Sashe 57
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbu ya rarrafo akan guiwowinsa yazo gaban Hajjatiye ya daura kansa akan cinyarta murya a sanyaye with full of regret ya soma magana.
"Ina me baki hakuri a madadin Huraira,naji takaicin wai yau matata ce ta tsaya tana yiwa mahaifiyata rashin kunya,dan Allah ki yafe min,in sha Allah se na dau mataki akan abinda ta aikata yau din nan".
Shafa kansa Hajjatiye ta yi ta ce "ban amince ka ce zaka dau mataki akanta ba,ni a wajena komai ya riga da ya wuce,ka dena damun kanka".
Murmushi Hajiya babba ta yi wannan dalilin ne suke sa'ke son surkar tasu,ko min irin masifar da zaka ga tana yi tofa bazata yarda wani abun ya ruguza ahalinta ba,wanda be san ta bane kawai zece tana da faɗa.
Magana sukayi sosai kafin Hajjatiye da Hajiya babba suka haura upstairs jin an kira sallah.
Su kuma suna jiran su LTG su fito su tafi masallaci.
A part din Ammuh kuwa,ummah se faman Safa da marwa takeyi tunda suka shigo ta kasa tsaye ta kuma kasa zaune.
Ita kan ta Ammuh lamarin ya girgiza ta,
"Hajiya Huraira dan Allah ki nutsu mu san mafita, wannan Safa da marwa da kike yi babu inda ze kai mu".
Zama ummah ta yi"kamar ni Isma'il ze tozarta a gaban yara da kuma kishiyoyin balbali na?".
"Calm down first wannan fa ba wani babban matsala ba ce amma duk kin bi kin tayarwa da kanki hankali,ko kin manta abinda zamu iya aikatawa ne".
"Hajiya khareema ina sane amma dole raina ya ɓaci kishiya fa?,tun da be min kishiya ba se yanzu da na girma ga yara na sun gama girma shine ze min kishiya".
Matsowa kusa da ita Ammuh ta yi dan ta lura har yanzu Ummah bata dawo dede ba.
"Ki shirya ranar Lahadi muje wajen boka mauzau,daga auren shi Abbu din harna Saghar din se mun watsar dashi".
Se sannan ne taji hankalinta ya kwanta ruwa me sanyi ta bata tasha.
Bayan sallar isha uncle Hameed ya dawo kai tsaye part dinsu ya nufa.
Tsaye a jikin window ya iske Anty amarya, kallo ɗaya ta mishi ta kauda idonta,tunda yaga haka yasan cewa akwai wani abinda ya faru ga idonta da ya kumbura tasha kukanta hatta koshi.
Wajen ta yi nufa.
"Amaryata me yake faruwa na ganki haka"murya na rawa ta sanar masa da duk abubuwan da suka faru bayan tafiyarsa,kafin ya shigo din nan Hajiya babba da Ammi suka fita a part dinta bayan sun gama rarrashinta.
Jawota jikinsa ya yi yana bata hakuri shi kanshi be ji daɗin abinda ya faru ba, yasan Abbie baze taɓa yanke wannan hukuncin ba,batare da kwakkwaran dalili ba.
"Kiyi hakuri in sha Allah a wannan karon bazamu rasa yarmu ta biyu ba Sabriyah, Allah yana sane da mu,kuma ya Mubarak nasan akwai dalilin da yasa ya yanke wannan hukuncin ".
Ba ta ce mishi komai ba.
8:00pm dede lokacin cin abinci as usual ummah da Ammuh basu fito ba,haka LTG shima yana part din sa, uncle Hameed ya yi iya yin sa amma Anty amarya taki fitowa itama.
A bangaren su Umaisha ma dakyar suka sha kansu Sabriyah suka je dinning.
Kowa ka gani fuskar sa babu walwala da annuri,kawai de ana cin abincin ne,bawai dan yana shiga yanda ya kamata ba.
