Sashe 21
Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki gaida ta, ina sauri ne." Daga haka ya fice daga ɗakin. Kai tsaye inda ya ajje motarsa ya nufa, yana tafe yana waya da Sultanah da ya sanar da ita za su yi maganar tun da yanzu da baƙi a gidan kuma tana aiki. Sosai ta yi wa yayan nata godiya kafin suka yi sallama. Har ya buɗe ƙofar motarsa yana ƙoƙarin shiga, sai kuma ya dakata idanunsa a kan wayarsa. Kusan mintuna wajen nawa yana kalla, kafin ya rufe motar kai tsaye ya koma cikin gidan. Part ɗinsa ya wuce a ɗan hanzarce zuciyarsa cike fall da saƙe-saƙe.
... A bakin wani tafkeken restaurant ya yi parking na motarsa, Daneen da Ameer suka bi shi da kallo lokacin da ya juya ya kalle ta ya ce
"Ku yi haƙuri ina ɗan zuwa, ba daɗewa zan yi ba." Jinjina kai kawai Daneen ta yi, don a lokacin ji take bakinta ya yi mata nauyi. Buɗe motar ya yi ya fice kai tsaye ya shige cikin restaurant ɗin. Bayan wasu sakanni Daneen ta juya ta kalli Ameer ta ce
"Guduwa za mu yi Ameer."
"Me ya sa Adda?" Ameer ya faÉ—a da mamaki.
"Kawai tafiya za mu yi Ameer, hankalina ya kasa kwanciya da mutanen nan, duk yadda aka yi akwai wani abun da suke ɓoye mini." Ta ƙare maganar muryarta a raunane.
"Amma na ji ya ce gidan aikin ze kai mu."
"Ameer zuciyata ta kasa samun sukuni, tun fitowar mu daga gida har zuwa yanzun. Yanzu kuma da zuwan mu gidan nan faɗuwar gaba ta ƙi bari na, duk kuwa da addu'ar da nake ta yi. Ina ganin babu alkhairi zuwan mu gidan nan. Da ƙyar idan haɗuwar mu da mutanen nan alkhairi ce. Kawai mu gudu mu bar su." Shiru Ameer ya yi yana cigaba da nazarin yayar tasa. Duk wasu alamomin ruɗewa sun bayyana a kan fuskarta, yadda take magana kuma kana gani ka san daga zuciyarta ne take faɗa. Don haka cikin son ba ta ƙwarin gwuiwa ya ce
"Toh mu tafi ɗin. Amma ta ya ya?" Ba tare da ta amsa wa Ameer tambayar da ya yi mata ba ta sanya hannunta a kan murfin ƙofar da ke gefen ta. Cikin karambani ta ga wajen da tabbas ya fi kama da inda za ta taɓa ƙofar ta buɗu, kamar yadda ta ga ya yi da zai fita. Sai dai kwata-kwata ta ƙi buɗuwa. Ta taɓa ta taɓa ta ƙi buɗuwa. Ameer da ya lura da yadda take yi, shi ma ya taɓa gefensa amma shiru ta ƙi buɗuwa.
"Ko dai ba haka ake ba?" Girgiza kai Daneen ta yi kafin ta ce
"Tabbas nan ya taɓa da zai fita. Sai dai kuma idan ana iya kulle wa kamar ƙofa."
"Eh kuma haka ne." Ameer ya faÉ—a yana jinjina kai.
"Toh yanzu ya za mu yi?" Kafin Daneen ta kai ga tunanin komai ko ta ce wani abun, aka buɗe ƙofar aka shigo. Mutumin ya ajje ledar hannunsa kafin ya tashi motar suka cigaba da tafiya. Shiru ne ya wanzu cikin motar, kowa da abin da yake saƙa wa cikin ransa. Har zuwa lokacin da ya sake tsaida motar, kamar ɗazun ya sake juyawa ya kalli Daneen ya ce
"Minti 1 gimbiya." Wannan gimbiyar da ya ambata ba ƙaramin kaɗa 'ya'yan cikin Daneen ya yi ba, cikin ƙanƙanin lokaci bugun zuciyarta ya ƙaru. Ta yi ƙarfin halin jinjina kai kawai. Hakan ne ya sa ya fice daga motar.
