Sashe 39
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata tanka masa ba ta mike tana cizan libs dinta ta fice masa a part.
Kai kanta toilet ta yi,ta gasa jikinta da ruwan zafi nan taji dadi.ko lotion bata shafa ba ta saka wata karamar riga ta kwanta.
Shigowa dakin Rameesa ta yi tazo dubawa ko Sabriyah din ta dawo,ko kuwa LTG har yanzu yana rike da ita.nan ta sameta baje akan gado.
"Sabriyah yana ganki a kwance!?"ta yi mata tambaya tana shigowa dakin,dago kai tayi ta je fa mata uwar harara kafin ta bata amsa "da a tsaye kikeso ki gan ni!?"ta tambaye ta tana maida kanta ta kwanta.
Dama Rameesa dan neman magana ne yasa ta yi mata wannan tambayar,tana sanye da hijabin da ta idar da sallah isha ta zauna a gefenta.
"Tashi muje dakinmu yau a can zamu ci abinci"cewar Rameesa,tabe fuska ta yi kamar zata sa ihu ta ce"Rameesa dan Allah ki barni in huta bana jin yunwa,haba tun shigowar ki kika dameni da magana bana ciki da tambaɗa", "hhhhhhhh! Allah yabaki hakuri sarkin yaƙi"
Tana gama gaya mata haka ta fice.
Suna zaune a dinning kowa anyi saving dinsa abinci mazan sun fara ci Ammi ta ce"wai nikam ina yan mata na ne!?" "Nima abinda nake son na tambaya kenan yau tunda na dawo aiki banji ɗu riyar su ba"Saghar ya faɗa yana ajiye spoon din hannunshi.
Sahil ya ce"yau ɓarna suka je yi wa LTG shikuma ya sa su punishment,yanzu de suna part dinsu ko wacce na jinyar jikinta",anty amarya, Ammi, Hajiya babba,ummah kallon Sahil dake basu labari suke yi dan su da suke cikin gidan ma basu san anyi haka ba.
Mikewa uncle Hameed ya yi yana magana"yanzu shalelen yan matan namu LTG ka galabaitar wayyo,ko wani hali Madam Zoya take cike oho!?"dariya suka kwashe dashi harda shi uncle Hameed din da ya yi maganar sannan ya nufi part dinsa,shide LTG ko ta kansu be bi ba cikin nutsuwa yake cin abincisa.
Sahil ya sake cewa"kuma babban abin tausayin shine harda wannan Sabriyah din da ya kawo gidan nan ya saka punishment din"zaro ido waje Ammi da anty amarya sukayi sannan suka maida kallonsu kan LTG.
"Yanzu Tajuddeen har da bakuwar mun ma baka bari ba!?,ni Wallahi har kunyarta ya kamani,ka sato ta sannan kazo kana haɗa ta da kannnenka kana musu Punishment!?"ta tambayesa tana riƙe habarta.
Ɗaukar wayarsa ya yi, ya bar musu dinning table din,ya nufi part din Abbie da baya nan.
Anty amarya da Ammi ne suka shiga part din dubasu.ga kuma fatime da ta shirya musu nasu abincin ta kai musu.
Sosai Ammi ta musu faɗa akan shiga masa part binciken da sukayi domin koda basu ɗauki komai ba ze ce sun mishi ɓarna,ga shi yanzu a banza ya sa su punishment.
Haka suka je wajen Sabriyah ma nan kam sannu sukayi mata sannan anty amarya ta zauna da ita tana bata abinci abaki tun bata karba hatta soma karba,bata barta ba se da ta tabbatar da ta koshi.lokacin har karfe 9:00 saura nan ta yi mata se da safe ta fita.kwanciya Sabriyah ta yi dan bacci takeji sosai sannan ta kwanta da ya ƙinin gobe LTG ze mayar da ita Lagos.
Sergent Khalifa ne da suke cikin dajin Kano sun yi ɗauki ba da ɗi da yan ta'addan da LTG ya tura su wajensu kuma sunyi nasara,nan ya samu ya kira LTG din a waya.
Yana dakin bincike da layin wayarsu yake bibiyar yan ta'addan da kuma su major Marry,shi yake basu direction akan inda zasu je da kuma yanda zasu yi yana daga zaune akan kujera ga hot black tea a kusa dashi.
"Hello LTG, Alhamdulillah mun gama dasu sede an harbi major Marry a hannunta na dama, sannan munyi losing din sojan mu daya!".
"Na sani na turo muku helicopter,ku dawo yanzu.and what about the girl fatan basu kasheta ba!?".
LTG ya jefawa Khalifa tambaya.
