Sashe 27
Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki kashe ni kawai Adda, ko na dena jin zafin da nake ji a cikin zuciyata. Ki ɗauki wani abun ki caka mini a ƙahon zuciyata Adda, na san tabbas zan ji sassaucin abin da nake ji a zuciyata. Ni kaɗai na san me nake ji, ni kaɗai na san irin raɗaɗi da zafin da nake ji Adda. Don Allah ki kashe ni ko na huta, ke ma ki huta da wannan baƙin cikin da na ja miki, ko hakan ze sa Inna kar ta ji labarin nan." Ya ƙare a raunane yana jujjuya kansa idanunsa na wani irin lumshewa kamar me shirin yin bacci.
"Haɗuwata da su kawai zan iya tunawa. Ban san abin da suke yi ba, har na tsawon kwana biyu. Sun ce mini aikin biredi ne zan din ga yi. Tun daga ranar kamar an sauya ni, shi ne suka soma amfani da ni, ban san yadda aka yi na kasa ƙin komawa gobe ba. Duk da yadda zan ji a zuciyata Allah zai kama mu, zai kuma yi mana azaba, hakan ba ya hana ni zuwa wajen su kullum. Kuma kullum cikin kuka nake Adda, amma ni.. na rasa ma me zan ce." I zuwa lokacin ta dena kukan kallon sa kawai take tana nazarin maganganunsa. Lokacin da ya kai ƙarshe, sai ta ji wasu guntayen hawaye sun sauko mata a kan fuskarta. Ta ja ɗan'uwanta ta rungume tana jin wani sabon kukan na taho mata. Ko babu komai ta san zai samu sassauci a kan abin da yake ji, ko babu komai ze yi kuka a kan kafaɗar 'yar'uwarsa ya ji tabbas fa yana da wajen da zai iya ɗora kansa ya yi kuka. Ai kuwa sai ya lumshe idanunsa yana barin hawayen na sauka a kan fuskarsa tamkar za su ƙare. Sun shafe wajen mintina goma a haka kafin ta ji yana sauke numfashi da gudun gaske. Ta yi azamar sanya hannu ta ɗago shi tana kallan sa.
"Ameer." Ta faÉ—a ganin yana ci gaba da lullumshe idanunsa. Fahimtar abin da take nufi ne ya sanya shi faÉ—in
"Cikina, da ƙirjina Adda.. Ina ji tamkar za su bar jikina. Wani abu nake ji ya tokare mini numfashina." Ya faɗa yana ci gaba da kokawa da numfashinsa. Da sauri ta gyara zamanta tana faɗi cikin rawar murya
"Kar ka damu, za ka samu sauƙi. Kwanta ka yi bacci kaa ji?" Ta faɗa tana taimaka masa, ta kwantar da kansa a kan cinyarta. Runtse idanunsa ya yi ruff, hannunsa na kan ƙirjinsa da yanzun ya fi masa ciwo a kan cikinsa. Ji yake tamkar duk wasu abubuwa da ke cikin ƙirjinsa suna dab da fitowa fili saboda wani irin yanayi da tun da Inna ta haife shi bai taɓa jinsa ba. Shiru Daneen ta yi tana kallon yadda yake sauke numfashi a wahalce, ta runtse idanunta da hawayen suka ƙeƙashe, suka ƙafe gaba ɗaya. Haƙiƙa yau ɗin wata rana ce wadda ba za ta taɓa mantawa da ita ba, yau ɗin wata rana ce da ta kafa musu mummunan tarihi cikin tarihin rayuwarsu. Abin da suke ji a nesa da su sai ga shi ya faru a kan ƙaninta, rabin jikinta. Su kuwa waɗannan mutanen su waye su? Waɗanne irin mugaye ne su, da suka rasa wanda za su lalata sai ƙaramin yaro Ameer? Daga zuwa neman aikin yi don su samar wa kansu abin da za su ci da wanda za su yi guzurin tafiya ƙauyensu? Don mugupnta da rashin tsoron Allah sun lalata mata rayuwar ƙani? Ba sau ɗaya ba ma har fiye da a ƙirga? Sun kuma yi amfani da wani abun can wajen rufe masa baki da jan hankalinsa zuwa wajen, duk da wayo da takatsantsan irin na Ameer? 'Hasbunallahu wa ni'imal wakeel' Ta faɗa a kan laɓɓanta tana runtse idanunta har lokacin bugun zuciyarta bai koma daidai ba. Lallai ko ma mene ne har abada sun gama neman aiki daga ita har ɗan'uwanta, gari na wayewa za su ɗauki hanyar tafiya ƙauyensu da ƙafafunsu, idan ya so in Allah Ya yi su isa suna a raye, idan kuma bai ƙaddara ba Allah Ya ji ƙan su. Haka wannan baƙar ranar ta ƙare suna zaune a wajen, ko wajen da take kwana ba ta koma ba, haka ta ci gaba da zama, kan Ameer na kan cinyarta har zuwa wayewar gari. Sai dai kafin gari ya gama yin haske jikin Ameer ya yi wani irin mahaukacin zafi, ban da karkarwa babu abin da yake yi, da ƙyar yake iya buɗe idanunsa saboda zafin ciwo. Zuwa lokacin Daneen ta gama ruɗewa, tun tana ƙoƙarin danne kukan da ke taho mata har ta kasa. Ta bar shi ya fito saman fuskarta da ke shimfiɗe da damuwa fall.
