Sashe 6
Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shi kenan. Na yarda da abin da ka faÉ—a, amma fa tabbas sau É—aya zan din ga ba ta abinci, zuwa lokacin da za ta haihu. Daga nan ko dai ta fidda miji, ko kuma ta koma ciyar da kanta, ko kuma gaba É—aya ma ta bar gidan." Ba ta jira wani daga cikin su ya ce komai ba ta bar wajen, ta bar su da bin ta da idanu.
"Na gode sosai Baffa." Inna-wuro ta faɗa da sanyayyiyar muryarta, a ranta tana addu'ar Allah Ya sake dawo mata da Baffanta daidai ko ta ji sauƙin rayuwarta cikin gidan.
Haka rayuwar Inna-wuro ta cigaba da tafiya ita da ɗiyarta. Baƙin cikin yau daban na gobe daban. Ko da wani lokacin Baffa ya yi niyyar taimaka mata ko kallanta da idon rahama sai Dada ta san yadda ta yi ta hana hakan faruwa. Shi kuma da ta yi magana shi kenan yake shiga taitayinsa. Sai dai zuwa lokacin Dada tana yarda ta ba ta abinci sau ɗaya a rana, daga nan kuma ko kallan inda take ba za ta sake yi ba. Wani lokacin sai dai a ɓoye Baffa ya kawo mata nasa. I zuwa lokacin kuwa ta soma ramewa, musamman da ya kasance ga shayarwa da take, ga kuma cikin jikinta. Sosai abubuwan suka haɗe mata, cikin lokaci ƙanƙani ta soma sauyawa daga ainahin Inna-wuronta, ga babu isasshen abinci, ga babu laifi cikin na matuƙar ba ta wahala, lokaci guda kuma ga Daneen da ke fama da rashin lafiya, duk ta bi ta rame saboda haƙori da ya saka ta gaba. Wannan ya taka muhimmiyar rawa wajen sake taɓarɓarewar lamarin Inna-wuron, ta zama abar tausayi. Idan ka yi mata kallo ɗaya ita da Daneen sai sun ba ka tausayi, musamman ma dai ita da duk ta bi ta lalace tamkar ba a gidan mahaifinta take ba.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 04
__ Babu wani sauyi da ya samu har zuwa lokacin da ta haife abin da ke cikinta, a cikin gida kamar yadda ta haifi Daneen cikin sauƙi da rangwamin Ubangiji. Sai dai wannan karon namiji Allah Ya ba ta, kyakykyawa mai kama da 'yar'uwarsa. Lokacin da ta haihu shekarar Daneen ɗaya, don haka ta yaye ta a wannan lokacin. Ko arba'in ba ta kai ga yi ba, ta ga zama cikin gidan nan haka kawai ba zai yi mata ba. Idan ba haka ba, ba jaririnta ba, ba Daneen ba, ita kanta yunwa za ta mata lahani. Dalili kenan da ya sa ta tattara duk wani abu da ta mallaka ta siyar, ta siyar da saniyar da Allah Ya taimake ta Dada ba ta ƙwace ta yi rara-gefe da ita ba. Kasancewar ba a gidan take kiwon ta ba. Da wannan kuɗaɗen ta haɗa ta soma siyar da abinci da fura da nono a cikin kasuwar ƙauyen nasu. Yaro ta samu shi ne wanda yake taya ta ayyuka saboda kula da 'ya'yanta. Wannan sana'ar, ba ƙaramin taimaka mata ta yi ba, domin kuwa za ta samu ta ci abinci, Daneen ma ta ci, sannan kuma jaririnta da ya ci suna Ameer ma ya samu ya ci.
.. "Ni fa na faɗa maka ba zai yiwu ba. Ta yaya za a yi a ce ƙatuwar mata har da 'ya'ya biyu a ce a gida za ta din ga zama. Daga wannan layin sai wancan layin. Fisabillahi a haka za a rayu? Haka za mu cigaba da zuba mata idanu ta yi ta zama babu aure?" Ta jiyo muryar Dada daga tsakar gida, daidai lokacin da take shayar da Ameer, ya yin da Daneen ke kwance a kan cinyarta. Runtse idanunta ta yi, ita kam ta rasa me Dada take nufi da ita. Duk salon rashin ƙaunarta ne yake cigaba da fito wa kusufa-kusufa haka? Ta nuna ba za ta ciyar da ita ba, ta yi haƙuri ta zauna. Yanzu kuma tana ciyar da kanta ma ba ta tsira ba? Wannan wace irin rayuwa ce. Sai dai cikin sakannin da ba su wuce biyar ba, ta buɗe idanunta lokacin da ta jiyo muryar Baffa na faɗin
"Ba kuma zai yiwu ba gaskiya sai dai ki yi haƙuri. Tun da dai sana'a take don ta ciyar da kanta da 'ya'yanta ba za mu hana ta ba gaskiya." Ya faɗa ba tare da ya kalli Dadan ba, duk da yadda yake jin wata irin shakkar ta. Amma ya danne, ya cije ya faɗi abin da ke masa yawo a zuciya. Lumshe idanunta Inna-wuro ta yi tana jin wani irin sanyi na ratsa ta. Wasu hawaye masu ɗumi suka zubo a kan kuncinta.
