Sashe 50
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
yanda suka zo haka suka koma, yanzu kamar dazun har suka dawo gida Parsa batayi magana ba.ita kanta Iklas seda ta yi mamaki kowa yasan ba halinta bane wannan amma ta yi shuru kamar me tunani.
Fita a motar Iklas ta yi ta barsu su biyu.kokarin bude motar ta yi taji taki budewa ta fahimci sarai Sahil ya saka lock ne a motar.
"Masoyiya meya sameki gaba daya kika sauya kamar ba ke ba!?"ya tambayeta yana tsareta da idon sa da takejin kunyar kallo.
"Bakomai"ta ba sa amsa a hankali.
"Karya kike, kowa yasan ba haka kike ba so tell me is something wrong?"girgiza mishi kai ta yi.
Haɗe fuska ya yi "kalli idona da kyau"ka sa dagowa ta yi.
Ya sake maimaita mata a karo na biyu.
"Kalli idona Parsa".
Dakyar ta iya masa kallon da be fi na second biyu ba.
"Tom sanar da ni meke faruwa".
Hawaye ne ya gangaro daga fuskarta,ya ɗigo akan hannunta.
Da mamaki ya sa'ke kallonta.
"Bazakiyi magana ba!?".
Tana sheshekar kuka ta ce "to ai ya Sahil kai ne".
"Ni ne meye Parsa"
Share fuskarta ta yi ta ce "to ba kai bane kace kana da budurwa a kano ba,kuma shine baka sanar damu kana da budurwa ba, ko a waya fa baka taɓa haɗa mu da ita ba ɓalle mu san antyn na mu,for God sake hakan ya yi ya Sahil.kasan yanda muke so a sha biki a gidanmu kuwa musamman na aurenka se yafi na kowa dadi,se munyi event goma a matsayin mu na ƙannen ango". lokaci daya ta canza magana domin bata da karfin guiwar da zata iya faɗa masa tana san shi, wannan dalilin yasata sauya maganar kawai.
Tunda ta fara magana yake kallonta,be yarda da Abinda ta faɗa ba,kawai ya ji ta ne, murmushi ya yi ya bude mata kofa yana murmushi.
Ya ce"shikenan yau din nan zan haɗa ku waya da ita".
Yaƙe ta yi ta fice a motar.
Bin bayanta ya yi da kallo har ta shige ciki.
Ajiyar zuciya ya yi, ya ce "nasan abinda yake cikin ranki masoyiya".
Yana fitowa daga motar yaga su Abbu sun fito duk sunyi alwala zasu je masallaci binsu ya yi.
"Saghar sun dawo ne,ya aikin nata?"
Ya tambayi Ashman.
"Alhamdulillah an yi aiki successful.se gobe za'a fara ganinta".
Shima "Alhamdulillah"ya faɗa.
Suna shigowa Sabriyah ta nufi part din Hajiya babba ta ga ko Asmita ta farka daga bacci,sannan ta yi mata albishiri da an siya musu sabbin wayoyi.ga kuma takardar da har lokacin yana rike kam a hannunta.
Haɗuwa da Hajiya babba ta yi a mahayan ƙarshe,ta ce"har kun dawo kenan?!", "Eh mun dawo Hajiya babba zan je in duba Asmita ne "riƙo hannunta ta yi ta ce"ya'yan ku Tajuddeen yace kar abar kowa ta shiga part din se bayan ya dawo".
Ba dan ranta yaso ba haka suka dawo main part da Hajiya babba,
Anty sakeena ta ce "ku je kuyi sallah"miƙewa sukayi banda Sabriyah dake zaune ta saba duk sanda zasu je yin Sallah tana zaune abunta.
Kallon ta anty sakeena ta yi.
"Sabriyah tashi muje muyi sallah" "to"
ta bi bayanta.
Ta ce mata ta shiga ta yi tsarki.bayan ta yi ne,ta koya mata yanda zata yi alwala.itama ta dauro nata alwala.
Sannan ta ce mata duk yanda ta yi a sallah itama ta yi.
