Sashe 26
Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allah Ya tsare." Ta sake maimaitawa tana bin sa da kallo har ya bar wajen a sanyaye. Sai da ya ɓace mata da gani sannan ta dena kallon sa, gaba ɗaya wani burinta ya tafi kan yadda za su yi maza su koma wajen Innarsu. Ba za ta sake barin ɗan'uwanta ya din ga aikin wahala ba. Tana fata ta yi kuɗi a rayuwarta, Ameer ya ji daɗi. Haka zalika Innarsu ma ta ji daɗi. Gaba ɗayansu su dena aikin wahala. Zama ta ci gaba da yi a wajen, ta yi shiru tamkar mai tunani. Sai dai zuwa can idan ta gaji sai ta ɗaga kai ta kalli abin da ke faruwa a gefenta sai kuma ta maida fuskarta kan cinyarta. A nan ta yi sallah, ko bi ta kan wani abinci ba ta yi ba, ta ci gaba da jiran Ameer. Zuwa can kuwa sai ga shi ya dawo. Ya wanzar da murmushi a kan fuskarsa da ta sauya daga da, wadda take koyaushe cikin matuƙar annushuwa, zuwa wata daban. Sai dai duk iya ƙoƙarinsa yake don kar Addar tasa ta fahimci wani abin. Duk da ya san hakan ma ba mai yiwuwa ba ne. Sai dai inda Allah Ya taimake shi, yadda damuwar da ke shimfiɗe a kan fuskarsa ta ta'allaƙa ta da gajiyar aiki kamar yadda ya sanar da ita. Ko minti 2 ba su ƙara ba, suka yi gaba zuwa wajen da suke zama, suka kuma saba. A nan suka ci abinci sannan suka ci gaba da zama.
A 'yan kwanakin da suka biyo baya, sosai al'amuran Ameer ke ci gaba da sauyawa, ba shi da aiki sai tunani da kuma damuwa. Har ta kai yanzu ba ma ya iya ɓoye damuwar a gaban Daneen ɗin saboda yadda ya gajiya. Duk wani ƙwarin gwuiwarsa ya ƙare. Ji yake kamar ƙwaƙwalwarsa za ta yi bindiga idan ya cika tunani.
Dare ne, domin kuwa wajen ƙarfe 10pm ne. Daga shi har ita babu wanda ya soma ƙoƙarin neman wajen kwanciya. Ita ta yi shiru ne kawai tana kallon sa, mamaki take yadda take ganin shimfiɗaɗɗiyar damuwa a kan fuskarsa amma ya ƙi faɗa mata. Bayan hakan ba halinsa ba ne. Ta rasa gane abin da ke damun Ameer ɗin, wanda ya sauya shi cikin kwanaki kaɗan haka. Ta rasa yadda za ta yi, don haka kawai sai ta zuba masa idanu ta ji ko zai sanar da ita damuwarsa. Sai dai abin da ma ta lura da shi, tamkar hakan ƙara ba shi lasisin yin tunani ne ta yi. Don kuwa kwantar da kansa ya yi jikin wani gini da ke gefensa ya yi shiru. Daga inda take zaune take ci gaba da kallon sa, tunani barkatai cikin ƙwaƙwalwarta. Ba tun yanzu ba take hango shi yana gyara zamansa, daga baya ma sai ya tashi daga inda yake ya sauya waje. A hankali ta miƙe jin da ta yi gabanta ya ɗan faɗi, kai tsaye ta ƙarasa inda yake.
"Ameer." Ta faÉ—a bayan ta dafa hannunta a kan kafaÉ—arsa. ÆŠaga jajayen idanunsa ya yi ya kalle ta hannunsa dafe da cikinsa. Ta bi hannun nasa da kallo ba tare da ta lura da idanunsa ba ta ce
"Me yake damun ka Ameer?" Ta faÉ—a a É—an gigice da muryarta da ke rawa. Girgiza kai ya yi kafin ya ce
"Adda cikina ke ciwo."
"Cikinka kuma?" Ta faɗa tana riƙo hannun nasa. Jinjina kai ya yi yana sake dafe cikinsa. Cikin matuƙar ruɗewa da rashin sanin abin yi Daneen ta ce
"Me ka ci Ameer? Me ya sami cikin naka?"
