← Book details Diyam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 112

Sashe 8

Diyam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari Friday, da sassafe Diyam taje school dan ko breakfast bata tsaya tayi ba saboda bata ma son abinda zai hada ta magana da Murjanatu har sai tayi deciding inda zatayi placing dinta. Ta jima a class tana duba takardunta amma a can kasan zuciyarta tana duba ta inda Bassam zai bullo. Tana nan a zaune har aka zo aka sanar cewa lecturer din ba zai samu zuwa ba, a dai dai nan Bassam ya shigo, suna hada ido tayi saurin dauke kanta amma ta kasan idonta ta hango shi straight ya taho gurinta, ta fara kokarin harhada takardunta pretending to be busy har yazo daf da seat dinta ya tsaya, da dan karfi yace "why? Menene dalilinki na cutting dina off? Laifin me nayi?" Bata ce komai ba amma sai taji wani abu ya rike a tsakiyar cikinta kamar mai jin yunwa, nan take jikinta ya kama karkarwa har takardun hannunta suka zame suka zube a kasa, ta sunkuya tana kwashewa shima ya sunkuyo yana taya ta, sunkuyon da tayi yasa rolling din veil dinta ya kunce gashinta ya zubo ya rufe mata fuska ya sauka akan hannayensa. Still yayi yana kallon tsaho, baki da santsin gashin, ya daga hannunsa ya mayar mata da gashin bayanta tare da bude mata fuskarta, a lokacin ya lura da how red fuskarta da idonta sukayi, sai kawai yaji tashi zuciyar tayi melting, yaji kamar bai kyauta ba da ya daga mata murya har ya bata mata rai. Ta mike ta warce papers din hannunsa ta ajiye a gefe tana gyara veil dinta yace "am sorry Diyam but dan Allah ki gaya min abinda nayi miki" ta dauki takardun ta ta zagaye shi zata wuce ya rike jakarta yace "saboda na fada miki am in trouble da family na shine zaki juya min baya?" Da sauri ta juyo tana sauke manyan idanuwanta da suka yi ja a kansa, she looked shocked, bata taba zaton zai yi linking wannan abin da labarin sa ba, ta warce jakarta tace "is that what you are thinking? tunanin da kake yi a kaina kenan?" Ya daga kafada yace "then tell me otherwise, me nayi miki" tace "babu abinda kayi min Bassam" ta danyi shiru kamar mai tunani sannan cikin karyayyiyar murya tace "am just not who you think I am. Am sorry" ta juya da sauri saboda hawayen da taji yana taho mata. Kafin ta kai kofa ya kuma rike jakarta, ta juyo ta zuba masa jajayen idanuwanta yace shima da raunanniyar murya "ko ba zaki cigaba da kulani ba, at least give me your number yadda zan ke jin halin da kike ciki ko a waya ne, ko physically ba zamuyi magana ba at least....."

"Number?" Ta katse shi "wacce number zan baka Bassam? Ohhh I have so many numbers a cikin wannan kan nawa" ta fara lissafa masa da yatsun hannunta "kaga na farko 24 itace number din shekaru na, 3 itace number adadin yayan dana haifa a duniya, 2 itace number of times I was divorced, 8 itace shekarun yar karamar yarinya ta, infinity shine number of times my heart was broken and 0 is the tolerance I have for other hear breaks. So tell me, wacce number zan baka a cikin wadannan?"

A hankali jakarta ta zame daga hannunsa saboda yadda gaba-daya jikinsa ya saki, tamkar numfashin sa aka zare gaba daya. Ta tako zuwa dai dai fuskarsa tace "like I said, am not who you think I am".

Har ta fita daga ajin bai motsa daga inda yake ba.

You did not see that coming, did you?
[1/7, 7:40 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Nine: The Gamer

Tabbas maganar da Diyam ta fada wa Bassam bashi kadai ta taba ba, har ita. Tana fita daga ajin taji kanta yana wani irin juyawa kamar zata fadi, duk reality din rayuwar ta yana dawo mata. Tun da tazo UK take living in a dream yanzu kuma ta farka, gobe kuma zata kara farkawa tunda gobe zai zo bata san kuma da wacce zai zo ba. As far as he is concerned yayi winning over her dan haka zata bi abinda yace kenan. Ta samu jikin wata bishiya ta jingina tana mayar da numfashi, a nan taji karar shigowar text wayarta, ta dauko a jaka ta bude taga wanda take tunanin ne ya aiko mata da message

"Tell him I say hi, kafin inzo mu gaisa gobe"

Ta sake karantawa, ta nanata amma ta kasa making sense of it. "Him?" who is him?. Wata karamar murya a can kasan zuciyarta tace "Bassam" ta zame ta durkushe a gurin, so he knows about Bassam? Abinda take ta gudu kenan gashi nan bata yi escaping ba. Amma ta yaya yasan labarin Bassam? "Murjanatu" muryar ta sake fada mata.