"Adda ya yi nisa fa." Ameer ya faɗa yana kallan Daneen da ke zaune tamkar wadda aka dasa. Duk da yadda tsoro ke shigar ta, wanda ya yi silar saka wa jikinta ya soma rawa. Hakan bai hana ta runtse idanunta ba, ta kai hannunta kan ƙofar ta sake tura wa cike da takatsantsan, cikin zuciyarta tana fatan kamar yadda suka tsammata su yi tozali da hakan, wato su ga ya bar motar a buɗe, a maimakon ɗazu da ya kulle su.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 14
Cikin sa'a kuwa sai jin ƙofar ta yi ta tafi, ta juya cikin wani irin farin ciki ta kalli Ameer. Farin cikin da ya gaza ɓoyuwa har a kan fuskarta. Ba tare da ta ce masa komai ba, ya saka hannu ya buɗe ƙofar gefen sa. Cikin sakannin da basu wuce biyar ba suka fice daga cikin motar. Ko tsayawa su rufe ma ba su yi ba, gaba ɗaya hankalinsu ya yi gaba. Don haka da gudu suka soma barin wajen hannayensu cikin na juna. Kasancewar duhun magribh ya mamaye garin ya sanya waɗanda ke lura da su ɗin ba su da yawa. Musamman da ya kasance hankalin da dama ya tafi kan masallacin da suke ƙoƙarin zuwa. Sai da suka yi mugun nisan da suka san sun yi wa mutumin nan nisa kafin suka suka soma rage gudun. Wani irin numfashi a gurguje a gurguje Daneen ke saukewa saboda yadda numfashinta ke sarƙewa. Hannun Ameer ta sake riƙowa tana dawo da shi baya lokacin da ta zube a wani waje tana ji tamkar numfashinta na ƙoƙarin barin gangar jikinta.
"Ameer.. na.. gaji." Ta harhaɗa kalmomin ta faɗa hannunta dafe da ƙirjinta. Dawowa ya yi ya zauna cikin matuƙar tashin hankali yana kallan fuskarta ya ce
"Sannu Adda. Ƙishirwa kike ji?" Ya tambaya yana kallan yadda take cigaba da ajje taggwan numfashi tana wani lumshe idanunta. Jinjina kai ta yi, har lokacin idanunta na lumshewa suna kuma buɗewa.
"Ki zauna a nan kin ji? Bari na je na samo miki ruwa." Ya faɗa yana miƙewa. Hannunsa ta sake riƙowa tana girgiza kai ta ce
"A'ah kar ka je ko'ina, zauna kawai." Girgiza kai Ameer ya yi tausayin er'uwar tasa na kama shi ya ce
"A'ah Adda, ƙishirwa kike ji. Ki zauna a nan don Allah kar ki je ko'ina ruwa kawai zan samo miki yanzun nan kin ji?" Be jira ta amsa ba, ya zame hannunsa ya bar wajen. Cigaba da zama ta yi kanta na kallan ƙasa tana ji tamkar ba za ta ƙara ƙwaƙwƙwaran minti 1 a wajen ba ran da ke gangar jikinta zai bar ta. Babu daɗewa kuwa sai ga Ameer nan ya dawo a guje hannunsa ɗauke da robar ruwa, ya ƙarasa da sauri yana kiran sunan Addar tasa.
"Tashi ki sha kin ji?" Ya faɗa yana ɗago ta, babu musu ta tashi zaune sosai. Ta karɓi ruwan duk da yadda hannunta ke rawa, ta kai baki. Tun da ta kafa ba ta sauke ba sai da ta shanye tass, kafin ta ajje tana sauke ajiyar zuciya.
"Sannu." Shi ne abin da Ameer ke ta maimaitawa yana kallan Daneen ɗin jikinsa a matuƙar sanyaye. Yana daga cikin halayensa shiga damuwa duk lokacin da Addar tasa ba ta da lafiya, shi ya sa ma ya fi so shi ya yi cutar a kan ita ta yi, don ta fi shi shan wahala. Musamman kuma a yanzu da suke su kaɗai babu Inna-wuronsu. Lallai sun yi matuƙar kuskuren baro ƙauyensu. Be ƙarasa tunanin ba ya jiyo muryar Daneen na faɗin
"Mu je mu yi Sallah, bacci nake ji Ameer." Kallan inda suke ya yi, idan har be yi kuskuren fahimta ba, kamar cikin kasuwa ne nan ɗin suke. Kuma lokacin da ya je nemo mata ruwa, ya ga mutane mata da maza ƙanana, almajirai da sauransu kowa ya kama waje kamar dai masu shirin kwana a wajen. Kenan idan haka ne su ma za su iya kwana a cikin kasuwar? Ya tambayi kansa yana cigaba da kallan cikin kasuwar.