"Mun samota sede bata cikin hankalinta ina tunanin ma zeye wuya in bata haukace ba sakamakon bakar fodar ibilis din da suka dinga shaƙa mata"
Jinjina kai kawai ya yi,ya kashe wayarsa.
Bari mu leka bangaren magajiya boss lady.
Tun ranar da aka sace Sabriyah da Asmita boss lady ta tayar da hankalinta,ko ina a cikin Lagos tasa a nemo mata su tunda har ita zasu iya yaudara su gudu daga gidan ba tare da ta yanta su ba amma ba'a samesu ba, domin ita gani take yi Sabriyah da Asmita guduwa sukayi daga gidan, wa'yanda akayi abun a gabansu sun yi mata bayani dallah_dallah kan cewa sace su akayi ,amma fir boss lady ta ƙi yarda da hakan, ta kudiri niyar duk sanda ta yi tozali dasu ko kuma tasa aka kamo mata su seta sa sun dandana guɗarsu.
Cele kullum se ya shigo afafa da sa ran ko ze ga Sabriyah da Asmita sun dawo,amma haka ze jisu shuru,ga anty Teema da ciwonta yanzu ya fara tashi gadan_gadan babu wanda yake zuwa dubata da taimaka mata se Nabiha da Cele,su suke kawo mata abinci da kuma magani.
Katsina state
Gidan mom Rumanatu Bishara yau zamu leka.
Babban gida ne kerarren gida wanda ya gaji da haɗuwa wato gidan minister Abu Sufyan Ubaid. Abu Sufyan ministan harkokin jiga da ficen kuɗaɗe ne,suna rayuwar farin ciki shida matarsa ɗaya se ya'yan su hudu biyu maza biyu mata.
Babban dan su shine Ashman da ya kasance babban manager a company babanshi Abu Sufyan,se Dawood shi kuma engineer ne.
Se ƙannen su mata,wanda suke saƙo da saƙo, Iftisan ce babba se yar autar su Jaleelah me shekara sha shida.
Tunda na shigo gidan na soma jin hayaniya kamar ana dambe a falo,leka kaina ciki nayi na hango wasu kyawawan yan mata guda biyu wanda kan su ɗaya kayan jikinsu kuwa dayar na sanye da jeans din wando baƙi da riga,dayar kuma doguwar riga take sanye dashi.
Dambe suke yi kamar zasu kashe junansu kuma badan komai ba se akan remote,da gudu na hango mom Rumanatu ta sauka daga downstairs tana ihun.
"Iftisan da Jaleelah bazaku bar wannan faɗan ba ko!?"karasowa cikin falon ta yi ta samu ta shiga tsakanin su ta raba faɗan, dukkansu biyu se haki suke yi suna hararan junansu.
"Mommy kin ga yanda Jaleelah take hararata ko!?, gaba-daya ta gama rena ni"Iftisan ta yi maganar tana nuna Jaleelah da yar yatsa.
"Yanzu wannan damben da ku ka za ge Kunayi kamar wasu makiyan juna duk akan menene!?"mom Rumanatu ta tambayesu tana bin ko wacce da kallo.
Cikin shagwaba Jaleelah ta ce "mommy ina zaune ne fa ina kallon cartoon shine Iftisan tazo wai sede in bata remote ta kamo mbc Bollywood shine na ƙi bata remote din,shine fa...shine fa ta fara dukana".
Kallon Iftisan din mom Rumanatu ta yi"yanzu akan wannan abin kuka tsaya faɗa,ina ce ta kan hakane ko waccen ku aka sa mata Tv a bedroom dinta!?,amma hakan be muku ba se kunzo falon downstairs kun yi mini faɗa ko!?,to bari yayanku ya dawo sena saka ya muku dan banzan duka.kuma daga yau kar wacce na sa'ke kallo a falo, da sunan tazo kallo tunda ku kamar wasu mayu kullum kuna cikin faɗa,jini daya uwarku daya ubanku ɗaya amma ko da yaushe kuna cikin faɗa kamar wasu ka ji".
"Mommy kiyi hakuri bazamu sa'ke ba!,and kiyiwa wannan fitsararriya magana ta dena mini rashin kunya na girmeta da shekara daya so am not her mate". Iftisan ta yi magana tana zazzagawa Jaleelah buhun harara kai kace idanunta zasu faɗo kasa.
Girgiza kai mom Rumanatu ta yi dan ita rikicin Iftisan da Jaleelah ya fara isarta,jira take yi Ashman ko Dawood wani ya dawo tasa su zane mata su.
Ta ce"ku bani guri ko in gwara kanku da kujerar nan"turo baki Jaleelah ta yi ido cike da hawaye ta ce"sorry mom! please karki faɗawa su ya Ashman". hararanta mom Rumanatu ta yi, sannan ta sake daka musu tsawa da gudu ko wacce ta nufi bedroom dinta.