Kallon Asmita dake tsakuran abinci Saghar ya yi yana ajiye spoon din hannunsa,jikinta ne yabata ana kallonta haka yasa babu shiri ta dago suka haɗa ido,hararanta ya yi,dan haushi ta bashi da Abbie ya tambaye su ko suna son komawa afafa har da cewa eh.
Sunkuyar da kanta ƙasa ta yi taci gaba da tsakuran abincin.
Bayan sun gama ne.zasu koma ciki Abbie. Ya ce
"Tafiyar ku da safe ne so be ready,kuma karku dau kaya da yawa saboda Monday akwai school kunji ko".
Ido kawai suka zubawa Abbie dukkansu suna tambayar kansu to me yake nufi?,kenan in suka tafi zasu dawo kenan,tunda ga shi har cewa musu yake Monday akwai school.
Ta rasa me zata ce kawai ta ce"thank you Abbie"kafin ta ja hannun Asmita suka wuce part din su,binsu a baya su Umaisha sukayi,kowa de ya rasa gane inda lamarin Abbie ya dosa.
Saghar da ya ƙasa hakuri ne ya ce"Abbie kenan zasu je su dawo ne?,Ni ban fahimta ba".
Fuskar Abbie ba yabo ba fallasa ya ce"ga shi nan de!"ya yi maganar yana fuskewa.
Be sa'ke cewa komai ba,ya miƙe yabar wajen.
Kamar yanda Abbie ya bukace su da suyi haka kuwa suka yi yar karamar trolley ta dauka ta saka musu kala biyu a ciki se dogayen hijabs.
Lieutenant general Tajuddeen
Yana nan a dakin bincike yana aiki,yaran da aka sace yau binciken sa ya tabbatar masa da Mafias ne suka sace su shisa ka ya maida hankali akan neman in da aka kai yaran,in har hasashen sa yabashi dede yaran da kuma masu kidnapping din Suna cikin garin Maiduguri kuma baze taɓa barin su bar garin nan ba se ya kwato yaran,karfe sha biyu ya kira Khalifa a waya ya sanar masa da ze kai Sabriyah Lagos gobe.
Tunda sukayi sallah asuba sukayi wanka suka shirya cikin dogayen rigunan abaya,daukan trolley din Rameesa ta yi sukayi fito falo.
Gaida kowa da suka samu afalon sukayi.dubawa ta yi taga anty amarya bata fakon hakan yasa ta haura part din ta sallama ta yi tana daga tsaye a bakin kofar,amsawa anty amarya ta yi.
"Mommy ina kwana?".
"Lafiya klau mommy's angel,how are you?".
"Am fine mommy"murmushi ta yi jin ta amsa mata da turanci,wato suna fahimtar karatu kenan duk da ma wa'yannan ƙananan words din bame wahalar wa bane.
"Mommy zamu tafi shine nazo miki sallama ki yafe min"shafa fuskarta ta yi,tana danne abinda yake yunkuro mata na baƙin ciki.
Ta ce"baki taɓa min laifi ba daughter, and in sha Allah za ki dawo wannan gidan da izinin Allah ta Allah".
Hawaye ne ta ji ya cika mata ido, hakan yasa ta rungume anty amaryan,.
Sun kusa minti uku a haka kafin ta zame jikinta ta ce"ko ma me ze faru kiyi min alkawarin bazaki taɓa komawa rayuwarki na ɗa ba?".
"Na yi miki wannan alkawarin mommy,".
Dawuwa falon tare sukayi.kowa ya hallara a falon ummah da Ammuh suna upstairs suna kallon duk wani abinda yake faruwa suna murmushi Finally burinsu de ya cika Sabriyah da Asmita sun bar gidan.
A babban filin farfajiyar gidan private jet na wajen, Khalifa su yake jira su fito,rako su har wajen sukayi suka shiga ciki.
Suna musu bye_bye a haka jet din ya tashi sama.sun tafi.