Haka sukayi sallah tare suka idar.
Uncle Hameed ya dawo gida.ya sanar da mom Rumanatu da Abbie,an yi nasara a aikin da aka mata,ba za'a jima ba zata farfaɗo shisa Saghar be dawo ba yana can.
Lokacin dinner ma gaba dayansu sun hallara,a dinning an yi saving din kowa abincin da yake so, Ammuh de bata fito ba dama can ita bata cin abincin su akan dinning se lokaci zuwa lokaci da Abbie yaga bata so se be ce lallai dole se tazo ba,haka ummah ma duk da ita tana fitowa amma bako da yaushe ba.
Fatime na gama serving din su takaiwa Ammuh da Ummah nasu part din su.
Ita de Sabriyah ta gama fahimtar akwai wani abu da ake boye mata,ba sa son ta sani,amma tunda LTG ya ce se ya dawo zataga Asmita to ita kuma ko karfe ɗari na dare ze dawo seta jirasa.
Bata wani ci abincin sosai ba,ta cire hannunta ba wani yunwa take ji ba.
"Ya kika cire hannunki"cewar Parsa.
"Masoyiya na koshi Wallahi".
Anty amarya dake gefenta bata ce mata komai ba, tasan dalilin ta be wuce rashin ganin Asmita bane.
Dawood ne ya miko mata wayarta.
"Yawwa ga shi na seta miki komai,daga icloud har updating din wayar na miki.
Wayarki za ki iya fara amfani da ita.akwai kati a ciki sannan data kuma daga zaran kin kunna WiFi shikenan,bakya bukatar data gidan nan kowa WiFi dinsa yake budewa".
"To na gode ya Dawood".
"Don't mention ".
Kallon wayar ta yi.tana Allah_ Allah su watse anan taje ta dauko takardan da ta boye,ta kira taji waye ne.
Hira sukayi kafin Hajjatiye ta ce ita fa surutun ya ishe ta,ta barsu a falo taje ta kwanta.
9:00pm na dare ta fara motsawa alamar zata farka.dakyar ta samu ta daga hannunta da ya yi mata nauyi ta ɗan da fa kanta,ji tayi kan akwai bandeji gaba daya an zagaye sa dashi,ga wani uban ciwo da kan yake mata.
Runtse idonta ta yi,tanaso ta tashi amma jiri ya hanata.
Ta riga da tasan a inda take,domin lokacin da suka iso asibiti ta farfaɗo nan uncle Hameed ya sanar da ita yanzu za'a shiga da ita operation,allura akayi mata na bacci fuskar Saghar shine fuskan wanda ta gani kafin ta faɗa bacci.
Hakan yasa a hankali muryanta baya fita sosai ta soma kiran sunan sa.
"Me kyau!me kyau!me kyau"yana bakin kofa suna magana shida wani doctor ya ji kamar ana magana a cikin dakin.
Shigowa ya yi ya sameta tana kwance idonta abude.
Murmushi ya yi ganin ta farka.
"Sannu ko,yanzu ina ne yake miki ciwo".
Bata ba shi amsar tambayar da ya mata ba ta ce"Sabriyah ta zo ne!?". girgiza kai ya yi.
Murya a hankali ta kuma cewa"meyasa batazo ba to me kyau !?",jin sunan da ta kirasa dashi ne yasa ya kalleta da kyau,wato wancan memoryn yarintar da ta shiga ba duka bane ya gushe ba,tunda ga shi still bayan ta dawo hayyacinta tana kiransa da me kyau.
Ya ce"bata ma san an yi miki aiki ba saboda zata iya tayar da hankalinta amma gobe duk zasu zo dubasu da jiki"gyada masa kai ta yi.
"Kai na!,na mini ciwo sosai kuma ina ganin jiri"zama ya yi a gefen gadon ya ce "ehh wannan normal ne,nan da wasu kwanaki za ki dena jin haka".
Shuru ne ya biyo baya daga ita har shi babu wanda ya sa'ke cewa komai.