"Sannu Ameer." Ta sake faÉ—a a karo na barkatai. Da kansa ya yi amfani wajen É—aga mata alamar ya ji ta. Sai dai jikinsa babu abin da ke sake yi sai É—aukar uban zafi mara misaltuwa.
"Adda ina ji kamar ana daddatsa mini ƙashi, zuciyata ta yi mini nauyi." Ya faɗa a sanyaye har lokacin idanunsa a lumshe.
"Sannu Ameer, ko dai mu je asibiti ne?" Ta yi maganar kamar mai tambaya, sai dai kuma a zahiri ba jiran amsar wani take nema ba. Wannan ne dalilin da ya sanya ta miƙewa cikin mutuƙar rikicewa ta nemi taimakon wasu don a ɗaukar mata Ameer ɗin ta kai shi asibiti. Kwata-kwata hankalinta bai kawo mata abin da asibitin za su iya nema ba, ita dai kawai ta ga Ameer ɗin a asibiti a duba shi a ba shi magani ya warke shi ne burinta, inda kuma hankalinta ya tafi.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 18
Da taimakon wasu bayin Allah aka saka mata Ameer cikin napep ɗin da aka tarar mata. Ta yi saurin faɗa wa ciki tana jin gaba ɗaya jikinta na ci gaba da rawa, tamkar ma ƙafarta ba za ta ɗauki nauyin jikinta ba. Babu ɓata lokaci drivern ya ja motar suka soma tafiya ba tare da ya jira jin ta bakinta ba. Saboda ko ba ta masa bayani ba, ya san idan ba asibiti ba babu inda za su tunkara a yanzu. Don haka ya yi hanyar asibitin da ya san ya fi kusa da inda suke. Yadda numfashin Ameer ke wani irin rikicewa, yana kai masa cafka cikin ficewar hayyaci, shi ne abin da ya sake tsorata Daneen. Ta rungumo shi cikin jikinta hawaye na gangaro wa a kan kuncinta, cikin wata dashashshiyar murya ta furta
"Don Allah Ameer kar ka yi mini haka.." Ta kai ƙarshen maganar tana sake sauke idanunta a kan fuskarsa da idanunsa ke kusan a rufe, hannunsa ɗaya na sautin zuciyarsa, ya yin da numfashinsa ke ci gaba da ƙoƙarin barin gangar jikinsa. Abin da ya sanya mai napep ɗin ƙara gudu kenan, don ƙoƙarin ganin sun isa asibiti a ceci ran wannan bawan Allahn da shi kansa yake ganin tamkar abubuwan da yake na fitar rai ne. A haka suka ƙarasa cikin asibitin, Ameer na rungume jikin Daneen, gaba ɗaya ta rasa sukuni, daga zarar ta janyo wannan addu'ar sai ta ji ta kufce mata, hawaye kuwa har ta gaji da tsaida su, ban da sauka kan kuncinta babu abin da suke yi. Zuciyarta na ci gaba da bugun da take ji tamkar za ta faso ƙirjinta ne ta fito. Mai napep ɗin da kansa ya sauka ya ɗaukar mata Ameer da har lokacin ba ya cikin hayyacinsa. Wani irin numfashi yake yi a wahalce, idan ka gan shi ma ba za ka ɗauka yana da rai ba, saboda yadda gaba ɗaya jikinsa ya saki. Sai dai idan ka kalli fuskarsa, ko kuma ka ƙura wa ƙirjinsa ido, shi ne za ka ga yadda yake ɗagawa a wani irin hankali. Bayansa Daneen ta bi da sauri, kamar yadda shi ma yake saurin. Tana tafe tana goge fuskarta da hannayenta, ba tare da ta san abin da take furtawa ba take ci gaba da faɗin abin da ya zo mata a rai.