"Babu abin da na ci fa." Ya faɗa har lokacin hannunsa a kan cikinsa. Da sauri ta shiga girgiza kai, daidai lokacin da idanunta suka cika taff da ƙwalla ta soma faɗin
"Me ya sa kake mini haka ne Ameer? Me na maka? Me ya sa kake ta ɓoye mini abubuwa da dama? Me ya sa ka tsiro da wasu halaye bayan da ba haka kake ba? Idan wani abu ya same ka me zan faɗa wa Inna? Ba za ka buɗe baki ka yi mini magana ba Ameer?" Ta ƙare maganar lokacin da wasu kyawawan hawaye suka sauka a kan kuncinta. Abin da ya matuƙar ba wa Daneen mamaki shi ne yadda Ameer ya fashe da kuka, kuka kuma ba irin na wasa ba, kuka sosai tamkar wanda ake duka ko ake yi wa wani mummunan abu. Maimakon ta ɗan ji sassauci, sai kukan nasa ya sake dugunzuma mata hankali, cikin rawar murya ta ce
"Na shiga uku Ameer, faɗa mini abin da ya faru? Cikin ne?" Ta tambaya a ruɗe tana sake riƙo hannun da ke riƙe da cikinsa.
"Ki yi haƙuri Addatah, ki yi haƙuri kin ji?" Shi ne abin da ya faɗa har lokacin yana kuka tamkar mace. Cikin ƙanƙanin lokaci jikinta ya ɗauki rawa, muryarta da ta shige ta yi ƙoƙarin janyo ta wajen faɗin
"Sanar da ni abin da ke faruwa Ameer, na shiga uku." Ta faɗa tana jin yadda wani bala'in tashin hankali ke ci gaba da rikito mata. Sai da ya sake girgiza kai, idanunsa da suke a lumshe ya buɗe, ya ɗora su a kan Daneen, ya sauke hannunsa da ke kan cikinsa, duk da yadda yake jin cikin nasa tamkar ba a jikinsa yake ba, amma ya yi ƙarfin halin kamo hannayenta duka biyun. Muryarsa har wani sarƙewa take yi lokacin da ya soma faɗin
"Adda ki yi haƙuri, na rasa yadda zan yi, ban san ya zan yi na raba kaina da mutanen nan ba, ban san tsautsayin da ya haɗa ni da su ba. Ban san abin da ke damun ƙwaƙwalwata ba. Ni dai kawai na ji ba na son rabuwa da su, ko da zan yi ƙoƙarin hakan ma ba zan iya ba. Adda maza ne su ba mutum ɗaya ba ba biyu ba, kullum sai sun yi amfani da ni Adda. Ba su taɓa ce mini kar na sanar wa da kowa ba, amma tamkar an rufe bakina na kasa faɗa miki, na kuma kasa hana kai kaina inda suke. Na kasa barin ki ki san inda nake zuwa Adda, ina tsoron kar ki hana ni zuwa kuma in ƙi hanuwa. Don ji nake yanzu haka in da zan wayi gari cikin ƙoshin lafiya toh zan koma wajen nasu. Kullum cikin kuka nake Adda cikin dare. Na rasa yadda zan yi, na rasa mene ne mafita. Na rasa abin da ke mini daɗi. Ina jin tamkar ƙwaƙwalwata ba ta jikina, ina ji tamkar wani noti da ke kaina ya kwance. Adda na rasa abin da ke mini daɗi. Ni da kaina fa nake kai kaina wajen su, me yake damu na? Anya kuwa ni ɗin ne? Ya zan yi ne ni kam? Na rasa abin da ke mini daɗi. Na rasa ya zan yi, don Allah Adda ki yi haƙuri ki sanar da ni abin da zan yi, ki yi haƙuri kar ki ɗauki matakin da ba zan iya jurewa ba. Zuciyata zafi take mini, ina ji ina numfashi da ƙyar. Ki yafe mini Adda." Ya ƙare maganar yana sake fashewa da wani marayan kuka. A hankali ta shiga zame hannunta daga cikin na Ameer, idanunta da suka ƙafe ƙaff, babu hawaye ko ɗigo a kan fuskarsa. Kallon sa kawai take yi tamkar wadda ta soma ganinsa a yau ɗin nan. Wani irin gudu zuciyarta take, wanda ya mugun wuce ƙa'ida. Don kuwa idan da za ka kalli ƙirjinta a lokacin, za ka iya ganin yadda zuciyarta ke bugawa