"Me kyau ban san sunanka ba"batare da ya kalleta ba,ya amsa mata da "Saghar".
Nan ma shuru ne ya sa'ke ratsawa, miƙewa ya yi ze fice,dan ya rasa meyasa duk lokacin da yake tare da ita se ya ji wani iri.
"Ya Saghar tafiya zakayi ka barni ni ɗaya!?"ya tsinkayi muryarta tana tambayarsa.
juyowa ya yi idonshi ya sauka cikin nata narkakkun idanun ta kafesa dashi tana kallonsa.
Komawa ya yi,ya zauna yana kallonta.
"Asmee dama kema matsoraciya ce!?".
"Ah ah naga zaka tafi ne ai to"
"Ke kuma bakya son in tafi?",sun kuyar da kanta ƙasa ta yi.
"Kina bukatar hutu ne za'a miki allura,za ki yi bacci ba'a son ki dinga magana sosai"gyada masa kai ta yi.
Yanda suke yiwa juna magana duk wanda ya kallesu ze yi tunanin sun daɗe da sanin juna,ko kuma akwai shakuwa sosai.
Se karfe goma ya bar dakin nata se da ya tabbatar da ta yi bacci kafin ya fito.yana kashe mata light.
Tana part din anty amarya idonta biyu ba tayi bacci ba tana jiran dawuwar LTG.
Anty amarya ma idanunta biyu,ita kanta jiran LTG takeyi ya dawo, saboda duk sanda ya fita ya yi dare ita da Ammi in ba sunji dawuwar sa ba tofa basa iya bacci.
Suna zaune tana ta koya mata wasu abubuwa.idanunsu biyu har sha biyu ya gota,nan ma shuru be dawo ba.
Wayarta ta dauka ta kira layinsa sede switch off.hakan yasa anty amarya ta dinga addu'a Allah de yasa lafiya.
Karfe 1:00 na dare motocin suka diro cikin gidan,anty amarya da Ammi da Abbie da suka kasance idon su biyu suna jiran dawuwar su sukayi hamdala.
Dama ya saba duk sanda ya yi dare ita yake kira a kawo masa coffee.
Suna zaune kira ya shigo wayarta ganin shine yasa ta daga.
"Anty amarya coffee please"haka kawai ya ce ya kashe wayar.
Miƙewa ta yi ta shiga kitchen din part dinta,cikin mintuna ƙalilan ta haɗa masa coffee, tunani ta fara zuwa ta tashi fatime ko kaltume,se kuma taga in ta yi haka kamar bata kyauta ba,duba da yanda suke yini suna aiki,dare ne kawai lokacin hutun su.
Kallon Sabriyah dake ɗale akan gado ta yi ta ce"sa hijabi ki zo ki nan"dogon hijab din da ta cire akan gadon ta dauka tasaka har ƙasa yazo mata.
Ba ta tray din coffee din ta yi,"ki kaiwa ya'yan ku Tajuddeen".
"To"har ta kai bakin kofa anty amarya ta ce"karki kuskura ki kirasa da wannan mugun da naji kike kiransa,ya Taj haka su Umaisha suke kiransa"gyada kai ta yi ta fita.
Knocking ta yi,ta ji shuru kusan five minutes tana tsaye can ta yanke shawarar shiga ciki kawai.
Ba kowa a bedroom din da alama yana wanka.
Ajiye coffee din ta yi akan Centre table.ta tsaya tana jiransa dan ta kudurci niyar tambayarsa ganin Asmita.
Idonta ne ya sauka akan wani ƙaramin hotonsa da Asrah a jiye akan bedside locker.
Nufan wajen ta yi tasa hannu ta dauki hoton kenan ta ji alamar mutum daf da ita.a tsorace ta juya,yana tsaye daf da ita distance din dake tsakanin su be fi taku biyu ba kwakkwaran motsi in ta yi jikinsu ze iya haɗuwa,ja da baya ta yi ta manne a jikin bango.
Dan ta tsorata da ganin yanayinsa na yau fuskarsa kamar wanda aka yiwa mutuwa,hannu na rawa ta ajiye hoton a inda ta dauka.
