaking hand ta cigaba da bashi abinci. Bai kuma magana ba sai ido daya tsare ta dasu har sai da ta tabbatar ya koshi sannan ta bashi drink ya sha sai kuma yace "thank you, this is the best food I have tasted for a while. Ko kuma yadda aka bani abincin ne ya saka naji yafi kowanne dadi?"

Sai kuma ta danji kunya ta rufe fuskarta da bakin hijab dinta, suddenly sai taji babu abinda take so irin ta kuma jin wannan kalmar daga bakinsa but as her husband yadda zata ji dadi fiye da na yanzu kuma ta samu lada mai yawa.

Sai ta zame daga kujerar da take zaune ta durkusa a gabansa tana kallon yadda yake kallonta da mamaki tace "Aliyu Umar Abatcha. Will you do me the honor of marrying me?"

Please, duk wanda Allah ya bawa ikon karanta wannan page din ina barar a karanta min surorin Falaq da Nas. Da niyyar Allah ya gina mana katangar tsari tsakanin mu da duk wanda yake neman mu da sharri, Allah kuma ya tabbatar mana da alkhairi tsakanin mu da duk mai neman mu da alkhairi. Allah yayi mana jagora kar ya barmu da iyawar mu dan mu ba zamu iya ba. Allah ya tabbatar mana da alkhairi a kasar mu baki daya.

Nagode
[3/14, 10:49 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Sixty Six: The Unbreakable Love 2

Naga adduoin ku, nagode sosai.

For two seconds ya zauna yana kallonta da tsantsar mamaki a fuskarsa sai kuma yayi sauri ya mike tsaye ya kamo hannayenta duk biyun ya mikar da ita tsaye yana kallonta tana murmushin ganin duk yadda yabi ya rude sai yace cikin saurin murya "No! No".

Ta bude ido da mamaki tace "no?" Sai ya saki hannunta da sauri ya dafe kansa yace "ba wannan no din ba, I mean no karki durkusa please, karki bata kayanki" ya fada yana ciwo hanky da sauri ya kama goge mata hijab dinta, sai daya dago sannan ta daga gira tace "so? Yes ne ko No?" Maimakon ya bata amsa sai ya dora goshinsa a kafadarta, tana jin yadda ya sauke wata nannauyar ajjiyar zuciya wadda tasa hawaye ya gangaro daga idon Diyam sannan yace can kasan makoshinsa "Yes Diyam. Of cause I will marry you. You have no idea how much I want to marry you"

Murjanatu ta bude kofa ta shigo, sai kuma ta tsaya tana kallon su sannan tace "wrong room. Ba nan zan shigo ba" sai ta kalli kofa tace "Na'am!" Ta juyo tace "they are calling me so I gotta go" sai ta juya da sauri ta fita. Diyam tayi dariya tana share kwallar idonta tace "she is funny. Babu wanda yake kiranta" ya danyi dariyar da Diyam taji vibration dinta a kirjinta yace "kika sani ko aljanun gidan ne suke kiranta?"

Ta dan matsa baya forcing him to raise his head from her shoulder. Sai ya kalle ta da idon da suka fara chanja color yace "yaushe kika chanja shawara kuma? What about Saghir? Kin fasa fitar dashi din?" Ta zauna a kujera tayi dagumi but fuskarta da murmushi tace "you won the bet, I can't continue to deny myself freedom. Nayi kokari ai ko?" Ta fada da sanyin murya. Ya zauna opposite dinta yace "Subay'a fa?" Tace "in muka yi aure Subay'a ta zama yarka. And I trust you will do everything in your power to make your daughter happy" ya gyada kai yace "you bet. She is going to be the happiest girl ever".

