Sashe 48
Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ba zan iya ba. Ni ba kowa ba ce, face wadda ke zaune a cikin gidanku saboda alfarma. Kar ka ce za ka saka mini ba ka ƙoda da na yi ta hanyar aure na. Ba zan iya ba." Ta ƙare maganar tana fashewa da kuka. Duk da ba har zuciyarta take faɗar hakan ba, kawai ta faɗa ne don kare kanta, saboda yadda ta lura da kallon tuhuma ɗin da yake bin ta da shi. Doguwar ajiyar zuciya Tareeq ya sauke mara sauti. Ko babu komai wannan maganganun da ta faɗa sun ruguza wannan karyayyen tunanin nasa da ya fara.
"Kar ki yanke hukunci cikin gaggawa. Ki je gaba ɗaya yinin yau ki yi tunani. Abin da nake so da ke kuma, ki cire wannan tunanin na cewar zan aure ki ne saboda in biya ki ƙodarki da kika ba ni. A'ah." Ya faɗa yana girgiza kai.
"Har abada ba zan iya biyan ki ba."
"Ba zan iya ba." Ta faɗa da ƙarfin gaske, tana jin wata irin wutar ƙiyayyarsa na sake ruruwa a cikin zuciyarta. Wannan wace irin rana ce? Wanda ya zamo silar mutuwar Ameer shi ne yake neman da ta amince ta aure shi? Wane irin sakaci ita kuwa ta yi? Ta yaya ma za ta iya aurensa bayan ta shigo gidan ne da niyyar ɗaukar fansa, ba kuma a kan kowa ba face shi? Ta aure shi ta ce ta auri me ke nan?
"Saboda yanzu ba na taka wa a kan ƙafata?" Ya jefa mata tambayar muryarsa a dake. Da sauri ta ɗaga idanunta ta kalle shi. Ya jinjina mata kai bayan ya ɗan saki wani murmushi ya ce
"Duk abin da kika yanke ki sanar da ni. Amma ki sani, idan ba ki amince ba, zan ɗauki hakan a matsayin saboda abin da ya sami ƙafata ne. Ko da yake, babu damuwa za ki iya tafiya." Ai tun kafin ya dire maganar ta soma barin wajen cike da sassarfa, haɗa hanya kawai take yi, kamar za ta kifa. A haka dai har ta ƙarasa ɗakinsu. Zubewa ta yi a kan gadon tana fashewa da wani kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Yau ɗin wata irin kewar Ameer ce ta dawo mata sabuwa, sai take ji tamkar yau ne Ameer ɗinta ya tafi ya bar ta. Sai take ji tamkar a yanzu ne suke magana ita da Ameer, maganar tasu da ta zamo ta ƙarshe. Ta cure cikin bargo waje ɗaya tana ci gaba da sheshsheƙar kuka cike da kewar Ameer da Innarsu. Ji take kamar ta watsar da komai ta koma ƙauyensu. Toh amma kuma ba ta da tabbacin idan ta koma ƙauyen ma za ta sami Innarsu, uwa uba kuma idan har ta bar gidan, ke nan hakan na nufin ruhin Ameer ya tafi a banza ke nan? Bayan ga shi tana da damar da za ta iya yin wani abu, wanda har zai kai su ga samun nasara. Wannan dalili, shi ne kaɗai abin da ya sa ta ji zuciyarta ta yi na'am da ci gaba da zaman ta cikin gidan, daga nan sai ta bazama ƙauyensu don biɗar Innarsu. Ta shafe fiye da awa ɗaya a wajen, kafin kamar wadda aka mintsina ta sakko daga kan gadon, kai tsaye toilet ta faɗa, ta rufe shi, sannan ta danna kiran Yohana. Jin tana neman katsewa kafin ya ɗaga ne ya sanya ta faɗin
"Ka ɗaga mana, ka ɗaga mana.." Daf da za ta tsinke ɗin kuwa ya ɗaga, ta sauke wata ƙatuwar ajiyar zuciya.
"Daneen." Ya ambata kamar yadda ya saba kullum saboda tsaro.
"Na'am." Ta ambata da muryarta da ta fara dashewa saboda kukan da ta sha.