"Ya Allah Ka ƙara dawo da hankalin Baffana kaina. Ka kare shi daga sharrin wannan matar." Ta faɗa a hankali, har lokacin idanunta na a rufe. Buɗe idanunta ta yi lokacin da ya sauka a kan Daneen da ke ta kallon ta, zuwa lokacin uwar ramar da ta yi duk ta yi nata wajen. Sai ta sakar mata murmushi tana kamo kumatunta ta ja.
Zaro idanu Dada ta yi zuciyarta na bugawa, cikin matuƙar tsoro ta ce bakinta har rawa yake
"Umar.." Ta ambata tana kallansa, kafin ya ce komai ta sake faÉ—in
"Ni kake faÉ—a wa haka?" Ta faÉ—a har lokacin bugun zuciyarta bai koma daidai ba.
"Toh ai gaskiya ce." Ya faɗa yana juya wa ya bar ta a wajen tsaye kamar wadda aka dasa. Ta kai wajen minti 5 tsaye a wajen ba tare da ta motsa ba. Gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta ta toshe, kanta ya kulle. Mai take ganin yana shirin faruwa? Lallai ta yi mugun sake. A daren Dada ta fice daga gidan zuwa gidan wata 'yar'uwarta. Kuka kawai ta fashe da shi tana faɗin
"Ni kam na shiga uku Hanne, ki taimaka mini kafin rayuwa ta juya mini baya. Umar ya fara juya mini baya." A ranar suka saɓi jiki zuwa wajen Malamin da ya saba musu aiki faka-faka.
_BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYAR_
A cikin shekarun nan abubuwa da dama sun faru, ciki kuwa har da sauyawar Dada kaɗan, saboda wani dalili da ita kaɗai ta bar wa kanta sani. Duk da shekarun da suka tafi, hakan be sa ta watsar da makamanta ba, ko don yadda girma ke ƙara kama su. Domin kuwa daga zarar ta ga Baffa ya soma ɗan sassautawa, yana ja da abin da ta faɗa za ta yi saurin koma wa wajen malaminta ya yi mata aiki a kansa. Kai daga ƙarshe ma sai ta nemi a yi mata aikin da har abada ba za ta sake dawo ba. Nan da nan Malamin ya nemi da ta kawo kuɗaɗe masu yawa, ta kuwa siyar da saniyarta ta biya kuɗin aikin, domin kuwa abin da take ƙoƙarin aikatawa ta san zai kawo mata ninkin ba ninkin kuɗin Saniyar da ta kashe. Daga nan kuwa al'amarin Baffa ya sake rikicewa fiye da da, ya zama shi ma ya koma muzgunawa Inna-wuro a cikin gidan nan. Kwata-kwata babu sauƙi ita kam a kowanne ɓangare sai a wajen Allah. Sai kuma idan ta kalli 'ya'yanta da take fata nan gaba su zame mata sanyin idaniya, kamar yadda tun yanzun su kaɗai take kalla ta ji daɗi. Daneen da Ameer sun taso ne tamkar 'yan biyu. Don kuwa tun da Ameer ya fara girma sai da ya kamo Daneen, sai ya zamana idan ma ba ka sani ba kana kallan su za ka kira su da 'yan biyu, saboda tsananin kamar da suke, uwa uba kuma kansu ɗaya. A tare suka taso da wata irin muguwar shaƙuwa, da tsananin soyayyar junansu. Ɗaya ba ya son abu ya samu ɗaya. Idan ɗaya ba shi da lafiya ba za ka taɓa gane waye bai da lafiya ba, saboda gaba ɗaya haɗuwa suke su yi jinyar tare. Wanda hakan ba ƙaramin tada wa da Inna-wuro hankali yake ba. Ta rasa inda za ta jefa kanta, har sai mara lafiyar ya warke kafin take samun nutsuwar zuciya, ita da mai taya jinyar. Har zuwa lokacin tana siyar da abinci kala-kala, har ma da wasu abubuwan buƙata. Da wannan sana'ar ta yi amfani wajen saka 'ya'yanta a makarantar da ke nan bakin kasuwar da take siyar da abinci. Nan suke zuwa su same ta idan an tashi kafin idan ta gama abin da take su tafi gida. Da daddare kuma su je makarantar dare, wadda take babu nisa daga gidansu. Duk wannan abubuwan har zuwa lokacin Dada ba ta canja ba. Sai dai wasu abubuwan sun ɗan yi sauƙi saboda gajiya. Uwa uba kuma da ya kasance watarana ma idan ta ga Inna-wuron da safe sai dare sannan za ta kuma sanya ta a ido. Dalili kenan da ya sa ta ɗan yi sanyi tana jira lokacin da Malam ya ce mata ta jira ya yi. Sai dai kuma maimakon haka sai ta ɗauki rabin tsanar da ta yi wa Inna-wuro ta maida ta kan Daneen da kuma Ameer, ba su da damar su fito tsakar gidan yin wasa, ko wani abun sai ta hantare su. Har gwara ma Baffa, duk da shi ma ba ya wani kula su, amma dai ba ya hantarar su kamar yadda Dada take.