Matar dazu ce ta shigo ta fara gyaran dining table sannan ta zo gurin su tana tambayar Sadauki in akwai abinda yake bukata in babu tana son tafiya. Ya sallameta ta tafi ya juyo yana kallon Diyam da take bin bayan matar da harara yayi murmushi yace "what?" Tace "fire her. Ita da wannan secretary din taka ta Kano" ya bude ido da mamaki yace "why?" Ta turo baki "ni bana son su" yayi dariya yana shafa kansa yace "and you accuse me of being heartless" ta bude hannu tace "sai ka basu wani aikin ai. Kai kuma ka samu maza suke yi maka irin wadannan aiyukan" yayi tagumi da hannu daya yana kallonta yace "yarinyar nan anya kuwa Baffa bada A'isha yayi miki huduba ba? Kishinki yayi yawa. Yanzu suna min aiki kince ba kya so, so tell me idan kuma kika gan mu tare muna cin abinci a cafeteria mai zaki yi? Hmm?" Ta gane inda ya dosa sai tayi saurin cewa "kayi hakuri, an gama ba za'a kuma sakewa ba" bai ce komai ba sai kallonta da yake tayi fuskarsa da murmushi. Ta jawo fuskar hijab dinta ta rufe fuskarta tace "ni kunya kake saka ni in kana kallona" sai ya koma ya jingina a jikin kujerar yace "kinsan tunanin me nake yi?" Ta bude fuskar ta tace "no" yace "tunani nake yi in koma airport a yau in koma Nigeria, gobe inga Kawu Isa jibi a daura mana aure in dawo gurin amaryata a jibin" tayi saurin mayar da fuskarta ta rufe tace "kai dan Allah. Ka dai bani lokaci in shirya dai ko?" Yace "wacce shiryawa kuma? Nasan a gida zasu ce zasu shirya wani abu amma koma menene sai dai su jira sai bayan na tare da amarya ta" sai ta mike da sauri tayi hanyar waje tana hada hanya tace "sai dai ka tare kai kadai" ya biyo bayanta yana cewa "dama ai ni kadai nake tarewa ta kullum on my empty cold bed, it is about time I get some warmth" ta karasa kofar da sauri tana hoping ba irin ta office dinsa bace ba. Tana murdawa taji ta bude ta fita tana raba idon inda zata hango Murjanatu, sai gashi nan ya fito shima ya rufe kofar ya jingina da jikin kofar ya harde hannayensa da kafafuwansa yace "run run little girl. Duk inda zaki je you will come back here" ya fada yana nuna kirjinsa yace "cos that's where you belong. A heart belongs to the chest".

Ta juya suka hada ido, feeling like yau ta fara ganin sa. She couldn't help but look at chest din daya nuna, very broad and very strong, sai taji babu abinda take so irin ta jita a gurin feeling the warmth and the strength that she so much miss. Ta hadiye wani abu tare da saurin girgiza kanta a kokarin ta na goge image din daga kanta tace masa "uhmmm. Lokacin Sallah. Murjanatu" yayi mata murmushin gefen baki sai ya nuna mata wata kofa da hannu" ta juya da sauri ta tafi can. Sai data bude kofar ta shiga sannan ta rufo kofar ta jingina da jikinta ta yi ajjiyar zuciya. Sai kuma tayi murmushi tana girgiza kanta.

Daga gefenta taji ance "hmmm. Wato da can anaso ana kaiwa kasuwa akeyi ko?" Ta juyo ta harari Murjanatu tace "ke nifa yayarki ce, bana son rashin kunya". Anan tare sukayi sallah tare sannan suka fita Murjanatu tana zagayawa da ita gidan Diyam tana ta kashe kwarkwatar idonta. Komai na gidan abin kallo ne, exact lissafin da Diyam take yi na abinda ake cewa aljannar duniya. Suna cikin zagayen suka hadu dashi, yace da Murjanatu "thank you Fanna, zaki iya komawa daki" ta turo baki tana buga kafa amma yana yi mata wani kallo ta juya ta koma. Diyam tace "kai kuwa ka barta mana mu karasa" yace "a gabanta zanyi hira dake? Kina sone ma ta raina ni kenan" suka jera suka cigaba da tafiya tare, but ba kallon gida sukeyi ba hirar su kawai suke yi suna jin dadin iskar da take kadasu.

Ta rungume hannunta tana jin sanyi amma bata son nunawa dan tana jin dadin hirar da yake yi mata, sai ya cire top dinsa ya saka mata, ya cigaba da bata labarin irin yadda ya yi ta kokarin ganin ta kira shi dan yayi wining amma taki. Yace "har halucination fa nake yi. In wani ya kira ni sai inga kamar ke. It was hectic. I almost lost it" tayi murmushi tace "kasan me? Wani lokacin sawa nake Murjanatu ta saka min kai a handsfree" ta fada tana rufe fuskarta, yace "laaa ila, that was cheating" ta bude fuskarta tana hararar sa tace "har zaka yi maganar cheating?" Yayi dariya yace "bature yace 'nothing is fair in love and war".
Chapter 90 · 0% Book details