Lagos
Bayan sun isa Lagos ne motar ya zo ya dauke su ya ajiye su har cikin afafa a bakin gate din gidan karuwan da suka baro.
Duk wacce su ka haɗu a hanya se ta kallesu suna mamakin sauyawan da sukayi da kyaun da suka ƙara.
Sashen su na gidan suka nufa,suna shiga suka iske,anty Teema ita kadai tana zaune ta rame sosai ta yi baƙi ta kode kamar ba ita ba,tana daure da fallen zani.
Cikin tsoro suke kallonta a tare suka haɗa baki wajen cewa.
"Anty Teema".
Ta jima da cire tsammanin sa'ke jin muryoyin su a rayuwarta,bude idonta da bacci ya fara saceta ta yi taga dagaske yaran nata ne.
"Hot girl!, Asmita da gaske kune?,kun ga ni yanda na koma ko?, kullum addu'a ta shine, Allah yasa in gan ku kafin in mutu ashe de da rabon za mu ga juna?".
Gyara mata zama Sabriyah ta yi, tana me jin tausayin Antyn nasu,ganin yanda gaba daya ta canza ta kare.
Asmita kam ta ma gagara magana.
"Anty Teema meyake faruwa ne,,shin maganin ki ne ya ƙare?".
"Ai komai ma ya ƙare Sabriyah rayuwar bariki be yi ba ko kadan,yanzu abincin da zan sa abakina ma babu rabona da abinci tun jiya da rana.mutane biyu ne kawai suke taimaka min daga Cele se Nabiha suma tun shekaran jiya basu zo ba".
Ta yi shiru,can kuma ta sa'ke magana.
"Ku da Allah yasa kuka bar nan wani ƙaddarar ce ya dawo daku gidan nan?, kullum inna tuna bakwa s wannan gida ina jin dadi a raina domin jikina yabani kuna a hannu na gari,dubi yanda kuka yi kyau kuka canza kamar ba ku ba,cikin shiga na mutunci".
Yanda take magana ma dakyar take iya bude bakinta,se sukaji kamar basu kyauta ba na barin antyn nasu har tsawon Wannan lokaci basu san halin da take ciki ba.
Gyara mata dakin nata suka yi kafin suka dauki kuɗin da Abbie ya basu koda suna bukatar wani abu.
Suka fice, babban pharmacy suka je suka siya mata magungunanta, sannan suka tsaya a shagon trader suka siya kayan abinci.
Suna a hanya suna tafiya ne, suka hango cele na nufo su, da alamar ya ji labarin dawuwar su ne.
Yana isowa ya ƙare musu kallo sama da kasa kafin ya basu hannu suka tafa,su kansu sun yi tsananin kewar abokin nasu biye da yanda ba'a magana,sun yi farin ciki sosai da ganinsa haka shima bakinsa ya kasa rufuwa se yabon kyau da kibar da sukayi yake yi.nan ya taya su daukan kaya suka koma gida.
Asmita me girkin su ita ce yauma ta musu jallof din macaroni.ta zubawa anty Teema da yawa ta kai mata ta kai mata harda ruwa.
Kiran Nabiha a waya Cele ya yi ya shaida mata,su Sabriyah sun dawo.
Dama tana dakin su bata je ko ina ba,ai kuwa da gudu ta nufo sashen nasu.
Tana zuwa suka rungume juna cike da kewa.
Nan fa aka fara hirar yaushe gamo,suna hira a na cin abinci.
Ko da suka gama cin abincin ma baranda suka dawo suka zauna suna hira harda anty Teema,da ta ɗan warware dama har da yunwa a abinda yake damunta.
Labarin dawuwar Sabriyah da Asmita ya gama kararide gidan,tun shigowarsu dan daudu ya gansu da gudu ya je ya sanarwa boss lady cewa sun dawo, dariyar mugunta ta yi,domin dama ta dau alwashin in de suka dawo se ta yi musu abinda basu taɓa tunani ba.