a haukace. Kallon sa kawai take yi, shin da gaske abin da take ji daga bakin Ameer gaskiya ne yake faɗa mata? Ameer Ameer dai nata shi ne yake faɗin wasu maza suna amfani da shi? Idan dai har ta fahimci abin da yake nufi kenan wasu sun yi lalata da shi? 'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un' Ta ambata a fili muryarta na wani irin karkarwa tamkar yadda jikinta ke wani mahaukacin ɓari tamkar wadda ke shirin zube wa a ƙasa. Dalili kenan da ya sanya Ameer ya ɗaga idanunsa da suka yi jajur, har sun yi wani luhu-luhu ya kalle ta, ita ma shi take kalla. Ya girgiza mata kai kafin cikin sanyi ya furta
"Ba laifina ba ne Adda." Maganar da ya yi, ita ce ta ba wa kukan da ya maƙale mata damar fitowa, ta shiga rera shi kamar za ta shiɗe. Zube wa ta yi a kan ƙafafunta ta shiga rera shi kamar ranta zai fita. Ita kam wannan wace kalar baƙar rana ce a wajenta? Wace kalar mummunar rana ce wannan? Wanne kalar bala'i ne wannan ya shigo cikin rayuwarsu ita da ɗan'uwanta? 'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un' Ta sake maimaitawa, daidai lokacin da Ameer ya ƙaraso inda take zaune ya zube shi ma a kan ƙafafunsa. A karo na barkatai ya sake furta
"Ki yi haƙuri Addatah, ban san yadda aka yi hakan ta faru ba. Kin fi kowa sanin halin ɗan'uwanki." Maganarsa da ke fita a wani hahharɗe ta daki dodon kunnenta. Sai a lokacin sannan ta samu ƙwarin gwuiwar soma magana.
"Me ya sa za ka mana haka Ameer? Me ya sa ba ka bari mun mutu da yunwa da rashin gata ba, a kan wannan abin. Iyee Ameer? Ba gwara mu mutu ba, da ka jefa kanka cikin wannan ɗabi'ar. Ameer me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ka canja daga Ameer ɗina da na sani? Me ya sa haka Ameer?" Ta ƙare hannunta a kan kwalar rigarsa tana ja kamar za ta cire rigar. Tun daga ƙasan zuciyarta maganar take fitowa, muryarta cikin kuka tamkar ba za ta iya ƙarasa maganar ba. Yanzu kam kukan Ameer babu sauti, sai hawayen da ke ta tsere a kan kuncinsa.
A 'yan kwanakin da suka biyo baya, sosai al'amuran Ameer ke ci gaba da sauyawa, ba shi da aiki sai tunani da kuma damuwa. Har ta kai yanzu ba ma ya iya ɓoye damuwar a gaban Daneen ɗin saboda yadda ya gajiya. Duk wani ƙwarin gwuiwarsa ya ƙare. Ji yake kamar ƙwaƙwalwarsa za ta yi bindiga idan ya cika tunani.
Dare ne, domin kuwa wajen ƙarfe 10pm ne. Daga shi har ita babu wanda ya soma ƙoƙarin neman wajen kwanciya. Ita ta yi shiru ne kawai tana kallon sa, mamaki take yadda take ganin shimfiɗaɗɗiyar damuwa a kan fuskarsa amma ya ƙi faɗa mata. Bayan hakan ba halinsa ba ne. Ta rasa gane abin da ke damun Ameer ɗin, wanda ya sauya shi cikin kwanaki kaɗan haka. Ta rasa yadda za ta yi, don haka kawai sai ta zuba masa idanu ta ji ko zai sanar da ita damuwarsa. Sai dai abin da ma ta lura da shi, tamkar hakan ƙara ba shi lasisin yin tunani ne ta yi. Don kuwa kwantar da kansa ya yi jikin wani gini da ke gefensa ya yi shiru. Daga inda take zaune take ci gaba da kallon sa, tunani barkatai cikin ƙwaƙwalwarta. Ba tun yanzu ba take hango shi yana gyara zamansa, daga baya ma sai ya tashi daga inda yake ya sauya waje. A hankali ta miƙe jin da ta yi gabanta ya ɗan faɗi, kai tsaye ta ƙarasa inda yake.