"Oh my gosh! Me ya faru Cutie?" Ya faɗa cike da mamakin yadda ya ji muryarta ta sauya. Sai da ta ja wata ajiyar zuciyar kafin ba tare da ɓata lokaci ba ta shiga kora masa duk wasu abubuwa da suka faru.
"Puhahaha..." Ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya, wadda ta matuƙar ba wa Daneen mamaki, wanda har hakan sai da ya bayyana a kan fuskarta. Ya kai wajen minti ɗaya kafin ya ce hallau dai cikin gurɓatacciyar hausarsa.
"Buɗe kunnenki da kyau ki ji. Wannan wata dama ce muka samu. Sanar da shi kin amince da aurensa, da ma ba hanyar shiga ɗakinsa muke nema ba? Idan kika aure shi ai dole ki shiga ɗakinsa, ko ma in ce dole a kai ki ɗakinsa. Kin ga damar da muke so ta samu, a cikin kwana biyu za ki iya samar mana abin da muke buƙata, kin fahimta? Saboda haka kar ki damu, aure ne kawai da za ku yi na kwanaki ƙidayayyu, daga zarar kin samo mana abin da muke nema shi ke nan sai ki nemi takardar saki." Tun da ya fara magana take jin zuciyarta na wani irin harbawa kamar za ta fito daga ƙirjinta. Ita dai haka nan kawai take jin tsoro na shigar ta, duk da kamar yadda ya faɗa ɗin hakan shi ne mafitar su, toh amma ta yaya za ta yi aure ba tare da sanin Innarta ba?
"Kuma ko an ce za a je ƙauyenku don sanar da kishiyar kakarku kamar yadda kika faɗa wa Alhaji Dikko, ki san yadda za ki ki hana, saboda kar a kwaɓa mana aiki." Ta jiyo muryar Yohanan kamar ya san abin da take tunani. Ta sake yin shiru na tsawon wasu sakannin kafin ta buɗe baki da ƙyar ta ce
"Toh." Daga haka ta katse wayar, ta yi shiru tana sake nazarin abubuwan da ya faɗa. Tabbas idan dai har mafita suke so, toh abin da Yohana ya faɗa shi ne daidai. Sai dai kuma idan ta haƙura da ɗaukar fansar ne. Abin da kuma ba ta ji zuciyarta ta yi na'am da hakan ba. Ran ɗan'uwanta fa, Ran Ameer ɗinta fa. Ta runtse idanunta a hankali zuciyarta a cunkushe, wanda ta rasa dalilin hakan.
... "Sultanah ina yi miki magana kin yi shiru, wai ma ni sa'ar ki ce ne?" Maami ta faÉ—a a fusace tana kallon ta. Runtse idanunta Sultanah ta yi cikin rashin sanin abin yi, ta rasa me Maamin take nufi da ita. Ruwan da ke gaban ta Maami ta É—auka ta kai bakinta ko za ta daina jin zafin da take ji cikin zuciyarta.
"Maami ba zan iya auren wani idan ba Yah Abdoul ba. Ban taɓa faɗa miki ba ne, amma na daɗe da soyayyar Yah Abdoul danƙare a cikin zuciyata. Kuma maganar da nake miki yanzu ma haka mun yi nisa ni da shi, har ya ce ma nan da lokaci kaɗan zai sanar wa da Abbansa." Wata daƙiƙiyar ƙwarewa da Maami ta yi, ita ce ta sanya Sultanah tana kai ƙarshen maganar da ta ɗauko ta yi shiru. Ta miƙe da sauri tana faɗin
"Sannu Maami." Ta faɗa bayan ta zuba ruwa cikin tambulan ta miƙa mata. Hannu Maami ta saka ta karɓa kawai, sai dai maimakon ta sha ruwan sai ta ci gaba da tarin har zuwa lokacin da ya yi sauƙi ba tare da ta sha ruwan ba. Kallon ta kawai Sultanah take yi, tana fata ta kalle ta da idon rahama, ta kalle ta da idon tausayi irin na mahaifiya.
"Wanne Abdoul É—in kike nufi?" Wata irin ajiyar zuciya Sultanah ta sauke, tana jin daÉ—in tambayar Maamin. Ta yi murmushi kana ta ce
"Maami Yah Abdoul fa namu, Yah Abdoul na Yah Tareeq." Ajiye kofin hannunta Maami ta yi, duk wani tashin hankali ya gama bayyana a kan fuskarta. Sai dai cikin dakiya ta ce, duk da yadda harshenta ke ƙoƙarin bijire mata wajen yin maganar, amma haka ta daure, ta cije ta yi iya bakin ƙoƙarinta.