Lokacin Sallah na yi suka tashi suka yi.
"Ina me baki hakuri a madadin Huraira,naji takaicin wai yau matata ce ta tsaya tana yiwa mahaifiyata rashin kunya,dan Allah ki yafe min,in sha Allah se na dau mataki akan abinda ta aikata yau din nan".
Shafa kansa Hajjatiye ta yi ta ce "ban amince ka ce zaka dau mataki akanta ba,ni a wajena komai ya riga da ya wuce,ka dena damun kanka".
Murmushi Hajiya babba ta yi wannan dalilin ne suke sa'ke son surkar tasu,ko min irin masifar da zaka ga tana yi tofa bazata yarda wani abun ya ruguza ahalinta ba,wanda be san ta bane kawai zece tana da faɗa.
Magana sukayi sosai kafin Hajjatiye da Hajiya babba suka haura upstairs jin an kira sallah.
Su kuma suna jiran su LTG su fito su tafi masallaci.
A part din Ammuh kuwa,ummah se faman Safa da marwa takeyi tunda suka shigo ta kasa tsaye ta kuma kasa zaune.
Ita kan ta Ammuh lamarin ya girgiza ta,
"Hajiya Huraira dan Allah ki nutsu mu san mafita, wannan Safa da marwa da kike yi babu inda ze kai mu".
Zama ummah ta yi"kamar ni Isma'il ze tozarta a gaban yara da kuma kishiyoyin balbali na?".
"Calm down first wannan fa ba wani babban matsala ba ce amma duk kin bi kin tayarwa da kanki hankali,ko kin manta abinda zamu iya aikatawa ne".
"Hajiya khareema ina sane amma dole raina ya ɓaci kishiya fa?,tun da be min kishiya ba se yanzu da na girma ga yara na sun gama girma shine ze min kishiya".
Matsowa kusa da ita Ammuh ta yi dan ta lura har yanzu Ummah bata dawo dede ba.
"Ki shirya ranar Lahadi muje wajen boka mauzau,daga auren shi Abbu din harna Saghar din se mun watsar dashi".
Se sannan ne taji hankalinta ya kwanta ruwa me sanyi ta bata tasha.
Bayan sallar isha uncle Hameed ya dawo kai tsaye part dinsu ya nufa.
Tsaye a jikin window ya iske Anty amarya, kallo ɗaya ta mishi ta kauda idonta,tunda yaga haka yasan cewa akwai wani abinda ya faru ga idonta da ya kumbura tasha kukanta hatta koshi.
Wajen ta yi nufa.
"Amaryata me yake faruwa na ganki haka"murya na rawa ta sanar masa da duk abubuwan da suka faru bayan tafiyarsa,kafin ya shigo din nan Hajiya babba da Ammi suka fita a part dinta bayan sun gama rarrashinta.
Jawota jikinsa ya yi yana bata hakuri shi kanshi be ji daɗin abinda ya faru ba, yasan Abbie baze taɓa yanke wannan hukuncin ba,batare da kwakkwaran dalili ba.
"Kiyi hakuri in sha Allah a wannan karon bazamu rasa yarmu ta biyu ba Sabriyah, Allah yana sane da mu,kuma ya Mubarak nasan akwai dalilin da yasa ya yanke wannan hukuncin ".
Ba ta ce mishi komai ba.
8:00pm dede lokacin cin abinci as usual ummah da Ammuh basu fito ba,haka LTG shima yana part din sa, uncle Hameed ya yi iya yin sa amma Anty amarya taki fitowa itama.
A bangaren su Umaisha ma dakyar suka sha kansu Sabriyah suka je dinning.
Kowa ka gani fuskar sa babu walwala da annuri,kawai de ana cin abincin ne,bawai dan yana shiga yanda ya kamata ba.