"Ameer." Ta faÉ—a bayan ta dafa hannunta a kan kafaÉ—arsa. ÆŠaga jajayen idanunsa ya yi ya kalle ta hannunsa dafe da cikinsa. Ta bi hannun nasa da kallo ba tare da ta lura da idanunsa ba ta ce
"Me yake damun ka Ameer?" Ta faÉ—a a É—an gigice da muryarta da ke rawa. Girgiza kai ya yi kafin ya ce
"Adda cikina ke ciwo."
"Cikinka kuma?" Ta faɗa tana riƙo hannun nasa. Jinjina kai ya yi yana sake dafe cikinsa. Cikin matuƙar ruɗewa da rashin sanin abin yi Daneen ta ce
"Me ka ci Ameer? Me ya sami cikin naka?"
"Babu abin da na ci fa." Ya faɗa har lokacin hannunsa a kan cikinsa. Da sauri ta shiga girgiza kai, daidai lokacin da idanunta suka cika taff da ƙwalla ta soma faɗin
"Me ya sa kake mini haka ne Ameer? Me na maka? Me ya sa kake ta ɓoye mini abubuwa da dama? Me ya sa ka tsiro da wasu halaye bayan da ba haka kake ba? Idan wani abu ya same ka me zan faɗa wa Inna? Ba za ka buɗe baki ka yi mini magana ba Ameer?" Ta ƙare maganar lokacin da wasu kyawawan hawaye suka sauka a kan kuncinta. Abin da ya matuƙar ba wa Daneen mamaki shi ne yadda Ameer ya fashe da kuka, kuka kuma ba irin na wasa ba, kuka sosai tamkar wanda ake duka ko ake yi wa wani mummunan abu. Maimakon ta ɗan ji sassauci, sai kukan nasa ya sake dugunzuma mata hankali, cikin rawar murya ta ce
"Na shiga uku Ameer, faɗa mini abin da ya faru? Cikin ne?" Ta tambaya a ruɗe tana sake riƙo hannun da ke riƙe da cikinsa.
"Ki yi haƙuri Addatah, ki yi haƙuri kin ji?" Shi ne abin da ya faɗa har lokacin yana kuka tamkar mace. Cikin ƙanƙanin lokaci jikinta ya ɗauki rawa, muryarta da ta shige ta yi ƙoƙarin janyo ta wajen faɗin
"Sanar da ni abin da ke faruwa Ameer, na shiga uku." Ta faɗa tana jin yadda wani bala'in tashin hankali ke ci gaba da rikito mata. Sai da ya sake girgiza kai, idanunsa da suke a lumshe ya buɗe, ya ɗora su a kan Daneen, ya sauke hannunsa da ke kan cikinsa, duk da yadda yake jin cikin nasa tamkar ba a jikinsa yake ba, amma ya yi ƙarfin halin kamo hannayenta duka biyun. Muryarsa har wani sarƙewa take yi lokacin da ya soma faɗin
"Adda ki yi haƙuri, na rasa yadda zan yi, ban san ya zan yi na raba kaina da mutanen nan ba, ban san tsautsayin da ya haɗa ni da su ba. Ban san abin da ke damun ƙwaƙwalwata ba. Ni dai kawai na ji ba na son rabuwa da su, ko da zan yi ƙoƙarin hakan ma ba zan iya ba. Adda maza ne su ba mutum ɗaya ba ba biyu ba, kullum sai sun yi amfani da ni Adda. Ba su taɓa ce mini kar na sanar wa da kowa ba, amma tamkar an rufe bakina na kasa faɗa miki, na kuma kasa hana kai kaina inda suke. Na kasa barin ki ki san inda nake zuwa Adda, ina tsoron kar ki hana ni zuwa kuma in ƙi hanuwa. Don ji nake yanzu haka in da zan wayi gari cikin ƙoshin lafiya toh zan koma wajen nasu. Kullum cikin kuka nake Adda cikin dare. Na rasa yadda zan yi, na rasa mene ne mafita. Na rasa abin da ke mini daɗi. Ina