Da ma kuma tun da suka taso suka fara wayo suka fahimci ko ma wace ce Dada ba ta ƙaunar su, don su ɗin yara ne masu matuƙar wayo. Don akwai ranar da suna kasuwa siyar da abinci, Ameer ya kalli Inna-wuro ya ce
"Inna.."
"Na'am Ameer." Inna-wuro ta faÉ—a bayan ta juyo ta kalle shi da murmushi É—auke a kan fuskarta.
"Wai me ya sa Dada ba ta sonmu?" Ya yi tambayar da ta sanya Inna-wuro janye murmushin fuskarta.
"Ameer?" Ta yi ƙarfin halin faɗar hakan fuskarta a haɗe. Ba ta taɓa zata ba, ba ta taɓa kawo wa tun a yanzu za su fahimci cewa Dadar ba ta ƙaunar su ne ba. Sai dai ga shi sun shammace ta. Kafin ya ce komai ta ɗora da faɗin
"Na gode sosai Baffa." Inna-wuro ta faɗa da sanyayyiyar muryarta, a ranta tana addu'ar Allah Ya sake dawo mata da Baffanta daidai ko ta ji sauƙin rayuwarta cikin gidan.
Haka rayuwar Inna-wuro ta cigaba da tafiya ita da ɗiyarta. Baƙin cikin yau daban na gobe daban. Ko da wani lokacin Baffa ya yi niyyar taimaka mata ko kallanta da idon rahama sai Dada ta san yadda ta yi ta hana hakan faruwa. Shi kuma da ta yi magana shi kenan yake shiga taitayinsa. Sai dai zuwa lokacin Dada tana yarda ta ba ta abinci sau ɗaya a rana, daga nan kuma ko kallan inda take ba za ta sake yi ba. Wani lokacin sai dai a ɓoye Baffa ya kawo mata nasa. I zuwa lokacin kuwa ta soma ramewa, musamman da ya kasance ga shayarwa da take, ga kuma cikin jikinta. Sosai abubuwan suka haɗe mata, cikin lokaci ƙanƙani ta soma sauyawa daga ainahin Inna-wuronta, ga babu isasshen abinci, ga babu laifi cikin na matuƙar ba ta wahala, lokaci guda kuma ga Daneen da ke fama da rashin lafiya, duk ta bi ta rame saboda haƙori da ya saka ta gaba. Wannan ya taka muhimmiyar rawa wajen sake taɓarɓarewar lamarin Inna-wuron, ta zama abar tausayi. Idan ka yi mata kallo ɗaya ita da Daneen sai sun ba ka tausayi, musamman ma dai ita da duk ta bi ta lalace tamkar ba a gidan mahaifinta take ba.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 04
__ Babu wani sauyi da ya samu har zuwa lokacin da ta haife abin da ke cikinta, a cikin gida kamar yadda ta haifi Daneen cikin sauƙi da rangwamin Ubangiji. Sai dai wannan karon namiji Allah Ya ba ta, kyakykyawa mai kama da 'yar'uwarsa. Lokacin da ta haihu shekarar Daneen ɗaya, don haka ta yaye ta a wannan lokacin. Ko arba'in ba ta kai ga yi ba, ta ga zama cikin gidan nan haka kawai ba zai yi mata ba. Idan ba haka ba, ba jaririnta ba, ba Daneen ba, ita kanta yunwa za ta mata lahani. Dalili kenan da ya sa ta tattara duk wani abu da ta mallaka ta siyar, ta siyar da saniyar da Allah Ya taimake ta Dada ba ta ƙwace ta yi rara-gefe da ita ba. Kasancewar ba a gidan take kiwon ta ba. Da wannan kuɗaɗen ta haɗa ta soma siyar da abinci da fura da nono a cikin kasuwar ƙauyen nasu. Yaro ta samu shi ne wanda yake taya ta ayyuka saboda kula da 'ya'yanta. Wannan sana'ar, ba ƙaramin taimaka mata ta yi ba, domin kuwa za ta samu ta ci abinci, Daneen ma ta ci, sannan kuma jaririnta da ya ci suna Ameer ma ya samu ya ci.