Kallon Asmita dake tsakuran abinci Saghar ya yi yana ajiye spoon din hannunsa,jikinta ne yabata ana kallonta haka yasa babu shiri ta dago suka haɗa ido,hararanta ya yi,dan haushi ta bashi da Abbie ya tambaye su ko suna son komawa afafa har da cewa eh.
Sunkuyar da kanta ƙasa ta yi taci gaba da tsakuran abincin.
Bayan sun gama ne.zasu koma ciki Abbie. Ya ce
"Tafiyar ku da safe ne so be ready,kuma karku dau kaya da yawa saboda Monday akwai school kunji ko".
Ido kawai suka zubawa Abbie dukkansu suna tambayar kansu to me yake nufi?,kenan in suka tafi zasu dawo kenan,tunda ga shi har cewa musu yake Monday akwai school.
Ta rasa me zata ce kawai ta ce"thank you Abbie"kafin ta ja hannun Asmita suka wuce part din su,binsu a baya su Umaisha sukayi,kowa de ya rasa gane inda lamarin Abbie ya dosa.
Saghar da ya ƙasa hakuri ne ya ce"Abbie kenan zasu je su dawo ne?,Ni ban fahimta ba".
Fuskar Abbie ba yabo ba fallasa ya ce"ga shi nan de!"ya yi maganar yana fuskewa.
Be sa'ke cewa komai ba,ya miƙe yabar wajen.
Kamar yanda Abbie ya bukace su da suyi haka kuwa suka yi yar karamar trolley ta dauka ta saka musu kala biyu a ciki se dogayen hijabs.
Lieutenant general Tajuddeen
Yana nan a dakin bincike yana aiki,yaran da aka sace yau binciken sa ya tabbatar masa da Mafias ne suka sace su shisa ka ya maida hankali akan neman in da aka kai yaran,in har hasashen sa yabashi dede yaran da kuma masu kidnapping din Suna cikin garin Maiduguri kuma baze taɓa barin su bar garin nan ba se ya kwato yaran,karfe sha biyu ya kira Khalifa a waya ya sanar masa da ze kai Sabriyah Lagos gobe.
Tunda sukayi sallah asuba sukayi wanka suka shirya cikin dogayen rigunan abaya,daukan trolley din Rameesa ta yi sukayi fito falo.
Gaida kowa da suka samu afalon sukayi.dubawa ta yi taga anty amarya bata fakon hakan yasa ta haura part din ta sallama ta yi tana daga tsaye a bakin kofar,amsawa anty amarya ta yi.
"Mommy ina kwana?".
"Lafiya klau mommy's angel,how are you?".
"Am fine mommy"murmushi ta yi jin ta amsa mata da turanci,wato suna fahimtar karatu kenan duk da ma wa'yannan ƙananan words din bame wahalar wa bane.
"Mommy zamu tafi shine nazo miki sallama ki yafe min"shafa fuskarta ta yi,tana danne abinda yake yunkuro mata na baƙin ciki.
Ta ce"baki taɓa min laifi ba daughter, and in sha Allah za ki dawo wannan gidan da izinin Allah ta Allah".
Hawaye ne ta ji ya cika mata ido, hakan yasa ta rungume anty amaryan,.
Sun kusa minti uku a haka kafin ta zame jikinta ta ce"ko ma me ze faru kiyi min alkawarin bazaki taɓa komawa rayuwarki na ɗa ba?".
"Na yi miki wannan alkawarin mommy,".
Dawuwa falon tare sukayi.kowa ya hallara a falon ummah da Ammuh suna upstairs suna kallon duk wani abinda yake faruwa suna murmushi Finally burinsu de ya cika Sabriyah da Asmita sun bar gidan.
A babban filin farfajiyar gidan private jet na wajen, Khalifa su yake jira su fito,rako su har wajen sukayi suka shiga ciki.
Suna musu bye_bye a haka jet din ya tashi sama.sun tafi.
Lagos
Bayan sun isa Lagos ne motar ya zo ya dauke su ya ajiye su har cikin afafa a bakin gate din gidan karuwan da suka baro.