"Na riga na zaɓa miki miji Sultanah." Shi ne kawai abin da ta iya faɗa. A take idanun Sultanah suka tara ƙwalla, ban da bugawa babu abin da zuciyarta ke yi. Cikin tashin hankali ta ce
"Maami ki yi mini afuwa. Ina son Yah Abdoul, wallahi ina son shi matuƙa, zuciyata za ta iya bugawa idan ban same shi ba. Maami taɓa ki ji yadda zuciyata ke harbawa, ban san halin da zan tsinci kaina ciki ba idan maganar da kike faɗa ta zama gaskiya. Maami Abdoul fa abokin Yah Tareeq, ɗan gidan aminin Abeey, kuma ɗan gidan amiyarki. Ki yi mini wannan alfarmar don girman Allah Maami." Ta ƙare maganar tana fashewa da sabon kuka. Kukan da ke fitowa tun daga ƙasan zuciyarta, wadda ke mata wani irin zafi, zafin da rabon da ta ji shi tun kafin Abdoul ya zo mata da tayin soyayyarsa. Ta daɗe rabon da ta ji shi, har ta fara sabawa da farin ciki, sai ga shi rana ɗaya, Maami na neman tarwatsa mata wannan farin cikin. Don kuwa ta san raba ta da Abdoul babban abu ne, wanda ba ta sani ba ko zuciyarta na da ƙarfin ɗauka. Ganin da ta yi Maami ta yi mata shiru ne ya sanya jikinta ya ƙara yin sanyi. Ta girgiza kanta tana jin yadda lokaci guda ya yi mata wani gingirin.
"Maamina ki ce wani abu mana don Allah." Ta faɗa cikin kuka. Sai bayan shuɗewar wasu sakanni masu yawa, sannan Maami ta miƙe, cikin ƙarfin hali ta ce
"Gwara ma ki cire ranki, don wallahi ba za ki auri Abdoul ba. Ke kika ce za ki ɗaga mini hankali wallahi sai na tsine miki a banza. Ki kama kanki, idan ba haka ba ran kowa ya ɓaci. Idan na ce kowa ina nufin kowa." Ta dakata a nan sannan ta ci gaba da faɗin
"Kar ki yanke hukunci cikin gaggawa. Ki je gaba ɗaya yinin yau ki yi tunani. Abin da nake so da ke kuma, ki cire wannan tunanin na cewar zan aure ki ne saboda in biya ki ƙodarki da kika ba ni. A'ah." Ya faɗa yana girgiza kai.
"Har abada ba zan iya biyan ki ba."
"Ba zan iya ba." Ta faɗa da ƙarfin gaske, tana jin wata irin wutar ƙiyayyarsa na sake ruruwa a cikin zuciyarta. Wannan wace irin rana ce? Wanda ya zamo silar mutuwar Ameer shi ne yake neman da ta amince ta aure shi? Wane irin sakaci ita kuwa ta yi? Ta yaya ma za ta iya aurensa bayan ta shigo gidan ne da niyyar ɗaukar fansa, ba kuma a kan kowa ba face shi? Ta aure shi ta ce ta auri me ke nan?