Yana sanye da rigar towel da ya rufe masa jiki kafafunsa ne kawai a waje.
Fita a motar Iklas ta yi ta barsu su biyu.kokarin bude motar ta yi taji taki budewa ta fahimci sarai Sahil ya saka lock ne a motar.
"Masoyiya meya sameki gaba daya kika sauya kamar ba ke ba!?"ya tambayeta yana tsareta da idon sa da takejin kunyar kallo.
"Bakomai"ta ba sa amsa a hankali.
"Karya kike, kowa yasan ba haka kike ba so tell me is something wrong?"girgiza mishi kai ta yi.
Haɗe fuska ya yi "kalli idona da kyau"ka sa dagowa ta yi.
Ya sake maimaita mata a karo na biyu.
"Kalli idona Parsa".
Dakyar ta iya masa kallon da be fi na second biyu ba.
"Tom sanar da ni meke faruwa".
Hawaye ne ya gangaro daga fuskarta,ya ɗigo akan hannunta.
Da mamaki ya sa'ke kallonta.
"Bazakiyi magana ba!?".
Tana sheshekar kuka ta ce "to ai ya Sahil kai ne".
"Ni ne meye Parsa"
Share fuskarta ta yi ta ce "to ba kai bane kace kana da budurwa a kano ba,kuma shine baka sanar damu kana da budurwa ba, ko a waya fa baka taɓa haɗa mu da ita ba ɓalle mu san antyn na mu,for God sake hakan ya yi ya Sahil.kasan yanda muke so a sha biki a gidanmu kuwa musamman na aurenka se yafi na kowa dadi,se munyi event goma a matsayin mu na ƙannen ango". lokaci daya ta canza magana domin bata da karfin guiwar da zata iya faɗa masa tana san shi, wannan dalilin yasata sauya maganar kawai.
Tunda ta fara magana yake kallonta,be yarda da Abinda ta faɗa ba,kawai ya ji ta ne, murmushi ya yi ya bude mata kofa yana murmushi.
Ya ce"shikenan yau din nan zan haɗa ku waya da ita".
Yaƙe ta yi ta fice a motar.
Bin bayanta ya yi da kallo har ta shige ciki.
Ajiyar zuciya ya yi, ya ce "nasan abinda yake cikin ranki masoyiya".
Yana fitowa daga motar yaga su Abbu sun fito duk sunyi alwala zasu je masallaci binsu ya yi.
"Saghar sun dawo ne,ya aikin nata?"
Ya tambayi Ashman.
"Alhamdulillah an yi aiki successful.se gobe za'a fara ganinta".
Shima "Alhamdulillah"ya faɗa.
Suna shigowa Sabriyah ta nufi part din Hajiya babba ta ga ko Asmita ta farka daga bacci,sannan ta yi mata albishiri da an siya musu sabbin wayoyi.ga kuma takardar da har lokacin yana rike kam a hannunta.
Haɗuwa da Hajiya babba ta yi a mahayan ƙarshe,ta ce"har kun dawo kenan?!", "Eh mun dawo Hajiya babba zan je in duba Asmita ne "riƙo hannunta ta yi ta ce"ya'yan ku Tajuddeen yace kar abar kowa ta shiga part din se bayan ya dawo".
Ba dan ranta yaso ba haka suka dawo main part da Hajiya babba,
Anty sakeena ta ce "ku je kuyi sallah"miƙewa sukayi banda Sabriyah dake zaune ta saba duk sanda zasu je yin Sallah tana zaune abunta.
Kallon ta anty sakeena ta yi.
"Sabriyah tashi muje muyi sallah" "to"
ta bi bayanta.
Ta ce mata ta shiga ta yi tsarki.bayan ta yi ne,ta koya mata yanda zata yi alwala.itama ta dauro nata alwala.
Sannan ta ce mata duk yanda ta yi a sallah itama ta yi.
Haka sukayi sallah tare suka idar.