.. "Ni fa na faɗa maka ba zai yiwu ba. Ta yaya za a yi a ce ƙatuwar mata har da 'ya'ya biyu a ce a gida za ta din ga zama. Daga wannan layin sai wancan layin. Fisabillahi a haka za a rayu? Haka za mu cigaba da zuba mata idanu ta yi ta zama babu aure?" Ta jiyo muryar Dada daga tsakar gida, daidai lokacin da take shayar da Ameer, ya yin da Daneen ke kwance a kan cinyarta. Runtse idanunta ta yi, ita kam ta rasa me Dada take nufi da ita. Duk salon rashin ƙaunarta ne yake cigaba da fito wa kusufa-kusufa haka? Ta nuna ba za ta ciyar da ita ba, ta yi haƙuri ta zauna. Yanzu kuma tana ciyar da kanta ma ba ta tsira ba? Wannan wace irin rayuwa ce. Sai dai cikin sakannin da ba su wuce biyar ba, ta buɗe idanunta lokacin da ta jiyo muryar Baffa na faɗin
"Ba kuma zai yiwu ba gaskiya sai dai ki yi haƙuri. Tun da dai sana'a take don ta ciyar da kanta da 'ya'yanta ba za mu hana ta ba gaskiya." Ya faɗa ba tare da ya kalli Dadan ba, duk da yadda yake jin wata irin shakkar ta. Amma ya danne, ya cije ya faɗi abin da ke masa yawo a zuciya. Lumshe idanunta Inna-wuro ta yi tana jin wani irin sanyi na ratsa ta. Wasu hawaye masu ɗumi suka zubo a kan kuncinta.
"Ya Allah Ka ƙara dawo da hankalin Baffana kaina. Ka kare shi daga sharrin wannan matar." Ta faɗa a hankali, har lokacin idanunta na a rufe. Buɗe idanunta ta yi lokacin da ya sauka a kan Daneen da ke ta kallon ta, zuwa lokacin uwar ramar da ta yi duk ta yi nata wajen. Sai ta sakar mata murmushi tana kamo kumatunta ta ja.
Zaro idanu Dada ta yi zuciyarta na bugawa, cikin matuƙar tsoro ta ce bakinta har rawa yake
"Umar.." Ta ambata tana kallansa, kafin ya ce komai ta sake faÉ—in
"Ni kake faÉ—a wa haka?" Ta faÉ—a har lokacin bugun zuciyarta bai koma daidai ba.
"Toh ai gaskiya ce." Ya faɗa yana juya wa ya bar ta a wajen tsaye kamar wadda aka dasa. Ta kai wajen minti 5 tsaye a wajen ba tare da ta motsa ba. Gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta ta toshe, kanta ya kulle. Mai take ganin yana shirin faruwa? Lallai ta yi mugun sake. A daren Dada ta fice daga gidan zuwa gidan wata 'yar'uwarta. Kuka kawai ta fashe da shi tana faɗin
"Ni kam na shiga uku Hanne, ki taimaka mini kafin rayuwa ta juya mini baya. Umar ya fara juya mini baya." A ranar suka saɓi jiki zuwa wajen Malamin da ya saba musu aiki faka-faka.
_BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYAR_
A cikin shekarun nan abubuwa da dama sun faru, ciki kuwa har da sauyawar Dada kaɗan, saboda wani dalili da ita kaɗai ta bar wa kanta sani. Duk da shekarun da suka tafi, hakan be sa ta watsar da makamanta ba, ko don yadda girma ke ƙara kama su. Domin kuwa daga zarar ta ga Baffa ya soma ɗan sassautawa, yana ja da abin da ta faɗa za ta yi saurin koma wa wajen malaminta ya yi mata aiki a kansa. Kai daga ƙarshe ma sai ta nemi a yi mata aikin da har abada ba za ta sake dawo ba. Nan da nan Malamin ya nemi da ta kawo kuɗaɗe masu yawa, ta kuwa siyar da saniyarta ta biya kuɗin aikin, domin kuwa abin da take ƙoƙarin aikatawa ta san zai kawo mata ninkin ba ninkin kuɗin Saniyar da ta kashe. Daga nan kuwa al'amarin Baffa ya sake rikicewa fiye da da, ya zama shi ma ya koma muzgunawa Inna-wuro a cikin gidan nan. Kwata-kwata babu sauƙi ita kam a kowanne ɓangare sai a wajen Allah. Sai kuma idan ta kalli 'ya'yanta da take fata nan gaba su zame mata sanyin idaniya, kamar yadda tun yanzun su kaɗai take kalla ta ji daɗi. Daneen da Ameer sun taso ne tamkar 'yan biyu. Don kuwa tun da Ameer ya fara girma sai da ya kamo Daneen, sai ya zamana idan ma ba ka sani ba kana kallan su za ka kira su da 'yan biyu, saboda tsananin kamar da suke, uwa uba kuma kansu ɗaya. A tare suka taso da wata irin muguwar shaƙuwa, da tsananin soyayyar junansu. Ɗaya ba ya son abu ya samu ɗaya. Idan ɗaya ba shi da lafiya ba za ka taɓa gane waye bai da lafiya ba, saboda gaba ɗaya haɗuwa suke su yi jinyar tare. Wanda hakan ba ƙaramin tada wa da Inna-wuro hankali yake ba. Ta rasa inda za ta jefa kanta, har sai mara lafiyar ya warke kafin take samun nutsuwar zuciya, ita da mai taya jinyar. Har zuwa lokacin tana siyar da abinci kala-kala, har ma da wasu abubuwan buƙata. Da wannan sana'ar ta yi amfani wajen saka 'ya'yanta a makarantar da ke nan bakin kasuwar da take siyar da abinci. Nan suke zuwa su same ta idan an tashi kafin idan ta gama abin da take su tafi gida. Da daddare kuma su je makarantar dare, wadda take babu nisa daga gidansu. Duk wannan abubuwan har zuwa lokacin Dada ba ta canja ba. Sai dai wasu abubuwan sun ɗan yi sauƙi saboda gajiya. Uwa uba kuma da ya kasance watarana ma idan ta ga Inna-wuron da safe sai dare sannan za ta kuma sanya ta a ido. Dalili kenan da ya sa ta ɗan yi sanyi tana jira lokacin da Malam ya ce mata ta jira ya yi. Sai dai kuma maimakon haka sai ta ɗauki rabin tsanar da ta yi wa Inna-wuro ta maida ta kan Daneen da kuma Ameer, ba su da damar su fito tsakar gidan yin wasa, ko wani abun sai ta hantare su. Har gwara ma Baffa, duk da shi ma ba ya wani kula su, amma dai ba ya hantarar su kamar yadda Dada take.
Da ma kuma tun da suka taso suka fara wayo suka fahimci ko ma wace ce Dada ba ta ƙaunar su, don su ɗin yara ne masu matuƙar wayo. Don akwai ranar da suna kasuwa siyar da abinci, Ameer ya kalli Inna-wuro ya ce
"Inna.."
"Na'am Ameer." Inna-wuro ta faÉ—a bayan ta juyo ta kalle shi da murmushi É—auke a kan fuskarta.
"Wai me ya sa Dada ba ta sonmu?" Ya yi tambayar da ta sanya Inna-wuro janye murmushin fuskarta.
"Ameer?" Ta yi ƙarfin halin faɗar hakan fuskarta a haɗe. Ba ta taɓa zata ba, ba ta taɓa kawo wa tun a yanzu za su fahimci cewa Dadar ba ta ƙaunar su ne ba. Sai dai ga shi sun shammace ta. Kafin ya ce komai ta ɗora da faɗin