"Saboda yanzu ba na taka wa a kan ƙafata?" Ya jefa mata tambayar muryarsa a dake. Da sauri ta ɗaga idanunta ta kalle shi. Ya jinjina mata kai bayan ya ɗan saki wani murmushi ya ce
"Duk abin da kika yanke ki sanar da ni. Amma ki sani, idan ba ki amince ba, zan ɗauki hakan a matsayin saboda abin da ya sami ƙafata ne. Ko da yake, babu damuwa za ki iya tafiya." Ai tun kafin ya dire maganar ta soma barin wajen cike da sassarfa, haɗa hanya kawai take yi, kamar za ta kifa. A haka dai har ta ƙarasa ɗakinsu. Zubewa ta yi a kan gadon tana fashewa da wani kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Yau ɗin wata irin kewar Ameer ce ta dawo mata sabuwa, sai take ji tamkar yau ne Ameer ɗinta ya tafi ya bar ta. Sai take ji tamkar a yanzu ne suke magana ita da Ameer, maganar tasu da ta zamo ta ƙarshe. Ta cure cikin bargo waje ɗaya tana ci gaba da sheshsheƙar kuka cike da kewar Ameer da Innarsu. Ji take kamar ta watsar da komai ta koma ƙauyensu. Toh amma kuma ba ta da tabbacin idan ta koma ƙauyen ma za ta sami Innarsu, uwa uba kuma idan har ta bar gidan, ke nan hakan na nufin ruhin Ameer ya tafi a banza ke nan? Bayan ga shi tana da damar da za ta iya yin wani abu, wanda har zai kai su ga samun nasara. Wannan dalili, shi ne kaɗai abin da ya sa ta ji zuciyarta ta yi na'am da ci gaba da zaman ta cikin gidan, daga nan sai ta bazama ƙauyensu don biɗar Innarsu. Ta shafe fiye da awa ɗaya a wajen, kafin kamar wadda aka mintsina ta sakko daga kan gadon, kai tsaye toilet ta faɗa, ta rufe shi, sannan ta danna kiran Yohana. Jin tana neman katsewa kafin ya ɗaga ne ya sanya ta faɗin
"Ka ɗaga mana, ka ɗaga mana.." Daf da za ta tsinke ɗin kuwa ya ɗaga, ta sauke wata ƙatuwar ajiyar zuciya.
"Daneen." Ya ambata kamar yadda ya saba kullum saboda tsaro.
"Na'am." Ta ambata da muryarta da ta fara dashewa saboda kukan da ta sha.
"Oh my gosh! Me ya faru Cutie?" Ya faɗa cike da mamakin yadda ya ji muryarta ta sauya. Sai da ta ja wata ajiyar zuciyar kafin ba tare da ɓata lokaci ba ta shiga kora masa duk wasu abubuwa da suka faru.
"Puhahaha..." Ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya, wadda ta matuƙar ba wa Daneen mamaki, wanda har hakan sai da ya bayyana a kan fuskarta. Ya kai wajen minti ɗaya kafin ya ce hallau dai cikin gurɓatacciyar hausarsa.
"Buɗe kunnenki da kyau ki ji. Wannan wata dama ce muka samu. Sanar da shi kin amince da aurensa, da ma ba hanyar shiga ɗakinsa muke nema ba? Idan kika aure shi ai dole ki shiga ɗakinsa, ko ma in ce dole a kai ki ɗakinsa. Kin ga damar da muke so ta samu, a cikin kwana biyu za ki iya samar mana abin da muke buƙata, kin fahimta? Saboda haka kar ki damu, aure ne kawai da za ku yi na kwanaki ƙidayayyu, daga zarar kin samo mana abin da muke nema shi ke nan sai ki nemi takardar saki." Tun da ya fara magana take jin zuciyarta na wani irin harbawa kamar za ta fito daga ƙirjinta. Ita dai haka nan kawai take jin tsoro na shigar ta, duk da kamar yadda ya faɗa ɗin hakan shi ne mafitar su, toh amma ta yaya za ta yi aure ba tare da sanin Innarta ba?
"Kuma ko an ce za a je ƙauyenku don sanar da kishiyar kakarku kamar yadda kika faɗa wa Alhaji Dikko, ki san yadda za ki ki hana, saboda kar a kwaɓa mana aiki." Ta jiyo muryar Yohanan kamar ya san abin da take tunani. Ta sake yin shiru na tsawon wasu sakannin kafin ta buɗe baki da ƙyar ta ce
"Toh." Daga haka ta katse wayar, ta yi shiru tana sake nazarin abubuwan da ya faɗa. Tabbas idan dai har mafita suke so, toh abin da Yohana ya faɗa shi ne daidai. Sai dai kuma idan ta haƙura da ɗaukar fansar ne. Abin da kuma ba ta ji zuciyarta ta yi na'am da hakan ba. Ran ɗan'uwanta fa, Ran Ameer ɗinta fa. Ta runtse idanunta a hankali zuciyarta a cunkushe, wanda ta rasa dalilin hakan.