Uncle Hameed ya dawo gida.ya sanar da mom Rumanatu da Abbie,an yi nasara a aikin da aka mata,ba za'a jima ba zata farfaɗo shisa Saghar be dawo ba yana can.
Lokacin dinner ma gaba dayansu sun hallara,a dinning an yi saving din kowa abincin da yake so, Ammuh de bata fito ba dama can ita bata cin abincin su akan dinning se lokaci zuwa lokaci da Abbie yaga bata so se be ce lallai dole se tazo ba,haka ummah ma duk da ita tana fitowa amma bako da yaushe ba.
Fatime na gama serving din su takaiwa Ammuh da Ummah nasu part din su.
Ita de Sabriyah ta gama fahimtar akwai wani abu da ake boye mata,ba sa son ta sani,amma tunda LTG ya ce se ya dawo zataga Asmita to ita kuma ko karfe ɗari na dare ze dawo seta jirasa.
Bata wani ci abincin sosai ba,ta cire hannunta ba wani yunwa take ji ba.
"Ya kika cire hannunki"cewar Parsa.
"Masoyiya na koshi Wallahi".
Anty amarya dake gefenta bata ce mata komai ba, tasan dalilin ta be wuce rashin ganin Asmita bane.
Dawood ne ya miko mata wayarta.
"Yawwa ga shi na seta miki komai,daga icloud har updating din wayar na miki.
Wayarki za ki iya fara amfani da ita.akwai kati a ciki sannan data kuma daga zaran kin kunna WiFi shikenan,bakya bukatar data gidan nan kowa WiFi dinsa yake budewa".
"To na gode ya Dawood".
"Don't mention ".
Kallon wayar ta yi.tana Allah_ Allah su watse anan taje ta dauko takardan da ta boye,ta kira taji waye ne.
Hira sukayi kafin Hajjatiye ta ce ita fa surutun ya ishe ta,ta barsu a falo taje ta kwanta.
9:00pm na dare ta fara motsawa alamar zata farka.dakyar ta samu ta daga hannunta da ya yi mata nauyi ta ɗan da fa kanta,ji tayi kan akwai bandeji gaba daya an zagaye sa dashi,ga wani uban ciwo da kan yake mata.
Runtse idonta ta yi,tanaso ta tashi amma jiri ya hanata.
Ta riga da tasan a inda take,domin lokacin da suka iso asibiti ta farfaɗo nan uncle Hameed ya sanar da ita yanzu za'a shiga da ita operation,allura akayi mata na bacci fuskar Saghar shine fuskan wanda ta gani kafin ta faɗa bacci.
Hakan yasa a hankali muryanta baya fita sosai ta soma kiran sunan sa.
"Me kyau!me kyau!me kyau"yana bakin kofa suna magana shida wani doctor ya ji kamar ana magana a cikin dakin.
Shigowa ya yi ya sameta tana kwance idonta abude.
Murmushi ya yi ganin ta farka.
"Sannu ko,yanzu ina ne yake miki ciwo".
Bata ba shi amsar tambayar da ya mata ba ta ce"Sabriyah ta zo ne!?". girgiza kai ya yi.
Murya a hankali ta kuma cewa"meyasa batazo ba to me kyau !?",jin sunan da ta kirasa dashi ne yasa ya kalleta da kyau,wato wancan memoryn yarintar da ta shiga ba duka bane ya gushe ba,tunda ga shi still bayan ta dawo hayyacinta tana kiransa da me kyau.
Ya ce"bata ma san an yi miki aiki ba saboda zata iya tayar da hankalinta amma gobe duk zasu zo dubasu da jiki"gyada masa kai ta yi.
"Kai na!,na mini ciwo sosai kuma ina ganin jiri"zama ya yi a gefen gadon ya ce "ehh wannan normal ne,nan da wasu kwanaki za ki dena jin haka".
Shuru ne ya biyo baya daga ita har shi babu wanda ya sa'ke cewa komai.
"Me kyau ban san sunanka ba"batare da ya kalleta ba,ya amsa mata da "Saghar".