Duk wacce su ka haɗu a hanya se ta kallesu suna mamakin sauyawan da sukayi da kyaun da suka ƙara.
Sashen su na gidan suka nufa,suna shiga suka iske,anty Teema ita kadai tana zaune ta rame sosai ta yi baƙi ta kode kamar ba ita ba,tana daure da fallen zani.
Cikin tsoro suke kallonta a tare suka haɗa baki wajen cewa.
"Anty Teema".
Ta jima da cire tsammanin sa'ke jin muryoyin su a rayuwarta,bude idonta da bacci ya fara saceta ta yi taga dagaske yaran nata ne.
"Hot girl!, Asmita da gaske kune?,kun ga ni yanda na koma ko?, kullum addu'a ta shine, Allah yasa in gan ku kafin in mutu ashe de da rabon za mu ga juna?".
Gyara mata zama Sabriyah ta yi, tana me jin tausayin Antyn nasu,ganin yanda gaba daya ta canza ta kare.
Asmita kam ta ma gagara magana.
"Anty Teema meyake faruwa ne,,shin maganin ki ne ya ƙare?".
"Ai komai ma ya ƙare Sabriyah rayuwar bariki be yi ba ko kadan,yanzu abincin da zan sa abakina ma babu rabona da abinci tun jiya da rana.mutane biyu ne kawai suke taimaka min daga Cele se Nabiha suma tun shekaran jiya basu zo ba".
Ta yi shiru,can kuma ta sa'ke magana.
"Ku da Allah yasa kuka bar nan wani ƙaddarar ce ya dawo daku gidan nan?, kullum inna tuna bakwa s wannan gida ina jin dadi a raina domin jikina yabani kuna a hannu na gari,dubi yanda kuka yi kyau kuka canza kamar ba ku ba,cikin shiga na mutunci".
Yanda take magana ma dakyar take iya bude bakinta,se sukaji kamar basu kyauta ba na barin antyn nasu har tsawon Wannan lokaci basu san halin da take ciki ba.
Gyara mata dakin nata suka yi kafin suka dauki kuɗin da Abbie ya basu koda suna bukatar wani abu.
Suka fice, babban pharmacy suka je suka siya mata magungunanta, sannan suka tsaya a shagon trader suka siya kayan abinci.
Suna a hanya suna tafiya ne, suka hango cele na nufo su, da alamar ya ji labarin dawuwar su ne.
Yana isowa ya ƙare musu kallo sama da kasa kafin ya basu hannu suka tafa,su kansu sun yi tsananin kewar abokin nasu biye da yanda ba'a magana,sun yi farin ciki sosai da ganinsa haka shima bakinsa ya kasa rufuwa se yabon kyau da kibar da sukayi yake yi.nan ya taya su daukan kaya suka koma gida.
Asmita me girkin su ita ce yauma ta musu jallof din macaroni.ta zubawa anty Teema da yawa ta kai mata ta kai mata harda ruwa.
Kiran Nabiha a waya Cele ya yi ya shaida mata,su Sabriyah sun dawo.
Dama tana dakin su bata je ko ina ba,ai kuwa da gudu ta nufo sashen nasu.
Tana zuwa suka rungume juna cike da kewa.
Nan fa aka fara hirar yaushe gamo,suna hira a na cin abinci.
Ko da suka gama cin abincin ma baranda suka dawo suka zauna suna hira harda anty Teema,da ta ɗan warware dama har da yunwa a abinda yake damunta.
Labarin dawuwar Sabriyah da Asmita ya gama kararide gidan,tun shigowarsu dan daudu ya gansu da gudu ya je ya sanarwa boss lady cewa sun dawo, dariyar mugunta ta yi,domin dama ta dau alwashin in de suka dawo se ta yi musu abinda basu taɓa tunani ba.
Lokacin Sallah na yi suka tashi suka yi.