"Sai dai mu kwana a cikin kasuwar nan Adda, na ga ba mu kaɗai ne mara sa gida ba. Idan ya so zuwa gobe sai mu nemi inda za mu samu kuɗin koma wa ƙauyenmu." Da sauri Daneen ta ɗaga idanunta ta kalli Ameer. Wato duk abin da ya faru tunani yake za su kuma shiga wani gidan su nemi aiki? Ta girgiza kai kafin ta ce a sanyaye
"Kowanne aiki za mu yi ba za mu kuma shiga gidan mutane ba. Gwara mu yi ko da aikin ƙarfi ne a cikin mutane mu karɓi kuɗinmu mu tafi." Ta ƙare tana ɗan sauke numfashi a hankali. Jinjina kai Ameer ya yi cike da amincewa da zancen Addar tasa.
.. A ɗaya ɓangaren kuwa, hannunsa ɗauke da wata leda ya fito. Tun kafin ya ƙarasa inda motar take ya ji gabansa ya faɗi, saboda yadda idanunsa ke masa wani mummunan gizo. Haka dai ya ƙarasa, sai dai tun kafin ya kai ga buɗe motar ya hangi yadda gaba ɗaya ƙofofi biyun motar suke a buɗe. Cike da fargaba ya ƙarasa, ya duba cikin motar, babu kowa. Ya sake dubawa duk da ya riga da ya tabbatar ba sa cikin motar. Juyawa ya shiga yi ko Allah zai sa ya hango inda suka nufa, sai dai ko ƙurarsu bai gani ba. Hannunsa har rawa yake lokacin da ya fiddo da wayarsa ya shiga neman layin Aunty, har wani huci yake fitar wa daga bakinsa.
"Yarinyar nan ta dawo ne?" Ya tambaya duk da a karan kansa sai da ya ji tambayar da ya yi kamar rainin hankali ce.
"Ban gane ba? Wace yarinya kenan?"
"Yarinyar da na siya yanzu a wajen ki mana." Ya ba ta amsa a fusace. Cikin tashin hankali da rashin sanin abin yi Aunty ta miƙe tsaye, tana jin faɗuwar gaba na ziyartarta. Da ƙyar ta iya ƙarfin halin faɗin
"Ba tare kuka fita ba?" Be ce komai ba sai katse wayar da ya yi. Ta sauke wayar daga kunnenta tana bin ta da kallo. Kenan yarinyar guduwa ta yi ko kuwa? Amma shi wane irin sake ya yi da har ta gudar masa, bayan uban kuɗin da ya biya ya siye ta? Soma zagaye ɗakin ta yi tana cigaba da tunane-tunane, ita ba komai ke ci mata tuwo a ƙwarya ba, illa yadda za ta maida masa da kuɗinsa idan har da gaske yarinyar guduwa ta yi.
... A bakin wani tafkeken restaurant ya yi parking na motarsa, Daneen da Ameer suka bi shi da kallo lokacin da ya juya ya kalle ta ya ce
"Ku yi haƙuri ina ɗan zuwa, ba daɗewa zan yi ba." Jinjina kai kawai Daneen ta yi, don a lokacin ji take bakinta ya yi mata nauyi. Buɗe motar ya yi ya fice kai tsaye ya shige cikin restaurant ɗin. Bayan wasu sakanni Daneen ta juya ta kalli Ameer ta ce
"Guduwa za mu yi Ameer."
"Me ya sa Adda?" Ameer ya faÉ—a da mamaki.
"Kawai tafiya za mu yi Ameer, hankalina ya kasa kwanciya da mutanen nan, duk yadda aka yi akwai wani abun da suke ɓoye mini." Ta ƙare maganar muryarta a raunane.
"Amma na ji ya ce gidan aikin ze kai mu."
"Ameer zuciyata ta kasa samun sukuni, tun fitowar mu daga gida har zuwa yanzun. Yanzu kuma da zuwan mu gidan nan faɗuwar gaba ta ƙi bari na, duk kuwa da addu'ar da nake ta yi. Ina ganin babu alkhairi zuwan mu gidan nan. Da ƙyar idan haɗuwar mu da mutanen nan alkhairi ce. Kawai mu gudu mu bar su." Shiru Ameer ya yi yana cigaba da nazarin yayar tasa. Duk wasu alamomin ruɗewa sun bayyana a kan fuskarta, yadda take magana kuma kana gani ka san daga zuciyarta ne take faɗa. Don haka cikin son ba ta ƙwarin gwuiwa ya ce
"Toh mu tafi ɗin. Amma ta ya ya?" Ba tare da ta amsa wa Ameer tambayar da ya yi mata ba ta sanya hannunta a kan murfin ƙofar da ke gefen ta. Cikin karambani ta ga wajen da tabbas ya fi kama da inda za ta taɓa ƙofar ta buɗu, kamar yadda ta ga ya yi da zai fita. Sai dai kwata-kwata ta ƙi buɗuwa. Ta taɓa ta taɓa ta ƙi buɗuwa. Ameer da ya lura da yadda take yi, shi ma ya taɓa gefensa amma shiru ta ƙi buɗuwa.