Nan ma shuru ne ya sa'ke ratsawa, miƙewa ya yi ze fice,dan ya rasa meyasa duk lokacin da yake tare da ita se ya ji wani iri.
"Ya Saghar tafiya zakayi ka barni ni ɗaya!?"ya tsinkayi muryarta tana tambayarsa.
juyowa ya yi idonshi ya sauka cikin nata narkakkun idanun ta kafesa dashi tana kallonsa.
Komawa ya yi,ya zauna yana kallonta.
"Asmee dama kema matsoraciya ce!?".
"Ah ah naga zaka tafi ne ai to"
"Ke kuma bakya son in tafi?",sun kuyar da kanta ƙasa ta yi.
"Kina bukatar hutu ne za'a miki allura,za ki yi bacci ba'a son ki dinga magana sosai"gyada masa kai ta yi.
Yanda suke yiwa juna magana duk wanda ya kallesu ze yi tunanin sun daɗe da sanin juna,ko kuma akwai shakuwa sosai.
Se karfe goma ya bar dakin nata se da ya tabbatar da ta yi bacci kafin ya fito.yana kashe mata light.
Tana part din anty amarya idonta biyu ba tayi bacci ba tana jiran dawuwar LTG.
Anty amarya ma idanunta biyu,ita kanta jiran LTG takeyi ya dawo, saboda duk sanda ya fita ya yi dare ita da Ammi in ba sunji dawuwar sa ba tofa basa iya bacci.
Suna zaune tana ta koya mata wasu abubuwa.idanunsu biyu har sha biyu ya gota,nan ma shuru be dawo ba.
Wayarta ta dauka ta kira layinsa sede switch off.hakan yasa anty amarya ta dinga addu'a Allah de yasa lafiya.
Karfe 1:00 na dare motocin suka diro cikin gidan,anty amarya da Ammi da Abbie da suka kasance idon su biyu suna jiran dawuwar su sukayi hamdala.
Dama ya saba duk sanda ya yi dare ita yake kira a kawo masa coffee.
Suna zaune kira ya shigo wayarta ganin shine yasa ta daga.
"Anty amarya coffee please"haka kawai ya ce ya kashe wayar.
Miƙewa ta yi ta shiga kitchen din part dinta,cikin mintuna ƙalilan ta haɗa masa coffee, tunani ta fara zuwa ta tashi fatime ko kaltume,se kuma taga in ta yi haka kamar bata kyauta ba,duba da yanda suke yini suna aiki,dare ne kawai lokacin hutun su.
Kallon Sabriyah dake ɗale akan gado ta yi ta ce"sa hijabi ki zo ki nan"dogon hijab din da ta cire akan gadon ta dauka tasaka har ƙasa yazo mata.
Ba ta tray din coffee din ta yi,"ki kaiwa ya'yan ku Tajuddeen".
"To"har ta kai bakin kofa anty amarya ta ce"karki kuskura ki kirasa da wannan mugun da naji kike kiransa,ya Taj haka su Umaisha suke kiransa"gyada kai ta yi ta fita.
Knocking ta yi,ta ji shuru kusan five minutes tana tsaye can ta yanke shawarar shiga ciki kawai.
Ba kowa a bedroom din da alama yana wanka.
Ajiye coffee din ta yi akan Centre table.ta tsaya tana jiransa dan ta kudurci niyar tambayarsa ganin Asmita.
Idonta ne ya sauka akan wani ƙaramin hotonsa da Asrah a jiye akan bedside locker.
Nufan wajen ta yi tasa hannu ta dauki hoton kenan ta ji alamar mutum daf da ita.a tsorace ta juya,yana tsaye daf da ita distance din dake tsakanin su be fi taku biyu ba kwakkwaran motsi in ta yi jikinsu ze iya haɗuwa,ja da baya ta yi ta manne a jikin bango.
Dan ta tsorata da ganin yanayinsa na yau fuskarsa kamar wanda aka yiwa mutuwa,hannu na rawa ta ajiye hoton a inda ta dauka.
Yana sanye da rigar towel da ya rufe masa jiki kafafunsa ne kawai a waje.