... "Sultanah ina yi miki magana kin yi shiru, wai ma ni sa'ar ki ce ne?" Maami ta faÉ—a a fusace tana kallon ta. Runtse idanunta Sultanah ta yi cikin rashin sanin abin yi, ta rasa me Maamin take nufi da ita. Ruwan da ke gaban ta Maami ta É—auka ta kai bakinta ko za ta daina jin zafin da take ji cikin zuciyarta.
"Maami ba zan iya auren wani idan ba Yah Abdoul ba. Ban taɓa faɗa miki ba ne, amma na daɗe da soyayyar Yah Abdoul danƙare a cikin zuciyata. Kuma maganar da nake miki yanzu ma haka mun yi nisa ni da shi, har ya ce ma nan da lokaci kaɗan zai sanar wa da Abbansa." Wata daƙiƙiyar ƙwarewa da Maami ta yi, ita ce ta sanya Sultanah tana kai ƙarshen maganar da ta ɗauko ta yi shiru. Ta miƙe da sauri tana faɗin
"Sannu Maami." Ta faɗa bayan ta zuba ruwa cikin tambulan ta miƙa mata. Hannu Maami ta saka ta karɓa kawai, sai dai maimakon ta sha ruwan sai ta ci gaba da tarin har zuwa lokacin da ya yi sauƙi ba tare da ta sha ruwan ba. Kallon ta kawai Sultanah take yi, tana fata ta kalle ta da idon rahama, ta kalle ta da idon tausayi irin na mahaifiya.
"Wanne Abdoul É—in kike nufi?" Wata irin ajiyar zuciya Sultanah ta sauke, tana jin daÉ—in tambayar Maamin. Ta yi murmushi kana ta ce
"Maami Yah Abdoul fa namu, Yah Abdoul na Yah Tareeq." Ajiye kofin hannunta Maami ta yi, duk wani tashin hankali ya gama bayyana a kan fuskarta. Sai dai cikin dakiya ta ce, duk da yadda harshenta ke ƙoƙarin bijire mata wajen yin maganar, amma haka ta daure, ta cije ta yi iya bakin ƙoƙarinta.
"Na riga na zaɓa miki miji Sultanah." Shi ne kawai abin da ta iya faɗa. A take idanun Sultanah suka tara ƙwalla, ban da bugawa babu abin da zuciyarta ke yi. Cikin tashin hankali ta ce
"Maami ki yi mini afuwa. Ina son Yah Abdoul, wallahi ina son shi matuƙa, zuciyata za ta iya bugawa idan ban same shi ba. Maami taɓa ki ji yadda zuciyata ke harbawa, ban san halin da zan tsinci kaina ciki ba idan maganar da kike faɗa ta zama gaskiya. Maami Abdoul fa abokin Yah Tareeq, ɗan gidan aminin Abeey, kuma ɗan gidan amiyarki. Ki yi mini wannan alfarmar don girman Allah Maami." Ta ƙare maganar tana fashewa da sabon kuka. Kukan da ke fitowa tun daga ƙasan zuciyarta, wadda ke mata wani irin zafi, zafin da rabon da ta ji shi tun kafin Abdoul ya zo mata da tayin soyayyarsa. Ta daɗe rabon da ta ji shi, har ta fara sabawa da farin ciki, sai ga shi rana ɗaya, Maami na neman tarwatsa mata wannan farin cikin. Don kuwa ta san raba ta da Abdoul babban abu ne, wanda ba ta sani ba ko zuciyarta na da ƙarfin ɗauka. Ganin da ta yi Maami ta yi mata shiru ne ya sanya jikinta ya ƙara yin sanyi. Ta girgiza kanta tana jin yadda lokaci guda ya yi mata wani gingirin.
"Maamina ki ce wani abu mana don Allah." Ta faɗa cikin kuka. Sai bayan shuɗewar wasu sakanni masu yawa, sannan Maami ta miƙe, cikin ƙarfin hali ta ce
"Gwara ma ki cire ranki, don wallahi ba za ki auri Abdoul ba. Ke kika ce za ki ɗaga mini hankali wallahi sai na tsine miki a banza. Ki kama kanki, idan ba haka ba ran kowa ya ɓaci. Idan na ce kowa ina nufin kowa." Ta dakata a nan sannan ta ci gaba da faɗin