← Book details Daneen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 49

Sashe 1

Daneen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*♡☆DANEEN☆♡*

Zahra Yusuf (Mhiz Innocent)

Mikiya Writers Ass..

Book 1
Pg 01

بسم الله الرحمن الرحيم.

__ Sassanyar iska ke tashi, wadda ke haɗuwa da ƙamshin jar jiƙaƙƙiyar ƙasar da ke malale a tsakar gidan. Hakan ne ya sa iskar da ke shiga hancin duk mahalukin da ya shaƙe ta, ta kasance daddaɗa. Ruwa ne kwance a wani gefe na tsakar gidan, ya yin da wani wajen ƙasar ce kawai a jiƙe. Wanda hakan ze alamta maka cewa ba a daɗe da ida ruwan sama ba. Tana zaune a kan kujera 'yar tsuguno, gaban murhu da tukunya ke ɗore a kai tana fifita wutar da ke ƙoƙarin mutuwa. Sautin sauke numfashin da ta soma jiyowa daga cikin ɗaya daga cikin ɗakunan da ke gidan ne ya sanya ta dakatawa daga fifita wutar da take. Ta sake ƙanƙance idanunta da suka ɗan sauya kala saboda yajin da ke shiga cikin idanunta, na icen da ke ci cikin wuta.

"Wayyo Allah! Wayyo.." Ta sake jiyo sautin a wahalce. Ba ta san lokacin da ta jefar da mificin hannunta ba, ta miƙe da sauri har tana ƙoƙarin tuntuɓe, ba ta tsaya ba ta yi gaba kai tsaye zuwa cikin ɗakin. Hannu ta saka ta yaye yalolon labulen da ya hana ta ganin abin da ke faruwa cikin ɗakin, har sai da ta shiga. Ta sauke idanunta a kan motsatstsiyar katifar da ke cikin ɗakin. Matashiyar budurwa ce zaune a kan katifar tana sauke numfashi a wahale, hannunta ɗaya dafe da turtsetsen cikin da ke gabanta, ya yin da ta yi amfani da ɗayan hannunta wajen damƙe gefen katifar da wani irin ƙarfi da ba ta san tana da shi ba. Idanunta a rufe suke gam tana jujjuya kanta cikin tsananin azabar naƙuda. Jin alamar an shigo cikin ɗakin ne ya sanya ta buɗe jajayen idanunta ta yi ƙarfin halin kallon matar da ta shigo. Cikin raunanniyar murya ta ce

"Dada marata, Dada zan mutu.." Ta ƙare maganar tana yarfe hannunta da ta ɗauke daga kan cikinta. Duk da ba ta da tabbacin ko Dadar za ta taimaka mata, ko za ta bar ta ne ba tare da ta yi yunƙurin taimaka mata ba. Murmushi wadda aka kira da Dadar ta yi tana faɗin

"Alhamdulillah!" Ta ƙare maganar tana maida idanunta kan Inna-wuro. A ranta tana ji kamar ta taka rawa don tsananin murna. Cikin ƙarfin hali tare da danne duk wani abu da take ji tace

"Sannu Inna-wuro." Ta faɗa tana ƙarasawa kan katifar. Duk da tsananin azabar da Inna-wuro ke ji hakan be hana ta kallan Dadar ba, ta lumshe idanunta tana jin wata ƙwalla na tarar mata a cikin idanunta. Duk wani ƙoƙari da za ta iya dan ganin Inna-wuron ta haihu lafiya Dadar ta din ga yi. Kasancewarta Ungozoma ya sa ba ta nemi wani taimako ba, ko yunƙurin kiran wani dan a kai ta asibiti ba. Ita dai burin ta kawai Inna-wuro ta haihu lafiya, ko da abin da ke cikinta be fito lafiya ba wannan ba damuwarta ba ce. An kwashe wajen minti 30 kafin wani dattijon bafulatanin mutum ya shigo cikin gidan da sallama ɗauke a bakinsa. Dada ba ta iya amsawa ba saboda cigaba da taimakawa Inna-wuro da take.