"Ameer kar ka yi mini haka.. Ka tashi ka warke mu koma wajen Innarmu don girman Allah." Ire-iren maganganun nan take ta furtawa tana bin bayan mai napep ɗin. Har zuwa lokacin da suka isa emergency. Cikin gaggawa aka karɓi Ameer saboda yadda jikinsa ya yi mugun tsamari. Daneen ta zube a kan gwuiwoyinta tana sake fashewa da wani sabon kukan. Ta jima a wajen, ba tare da ta san abin da ya ci gaba da faruwa ba. Ita dai burinta ɗaya ta ji halin da ɗan'uwanta yake ciki.
"Ki yi haƙuri, In Sha Allah zai samu sauƙi. Addu'a za ki yi masa ba kuka ba." Ta jiyo muryar mai napep ɗin nan yana faɗa mata. A hankali ta ɗan ɗaga jajayen idanunta ta kalle shi, da ƙyar cikin dashashshiyar murya ta ce
"Na gode sosai, Allah Ya saka maka da alkhairi." Ta faÉ—a tana lumshe idanunta.
"Babu komai." Ya faÉ—a, kafin ya gyara tsayuwarsa ya ce
"Bari na wuce, Allah Ya ƙara sauƙi. In Allah Ya yarda zuwa an jima zan shigo."
"Toh." Ta faɗa a sanyaye. Ko minti 5 bai yi da tafiya ba, aka nemi ganin waɗanda suka kawo Ameer. Da wani irin sauri Daneen ta miƙe ta shiga office ɗin likitan. Gwaje-gwaje aka ba su rubuce a takarda. Ita dai Daneen ba wannan take buƙatar ji ba. Don haka ta luma ƙwayar idanunta cikin na likitan ta ce
"Don Allah ya jikin ƙanina?" Sai da ya kalle ta, ya ɗan yi jimm kafin ya ce
"Haɗuwata da su kawai zan iya tunawa. Ban san abin da suke yi ba, har na tsawon kwana biyu. Sun ce mini aikin biredi ne zan din ga yi. Tun daga ranar kamar an sauya ni, shi ne suka soma amfani da ni, ban san yadda aka yi na kasa ƙin komawa gobe ba. Duk da yadda zan ji a zuciyata Allah zai kama mu, zai kuma yi mana azaba, hakan ba ya hana ni zuwa wajen su kullum. Kuma kullum cikin kuka nake Adda, amma ni.. na rasa ma me zan ce." I zuwa lokacin ta dena kukan kallon sa kawai take tana nazarin maganganunsa. Lokacin da ya kai ƙarshe, sai ta ji wasu guntayen hawaye sun sauko mata a kan fuskarta. Ta ja ɗan'uwanta ta rungume tana jin wani sabon kukan na taho mata. Ko babu komai ta san zai samu sassauci a kan abin da yake ji, ko babu komai ze yi kuka a kan kafaɗar 'yar'uwarsa ya ji tabbas fa yana da wajen da zai iya ɗora kansa ya yi kuka. Ai kuwa sai ya lumshe idanunsa yana barin hawayen na sauka a kan fuskarsa tamkar za su ƙare. Sun shafe wajen mintina goma a haka kafin ta ji yana sauke numfashi da gudun gaske. Ta yi azamar sanya hannu ta ɗago shi tana kallan sa.