Ta mike and for the first time ta tari cab saboda yadda take ji ba zata iya tafiya a kafa ba. A motar ma dunkule wa tayi dan ba zata iya zama straight ba saboda wannan abin daya dunkule mata a ciki har yanzu bai saki ba, sai da drivern yayi mata magana sannan ta san sunzo, ta bashi kudinsa ta shiga ciki. Tana bude kofa idonta ya sauka akan Murjanatu a zaune tana facing kofa, suna hada ido Diyam tayi realising gaskiya, ba Murjanatu ce ta gaya masa ba. Murjanatu ta mike tana twisting hannunta tace "Diyam, yaya yasan kuna tare da wannan yaron" Diyam ta bita da kallo bata ce komai ba, Murjanatu ta cigaba "wallahi bani na gaya masa ba, I wanted to tell you tun jiya ya kira ni ya tambayeni wai waye kuke yawo tare dashi a school nace masa ni bansan kina yawo da kowa ba, he said in bangaya masa ba in yazo sai na sani. To dazu kuma ya kira yace min nayi masa karya kuma sai na gane kure na" still Diyam bata ce komai ba, kallonta take kawai tana lura da yadda tsoro ya fito baro baro a kyakykyawar fuskarta. Ta taho ta zagaye ta zata shiga corridor Murjanatu ta mike ta rike hannunta tace "Diyam am sorry akan maganar shekaran jiya, wallahi bansan betting kuka yi a kan wani abu ba, ni kawai cewa yayi min zamuyi playing game, yana so in nuna miki da gaske yake zai kori Judith, please Diyam kiyi hakuri bana son alakar mu ta baci a saboda wannan" ba tare da Diyam tace komai ba ta zare hannunta daga na Murjanatu ta shige dakinta ta rufe kofa. Direct toilet ta shiga, ta cire kayanta gaba-daya ta shiga shower ta kunnawa kanta ruwan dumi. Ta lumshe idonta tana jin dadin yadda ruwan yake sauka a kanta, tana jin duminsa yana narkar da daskararriyar zuciyarta, tana jin jijiyoyinta suna warewa suna aikawa da sakonni kwakwalwarta. Ta tuno abinda Murjanatu tace "a game" of course it is all a game, shi komai a gurin sa ai game ne. Ta tuno wata magana daya taba fada mata shekaru da dama da suka wuce

"Diyam, life is like a game of chess, the secret to winning is to observe the movements of your opponent, think deeply and make your move"

Amma abinda ya kasa ganewa shine a yanzu bashi da opponent din, shi kadai yake buga game dinsa, kuma ya kasa realizing cewa a haka zai zo yayi hurting others, innocent mutane kamar Bassam. Ya kasa realizing cewa duk abinda take yi tana yi ne for him not against him. Shi kawai burinsa yayi winning, no matter the cost. Ita kuma burinta shine ya ajiye wannan game din ya duba reality, ita bata son wannan game din nasa mai ban tsoro, dan last game din da ya buga didn't end well, it ended with someone in jail for life, someone very important to her.

Ta kashe shower din ta fito ta daura dogon towel sannan ta dauki karami tana goge fuskarta da dogon gashinta dashi, a ranta tana kokarin placing kanta in his place daga nan sai taga menene next move dinsa. Amma duk iya kokarinta ta kasa guessing menene zaiyi a next move dinsa. Ta fito ta dauki wayarta data ajiye tana dubawa, sai a lokacin tayi realising cewa for the first time tun zuwanta kasar yau ne rana ta farko da bai kira ta ba, hakan yana nufin yayi fushi da ita, fushi kuwa mai tsanani. Ita dai tasan har ga Allah bata fara kula Bassam saboda wani abu ba, ta fara kula shine saboda maganganu marasa dadi data fada masa a farkon fara maganar su, wannan yasa ta sauko da niyyar ta wanke kanta a gurin sa kuma sai abota ta shiga tsakaninsu. Ita tasan ko da da digon zarra bata jin wani feeling a kan Bassam wanda ya wuce na mutumta juna da aminci.

Ta shirya cikin doguwar rigar zaman gida, ta kwanta ta dauki pillow ta dora akan cikinta ta rungume, sai a sannan ta tuna cewa ko breakfast bata yi ba amma kuma yunwa is the last thing a mind dinta. She just want to know wanne mataki zai dauka, she just want to make sure ba zaiyi hurting kowa ba akanta. Tana nan kwance ita ba bacci ba ita ba ido biyu ba har lokacin sallar zuhr yayi, tayi alwala ta sauke farali sannan ta fito parlor, babu kowa dan haka tashiga kitchen ta dafa noodle ta zauna akan stool taci sannan ta wanke plate da tukunyar data bata ta dauki bottled water ta fito parlor ta zauna tana sha. Dai dai nan Murjanatu ta fito itama da shirin tafiya school. Ta dan zauna a gefen Diyam amma bata ce komai ba. Diyam ta mike ta shiga daki ta dauko dogon hijab ta saka tayi hanyar waje, har ta taba kofa taji Murjanatu tace "Diyam" sai ta juyo ta dawo kusa da ita ta zauna ta rike hannayenta a cikin nata tace "don't worry. He won't hurt you, not while am here". Sai kuma ta tashi ta fita da sauri.
Chapter 8 · 0% Book details