"Kina ina ne Uwar gida." Ya faɗa yana zame hular kansa. Shirun da ya ji ya sanya shi ƙarasowa cikin gidan, yana dab da ƙarasawa Dada ta fito. Ya kalle ta sosai yana nazarin yanayinta. Tun kafin yace komai ta ce

"Naƙuda ce ta tasowa Inna-wuro." Zaro idanunsa ya yi, da sauri ya kai hannunsa yana lalubar aljihunsa.

"Bari na kira..."

"Ka kira wa?" Ta katse shi da faɗin hakan bayan ta tattaro girar sama da ƙasa ta haɗe waje ɗaya. Dakatawa ya yi daga ƙoƙarin lalubo wayarsa da yake, cikin 'yar rikicewa ya ce

"A'ah.. wai da a kira shi a sanar da shi ta soma naƙuda." Numfashi Dada ta sauke har lokacin ba ta saki fuskarta ba, ta ce

"Toh ga ka ga wayar nan ai sai ka kira." Daga haka ta juya ta koma cikin ɗakin. Fahimtar gatse take masa ya sanya shi bin ta da kallo kawai ba tare da ya sake yunƙurin taɓa aljihunsa ba. Daidai lokacin da ta saka ƙafarta cikin ɗakin, ya yi daidai da lokacin da kukan jariri ya cika cikin ɗakin. Da sauri ta ƙarasa, cikin mamakin yadda haihuwar ta zo wa Inna-wuron a sauƙaƙe duk da kasancewa ta fari ce. Kukan jaririn da take ji be sanya ta kula inda yake ba. Sai ƙarasawa da ta yi cikin tashin hankalin da ya rufto mata lokaci guda. Ta sanya hannu ta riƙo Inna-wuro da tun da babyn ya fito ta zube a wajen ba ta sake motsawa ba. Idanunta da ke motsawa a wahalce ne ya sanya Dada sakin ajiyar zuciya. Sai a lokacin sannan ta miƙe ta saka hannu ta ɗauki babyn da ke ta rusa kuka. Ta sanya shi cikin zani ta ajje gefe. Farawa ta yi da gyara Inna-wuro, cike da kulawa kamar wani ƙwai haka take kula da ita. Abin da ya saka Inna-wuro sakin baki tana kallanta cike da maɗaukakin mamaki. Sai dai ba ta ce komai ba, ta cigaba da bin komai da ido.

.. "Zan iya sanar da shi abin da aka samu?" Baffa da ke zaune a kan kujera ya faÉ—a yana kallan Dada da ta fito daga cikin É—akin.

"Hohoho.. Wai ni kam Malam me ye damuwarka da wannan haihuwar ne? Yoh har wani ma abin alfahari ne a wajenmu da yarinyar nan ta haifi mace? Ka dai san a kan yarjejeniyar da aka rabu, saboda haka don Allah ka dena mini maganar nan. Ka bar ni in ji da abin da nake ji."

Lumshe idanunta ta yi lokacin da kunnuwanta suka gama jiyo mata maganganun Dada. A hankali ta kai kyawawan fararen idanunta kan babyn da ke kwance cikin zani tana bacci. Hannunta ta kai ta ɗauke ta, ta ɗan gyara zamanta tana runtse idanunta. Murmushi ne ya suɓuce mata a kan fuska lokacin da idanunta suka sauka a kan kyakkyawar farar fuskar jinjirar da ke bacci cikin kwanciyar hankali, tana sauke numfashi a hankali. Kafe ta ta yi da idanunta tana jin wata irin ƙaunar ta na ratsa duk wata gaɓa ta jikinta. Sai dai cikin ƙanƙanin lokaci idanunta suka fara juyewa zuwa ja. Ƙalubalen da ke cikin rayuwarsu shi ya soma faɗo mata. Shin ko ita ɗin mahaifinta ze yi farin ciki da zuwanta duniya? Shin mahaifinta ze karɓe ta kamar yadda kowanne uba ke karɓar ɗan da ya haifa? Shin akwai mutanen da ke farin ciki da zuwan wannan halitta duniya ko kuwa ita kaɗai da ta haife ta ita ke farin ciki da zuwan ta? Sabuwar ƙwallar da ta tarar mata a idanu ita ce ta sanya ta lumshe idanunta, tana jan kyakykyawar babyn ta rungume a ƙirjinta. Wani irin sanyi na ratsa ta. Soyayyar ɗiyarta na shigar ta.