"Ameer." Ta faÉ—a ganin yana ci gaba da lullumshe idanunsa. Fahimtar abin da take nufi ne ya sanya shi faÉ—in
"Cikina, da ƙirjina Adda.. Ina ji tamkar za su bar jikina. Wani abu nake ji ya tokare mini numfashina." Ya faɗa yana ci gaba da kokawa da numfashinsa. Da sauri ta gyara zamanta tana faɗi cikin rawar murya
"Kar ka damu, za ka samu sauƙi. Kwanta ka yi bacci kaa ji?" Ta faɗa tana taimaka masa, ta kwantar da kansa a kan cinyarta. Runtse idanunsa ya yi ruff, hannunsa na kan ƙirjinsa da yanzun ya fi masa ciwo a kan cikinsa. Ji yake tamkar duk wasu abubuwa da ke cikin ƙirjinsa suna dab da fitowa fili saboda wani irin yanayi da tun da Inna ta haife shi bai taɓa jinsa ba. Shiru Daneen ta yi tana kallon yadda yake sauke numfashi a wahalce, ta runtse idanunta da hawayen suka ƙeƙashe, suka ƙafe gaba ɗaya. Haƙiƙa yau ɗin wata rana ce wadda ba za ta taɓa mantawa da ita ba, yau ɗin wata rana ce da ta kafa musu mummunan tarihi cikin tarihin rayuwarsu. Abin da suke ji a nesa da su sai ga shi ya faru a kan ƙaninta, rabin jikinta. Su kuwa waɗannan mutanen su waye su? Waɗanne irin mugaye ne su, da suka rasa wanda za su lalata sai ƙaramin yaro Ameer? Daga zuwa neman aikin yi don su samar wa kansu abin da za su ci da wanda za su yi guzurin tafiya ƙauyensu? Don mugupnta da rashin tsoron Allah sun lalata mata rayuwar ƙani? Ba sau ɗaya ba ma har fiye da a ƙirga? Sun kuma yi amfani da wani abun can wajen rufe masa baki da jan hankalinsa zuwa wajen, duk da wayo da takatsantsan irin na Ameer? 'Hasbunallahu wa ni'imal wakeel' Ta faɗa a kan laɓɓanta tana runtse idanunta har lokacin bugun zuciyarta bai koma daidai ba. Lallai ko ma mene ne har abada sun gama neman aiki daga ita har ɗan'uwanta, gari na wayewa za su ɗauki hanyar tafiya ƙauyensu da ƙafafunsu, idan ya so in Allah Ya yi su isa suna a raye, idan kuma bai ƙaddara ba Allah Ya ji ƙan su. Haka wannan baƙar ranar ta ƙare suna zaune a wajen, ko wajen da take kwana ba ta koma ba, haka ta ci gaba da zama, kan Ameer na kan cinyarta har zuwa wayewar gari. Sai dai kafin gari ya gama yin haske jikin Ameer ya yi wani irin mahaukacin zafi, ban da karkarwa babu abin da yake yi, da ƙyar yake iya buɗe idanunsa saboda zafin ciwo. Zuwa lokacin Daneen ta gama ruɗewa, tun tana ƙoƙarin danne kukan da ke taho mata har ta kasa. Ta bar shi ya fito saman fuskarta da ke shimfiɗe da damuwa fall.
"Sannu Ameer." Ta sake faÉ—a a karo na barkatai. Da kansa ya yi amfani wajen É—aga mata alamar ya ji ta. Sai dai jikinsa babu abin da ke sake yi sai É—aukar uban zafi mara misaltuwa.
"Adda ina ji kamar ana daddatsa mini ƙashi, zuciyata ta yi mini nauyi." Ya faɗa a sanyaye har lokacin idanunsa a lumshe.