"Ko dai ba haka ake ba?" Girgiza kai Daneen ta yi kafin ta ce
"Tabbas nan ya taɓa da zai fita. Sai dai kuma idan ana iya kulle wa kamar ƙofa."
"Eh kuma haka ne." Ameer ya faÉ—a yana jinjina kai.
"Toh yanzu ya za mu yi?" Kafin Daneen ta kai ga tunanin komai ko ta ce wani abun, aka buɗe ƙofar aka shigo. Mutumin ya ajje ledar hannunsa kafin ya tashi motar suka cigaba da tafiya. Shiru ne ya wanzu cikin motar, kowa da abin da yake saƙa wa cikin ransa. Har zuwa lokacin da ya sake tsaida motar, kamar ɗazun ya sake juyawa ya kalli Daneen ya ce
"Minti 1 gimbiya." Wannan gimbiyar da ya ambata ba ƙaramin kaɗa 'ya'yan cikin Daneen ya yi ba, cikin ƙanƙanin lokaci bugun zuciyarta ya ƙaru. Ta yi ƙarfin halin jinjina kai kawai. Hakan ne ya sa ya fice daga motar.
"Adda ya yi nisa fa." Ameer ya faɗa yana kallan Daneen da ke zaune tamkar wadda aka dasa. Duk da yadda tsoro ke shigar ta, wanda ya yi silar saka wa jikinta ya soma rawa. Hakan bai hana ta runtse idanunta ba, ta kai hannunta kan ƙofar ta sake tura wa cike da takatsantsan, cikin zuciyarta tana fatan kamar yadda suka tsammata su yi tozali da hakan, wato su ga ya bar motar a buɗe, a maimakon ɗazu da ya kulle su.
*♡☆DANEEN☆♡*
Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)
Mikiya Writers Ass..
Book 1
Pg 14
Cikin sa'a kuwa sai jin ƙofar ta yi ta tafi, ta juya cikin wani irin farin ciki ta kalli Ameer. Farin cikin da ya gaza ɓoyuwa har a kan fuskarta. Ba tare da ta ce masa komai ba, ya saka hannu ya buɗe ƙofar gefen sa. Cikin sakannin da basu wuce biyar ba suka fice daga cikin motar. Ko tsayawa su rufe ma ba su yi ba, gaba ɗaya hankalinsu ya yi gaba. Don haka da gudu suka soma barin wajen hannayensu cikin na juna. Kasancewar duhun magribh ya mamaye garin ya sanya waɗanda ke lura da su ɗin ba su da yawa. Musamman da ya kasance hankalin da dama ya tafi kan masallacin da suke ƙoƙarin zuwa. Sai da suka yi mugun nisan da suka san sun yi wa mutumin nan nisa kafin suka suka soma rage gudun. Wani irin numfashi a gurguje a gurguje Daneen ke saukewa saboda yadda numfashinta ke sarƙewa. Hannun Ameer ta sake riƙowa tana dawo da shi baya lokacin da ta zube a wani waje tana ji tamkar numfashinta na ƙoƙarin barin gangar jikinta.
"Ameer.. na.. gaji." Ta harhaɗa kalmomin ta faɗa hannunta dafe da ƙirjinta. Dawowa ya yi ya zauna cikin matuƙar tashin hankali yana kallan fuskarta ya ce
"Sannu Adda. Ƙishirwa kike ji?" Ya tambaya yana kallan yadda take cigaba da ajje taggwan numfashi tana wani lumshe idanunta. Jinjina kai ta yi, har lokacin idanunta na lumshewa suna kuma buɗewa.
"Ki zauna a nan kin ji? Bari na je na samo miki ruwa." Ya faɗa yana miƙewa. Hannunsa ta sake riƙowa tana girgiza kai ta ce
"A'ah kar ka je ko'ina, zauna kawai." Girgiza kai Ameer ya yi tausayin er'uwar tasa na kama shi ya ce
"A'ah Adda, ƙishirwa kike ji. Ki zauna a nan don Allah kar ki je ko'ina ruwa kawai zan samo miki yanzun nan kin ji?" Be jira ta amsa ba, ya zame hannunsa ya bar wajen. Cigaba da zama ta yi kanta na kallan ƙasa tana ji tamkar ba za ta ƙara ƙwaƙwƙwaran minti 1 a wajen ba ran da ke gangar jikinta zai bar ta. Babu daɗewa kuwa sai ga Ameer nan ya dawo a guje hannunsa ɗauke da robar ruwa, ya ƙarasa da sauri yana kiran sunan Addar tasa.