Kwana 5 da haihuwar jikinta ya soma komawa daidai. Ta ji daÉ—in jikinta ainun. Babynta ma da yake tana samun isasshen abinci ya sanya ta yi kyau abin ta. Duk a tsawon kwanakin nan ta É—auka za ta ji Dada ko Baffa wani ya ce mata Alhaji Baita ya kira ta a waya dan jin lafiyarta. Sai dai har aka shafe kwanaki ba ta ji daga gare shi ba, duk da dai ta san da ma hakan kan iya faruwa.

... "Ya ce a ɗauki kuɗin rago cikin kuɗaɗen da yake turowa, sannan ya kuma ba ki wuƙa da nama a kan zaɓar wa 'yarki suna. Ba shi da matsala da hakan, saboda haka wane suna za a raɗa mata?" Baffa ya faɗa yana kallan Inna-wuro. Wani irin yawu me ɗaci ta haɗiye, karyayyiyar zuciyarta na sake karyewa. Tausayin rayuwar ɗiyarta na sake kama ta. Kenan har rashin muhimmancinta, da kuma son nuna be damu da abin da ta haifa ba ya kai ya kasa sakawa 'yarsa suna? 'yar da ya haifa da cikinsa? Ta ja wani numfashi da ƙyar kafin ta ce

"Baffa ka saka mata duk sunan da ya maka." Ta faɗa cikin ƙarfin hali, tana jira ta ji amsar da za ta fito daga bakin Baffan. Kamar yadda ta tsammata kuwa sai cewa ya yi

"A'ah, kin ga ni fa cewa na yi ki faɗi sunan da za a sanya wa yarinya. Me ye garin gamina da ita kuma? Ubanta ma be saka mata suna ba sai ni karan kaɗa miya?" Ya ƙare yana nuna kansa. Daidai lokacin da Dada ta fito daga cikin ɗakinta tana kallan su. Ta taɓe baki kafin ta wuce banɗaki. Dalili kenan da ya sa ba ta son cika magana da Baffan nata, don abubuwa da dama kan zo cikin ƙwaƙwalwarta, tana sake ji duniyar na mata zafi, komai yana sake juye mata saboda halin da Baffan ke nuna mata. Baffan nata da be daɗe da sauyawa ba.

"DANEEN, Allah Ya raya ta da imani." Ta faɗi abin da daga shi har Dadan suka kasa faɗa tun da ta haihu. Tana gama faɗa ta miƙe.

"Ameen." Baffa ya faɗa. Ita kuma Inna-wuro ta wuce cikin ɗaki. Daidai lokacin da babyn ta soma kuka, ta ƙarasa da sauri tana sakin murmushi ta ɗauke ta. Ta yi amfani da hannunta ɗaya wajen ɗauke ƙwallar da ta sakko mata a kan fuska.

"Ya isa haka Shalele." Ta faɗa tana ƙarasawa ta zauna, ta shiga shayar da yarinyar tana kallan kyakykyawar fuskarta da kullum kyawunta sake fitowa yake yi. A duk lokacin da za ta kalli fuskarta sai ta tuna abubuwa da dama, abubuwan da suka faru a baya, da ma waɗanda take hasaso tabbas za su faru nan gaba, idan dai ba Allah ne Ya taƙaita ba.

A ranar aka yanka rago aka kuma sanya wa yarinya suna DANEEN. Haka Inna-wuro ta cigaba da kula da ɗiyarta cikin kulawa, so da kuma ƙauna. Ta gefe guda kuma Dada na sanya ido a kan duk wani motsinta, sai dai ga mamakinta ba ta taɓa damuwa da ya Daneen ta tashi ba, ya ta kwana, kullum burinta ta san lafiyar Inna-wuron. Dalili kenan da ya sa ta maida hankali sosai wajen kula da 'yarta, tun da dai ita kaɗai ce ke son rayuwa da kuma lafiyarta.
Chapter 1 · 0% Book details