jin tamkar ƙwaƙwalwata ba ta jikina, ina ji tamkar wani noti da ke kaina ya kwance. Adda na rasa abin da ke mini daɗi. Ni da kaina fa nake kai kaina wajen su, me yake damu na? Anya kuwa ni ɗin ne? Ya zan yi ne ni kam? Na rasa abin da ke mini daɗi. Na rasa ya zan yi, don Allah Adda ki yi haƙuri ki sanar da ni abin da zan yi, ki yi haƙuri kar ki ɗauki matakin da ba zan iya jurewa ba. Zuciyata zafi take mini, ina ji ina numfashi da ƙyar. Ki yafe mini Adda." Ya ƙare maganar yana sake fashewa da wani marayan kuka. A hankali ta shiga zame hannunta daga cikin na Ameer, idanunta da suka ƙafe ƙaff, babu hawaye ko ɗigo a kan fuskarsa. Kallon sa kawai take yi tamkar wadda ta soma ganinsa a yau ɗin nan. Wani irin gudu zuciyarta take, wanda ya mugun wuce ƙa'ida. Don kuwa idan da za ka kalli ƙirjinta a lokacin, za ka iya ganin yadda zuciyarta ke bugawa a haukace. Kallon sa kawai take yi, shin da gaske abin da take ji daga bakin Ameer gaskiya ne yake faɗa mata? Ameer Ameer dai nata shi ne yake faɗin wasu maza suna amfani da shi? Idan dai har ta fahimci abin da yake nufi kenan wasu sun yi lalata da shi? 'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un' Ta ambata a fili muryarta na wani irin karkarwa tamkar yadda jikinta ke wani mahaukacin ɓari tamkar wadda ke shirin zube wa a ƙasa. Dalili kenan da ya sanya Ameer ya ɗaga idanunsa da suka yi jajur, har sun yi wani luhu-luhu ya kalle ta, ita ma shi take kalla. Ya girgiza mata kai kafin cikin sanyi ya furta
"Ba laifina ba ne Adda." Maganar da ya yi, ita ce ta ba wa kukan da ya maƙale mata damar fitowa, ta shiga rera shi kamar za ta shiɗe. Zube wa ta yi a kan ƙafafunta ta shiga rera shi kamar ranta zai fita. Ita kam wannan wace kalar baƙar rana ce a wajenta? Wace kalar mummunar rana ce wannan? Wanne kalar bala'i ne wannan ya shigo cikin rayuwarsu ita da ɗan'uwanta? 'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un' Ta sake maimaitawa, daidai lokacin da Ameer ya ƙaraso inda take zaune ya zube shi ma a kan ƙafafunsa. A karo na barkatai ya sake furta
"Ki yi haƙuri Addatah, ban san yadda aka yi hakan ta faru ba. Kin fi kowa sanin halin ɗan'uwanki." Maganarsa da ke fita a wani hahharɗe ta daki dodon kunnenta. Sai a lokacin sannan ta samu ƙwarin gwuiwar soma magana.
"Me ya sa za ka mana haka Ameer? Me ya sa ba ka bari mun mutu da yunwa da rashin gata ba, a kan wannan abin. Iyee Ameer? Ba gwara mu mutu ba, da ka jefa kanka cikin wannan ɗabi'ar. Ameer me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ka canja daga Ameer ɗina da na sani? Me ya sa haka Ameer?" Ta ƙare hannunta a kan kwalar rigarsa tana ja kamar za ta cire rigar. Tun daga ƙasan zuciyarta maganar take fitowa, muryarta cikin kuka tamkar ba za ta iya ƙarasa maganar ba. Yanzu kam kukan Ameer babu sauti, sai hawayen da ke ta tsere a kan kuncinsa.