"Sannu Ameer, ko dai mu je asibiti ne?" Ta yi maganar kamar mai tambaya, sai dai kuma a zahiri ba jiran amsar wani take nema ba. Wannan ne dalilin da ya sanya ta miƙewa cikin mutuƙar rikicewa ta nemi taimakon wasu don a ɗaukar mata Ameer ɗin ta kai shi asibiti. Kwata-kwata hankalinta bai kawo mata abin da asibitin za su iya nema ba, ita dai kawai ta ga Ameer ɗin a asibiti a duba shi a ba shi magani ya warke shi ne burinta, inda kuma hankalinta ya tafi.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 18
Da taimakon wasu bayin Allah aka saka mata Ameer cikin napep ɗin da aka tarar mata. Ta yi saurin faɗa wa ciki tana jin gaba ɗaya jikinta na ci gaba da rawa, tamkar ma ƙafarta ba za ta ɗauki nauyin jikinta ba. Babu ɓata lokaci drivern ya ja motar suka soma tafiya ba tare da ya jira jin ta bakinta ba. Saboda ko ba ta masa bayani ba, ya san idan ba asibiti ba babu inda za su tunkara a yanzu. Don haka ya yi hanyar asibitin da ya san ya fi kusa da inda suke. Yadda numfashin Ameer ke wani irin rikicewa, yana kai masa cafka cikin ficewar hayyaci, shi ne abin da ya sake tsorata Daneen. Ta rungumo shi cikin jikinta hawaye na gangaro wa a kan kuncinta, cikin wata dashashshiyar murya ta furta
"Don Allah Ameer kar ka yi mini haka.." Ta kai ƙarshen maganar tana sake sauke idanunta a kan fuskarsa da idanunsa ke kusan a rufe, hannunsa ɗaya na sautin zuciyarsa, ya yin da numfashinsa ke ci gaba da ƙoƙarin barin gangar jikinsa. Abin da ya sanya mai napep ɗin ƙara gudu kenan, don ƙoƙarin ganin sun isa asibiti a ceci ran wannan bawan Allahn da shi kansa yake ganin tamkar abubuwan da yake na fitar rai ne. A haka suka ƙarasa cikin asibitin, Ameer na rungume jikin Daneen, gaba ɗaya ta rasa sukuni, daga zarar ta janyo wannan addu'ar sai ta ji ta kufce mata, hawaye kuwa har ta gaji da tsaida su, ban da sauka kan kuncinta babu abin da suke yi. Zuciyarta na ci gaba da bugun da take ji tamkar za ta faso ƙirjinta ne ta fito. Mai napep ɗin da kansa ya sauka ya ɗaukar mata Ameer da har lokacin ba ya cikin hayyacinsa. Wani irin numfashi yake yi a wahalce, idan ka gan shi ma ba za ka ɗauka yana da rai ba, saboda yadda gaba ɗaya jikinsa ya saki. Sai dai idan ka kalli fuskarsa, ko kuma ka ƙura wa ƙirjinsa ido, shi ne za ka ga yadda yake ɗagawa a wani irin hankali. Bayansa Daneen ta bi da sauri, kamar yadda shi ma yake saurin. Tana tafe tana goge fuskarta da hannayenta, ba tare da ta san abin da take furtawa ba take ci gaba da faɗin abin da ya zo mata a rai.
"Ameer kar ka yi mini haka.. Ka tashi ka warke mu koma wajen Innarmu don girman Allah." Ire-iren maganganun nan take ta furtawa tana bin bayan mai napep ɗin. Har zuwa lokacin da suka isa emergency. Cikin gaggawa aka karɓi Ameer saboda yadda jikinsa ya yi mugun tsamari. Daneen ta zube a kan gwuiwoyinta tana sake fashewa da wani sabon kukan. Ta jima a wajen, ba tare da ta san abin da ya ci gaba da faruwa ba. Ita dai burinta ɗaya ta ji halin da ɗan'uwanta yake ciki.
"Ki yi haƙuri, In Sha Allah zai samu sauƙi. Addu'a za ki yi masa ba kuka ba." Ta jiyo muryar mai napep ɗin nan yana faɗa mata. A hankali ta ɗan ɗaga jajayen idanunta ta kalle shi, da ƙyar cikin dashashshiyar murya ta ce
"Na gode sosai, Allah Ya saka maka da alkhairi." Ta faÉ—a tana lumshe idanunta.
"Babu komai." Ya faÉ—a, kafin ya gyara tsayuwarsa ya ce
"Bari na wuce, Allah Ya ƙara sauƙi. In Allah Ya yarda zuwa an jima zan shigo."
"Toh." Ta faɗa a sanyaye. Ko minti 5 bai yi da tafiya ba, aka nemi ganin waɗanda suka kawo Ameer. Da wani irin sauri Daneen ta miƙe ta shiga office ɗin likitan. Gwaje-gwaje aka ba su rubuce a takarda. Ita dai Daneen ba wannan take buƙatar ji ba. Don haka ta luma ƙwayar idanunta cikin na likitan ta ce
"Don Allah ya jikin ƙanina?" Sai da ya kalle ta, ya ɗan yi jimm kafin ya ce