"Tashi ki sha kin ji?" Ya faɗa yana ɗago ta, babu musu ta tashi zaune sosai. Ta karɓi ruwan duk da yadda hannunta ke rawa, ta kai baki. Tun da ta kafa ba ta sauke ba sai da ta shanye tass, kafin ta ajje tana sauke ajiyar zuciya.
"Sannu." Shi ne abin da Ameer ke ta maimaitawa yana kallan Daneen ɗin jikinsa a matuƙar sanyaye. Yana daga cikin halayensa shiga damuwa duk lokacin da Addar tasa ba ta da lafiya, shi ya sa ma ya fi so shi ya yi cutar a kan ita ta yi, don ta fi shi shan wahala. Musamman kuma a yanzu da suke su kaɗai babu Inna-wuronsu. Lallai sun yi matuƙar kuskuren baro ƙauyensu. Be ƙarasa tunanin ba ya jiyo muryar Daneen na faɗin
"Mu je mu yi Sallah, bacci nake ji Ameer." Kallan inda suke ya yi, idan har be yi kuskuren fahimta ba, kamar cikin kasuwa ne nan ɗin suke. Kuma lokacin da ya je nemo mata ruwa, ya ga mutane mata da maza ƙanana, almajirai da sauransu kowa ya kama waje kamar dai masu shirin kwana a wajen. Kenan idan haka ne su ma za su iya kwana a cikin kasuwar? Ya tambayi kansa yana cigaba da kallan cikin kasuwar.
"Sai dai mu kwana a cikin kasuwar nan Adda, na ga ba mu kaɗai ne mara sa gida ba. Idan ya so zuwa gobe sai mu nemi inda za mu samu kuɗin koma wa ƙauyenmu." Da sauri Daneen ta ɗaga idanunta ta kalli Ameer. Wato duk abin da ya faru tunani yake za su kuma shiga wani gidan su nemi aiki? Ta girgiza kai kafin ta ce a sanyaye
"Kowanne aiki za mu yi ba za mu kuma shiga gidan mutane ba. Gwara mu yi ko da aikin ƙarfi ne a cikin mutane mu karɓi kuɗinmu mu tafi." Ta ƙare tana ɗan sauke numfashi a hankali. Jinjina kai Ameer ya yi cike da amincewa da zancen Addar tasa.
.. A ɗaya ɓangaren kuwa, hannunsa ɗauke da wata leda ya fito. Tun kafin ya ƙarasa inda motar take ya ji gabansa ya faɗi, saboda yadda idanunsa ke masa wani mummunan gizo. Haka dai ya ƙarasa, sai dai tun kafin ya kai ga buɗe motar ya hangi yadda gaba ɗaya ƙofofi biyun motar suke a buɗe. Cike da fargaba ya ƙarasa, ya duba cikin motar, babu kowa. Ya sake dubawa duk da ya riga da ya tabbatar ba sa cikin motar. Juyawa ya shiga yi ko Allah zai sa ya hango inda suka nufa, sai dai ko ƙurarsu bai gani ba. Hannunsa har rawa yake lokacin da ya fiddo da wayarsa ya shiga neman layin Aunty, har wani huci yake fitar wa daga bakinsa.
"Yarinyar nan ta dawo ne?" Ya tambaya duk da a karan kansa sai da ya ji tambayar da ya yi kamar rainin hankali ce.
"Ban gane ba? Wace yarinya kenan?"
"Yarinyar da na siya yanzu a wajen ki mana." Ya ba ta amsa a fusace. Cikin tashin hankali da rashin sanin abin yi Aunty ta miƙe tsaye, tana jin faɗuwar gaba na ziyartarta. Da ƙyar ta iya ƙarfin halin faɗin
"Ba tare kuka fita ba?" Be ce komai ba sai katse wayar da ya yi. Ta sauke wayar daga kunnenta tana bin ta da kallo. Kenan yarinyar guduwa ta yi ko kuwa? Amma shi wane irin sake ya yi da har ta gudar masa, bayan uban kuɗin da ya biya ya siye ta? Soma zagaye ɗakin ta yi tana cigaba da tunane-tunane, ita ba komai ke ci mata tuwo a ƙwarya ba, illa yadda za ta maida masa da kuɗinsa idan har da gaske yarinyar guduwa ta yi.