Zama ta yi a palour tana girgiza kanta,kallon agogon dake manne a falon ta yi taga 9:50pm na dare ga shi basu dawo ba,jiransu takeyi dan tasan daga su har daddyn nasu suna tare.
Da sauri me aikinta ta shigo falon riƙe da wayar mom Rumanatu da ta barshi a bedroom dinta.
"Anty! Hajjatiye ce ke kiranki"ta faɗa tana me miƙa mata wayar,da sauri mom Rumanatu ta karba jin an ce mahaifiyar su ce kiranta.
Tana sa wayar a kunne ta ji Hajjatiye ta fashe da kuka.
Gabanta ne ya faɗi aranta ta ce "yau kuma laifin me nayiwa Hajjatiye ni Rumanatu".
Murya a sanyaye ta yi magana"assalamualaikum! Hajjatiye na Barka da wannan lokacin".
A bangaren Hajjatiye kuwa jan majina ta yi,ta ce "munafukar banza da wofi babu tsiyar tsinantakar da gaisuwar ki zata mini!ku kasheni kawai ku huta,nagaji da tsiyar tsinantakar ku bazan iya ba,baze yu ba".
Daura hannu aka mom Rumanatu ta yi jin yanda Hajjatiye ke surfa mata ruwan masifa.
Ta ce"haba Hajjatiye na, faɗamin laifin me mukayi nida su ya Mubarak din!?".
Cikin masifa Hajjatiye ta sa'ke hayayyaƙowa mom Rumanatu"bansaniba!, ni zaku mayar tsohuwar banza ko,ku ce zaku turo anlikonta ya ɗauke ni inzo Nijeriya shine zaku watsa mini ƙasa a ido ko!to duk sena yi maganin tsinantakar dake damunku!su kam ma da suka saka yaransu da matan su suka rena ni ina zasu ga girmana kowa yana tsula tsiyar da yake so,to bazaku kasheni ba se lokacin mutuwata ya yi ".magana take yi amma mom Rumanatu tana jiyo hucin da takeyi ta waya.
Dariya ne yaso kufcewa mom Rumanatu jin yanda Hajjatiye ta kira helicopter da anlikonta,ga kuma maganar dawuwarta da takeyi wai anki turawa a ɗaukota.bayan yau da safe aka gama waya da ita ana sanar mata kan cewa gobe jirgi zezo ya dauketa.duk yanda su Ammi suke mata ladabi da biyayya amma yanzu rikicin tsufa yasa tana cewa wai duk sun renata basa ganin girmanta.
Gyaran murya mom Rumanatu ta yi cikin kwantar da murya da ya,lallashi haɗe da girmamawa ta fara bawa Hajjatiye hakuri da kuma rarrashinta har ta samu ta shawo kanta.da kuma yi mata alkawarin gobe za'a zo a dauketa.
Kai kanta toilet ta yi,ta gasa jikinta da ruwan zafi nan taji dadi.ko lotion bata shafa ba ta saka wata karamar riga ta kwanta.
Shigowa dakin Rameesa ta yi tazo dubawa ko Sabriyah din ta dawo,ko kuwa LTG har yanzu yana rike da ita.nan ta sameta baje akan gado.
"Sabriyah yana ganki a kwance!?"ta yi mata tambaya tana shigowa dakin,dago kai tayi ta je fa mata uwar harara kafin ta bata amsa "da a tsaye kikeso ki gan ni!?"ta tambaye ta tana maida kanta ta kwanta.
Dama Rameesa dan neman magana ne yasa ta yi mata wannan tambayar,tana sanye da hijabin da ta idar da sallah isha ta zauna a gefenta.
"Tashi muje dakinmu yau a can zamu ci abinci"cewar Rameesa,tabe fuska ta yi kamar zata sa ihu ta ce"Rameesa dan Allah ki barni in huta bana jin yunwa,haba tun shigowar ki kika dameni da magana bana ciki da tambaɗa", "hhhhhhhh! Allah yabaki hakuri sarkin yaƙi"
Tana gama gaya mata haka ta fice.
Suna zaune a dinning kowa anyi saving dinsa abinci mazan sun fara ci Ammi ta ce"wai nikam ina yan mata na ne!?" "Nima abinda nake son na tambaya kenan yau tunda na dawo aiki banji ɗu riyar su ba"Saghar ya faɗa yana ajiye spoon din hannunshi.
Sahil ya ce"yau ɓarna suka je yi wa LTG shikuma ya sa su punishment,yanzu de suna part dinsu ko wacce na jinyar jikinta",anty amarya, Ammi, Hajiya babba,ummah kallon Sahil dake basu labari suke yi dan su da suke cikin gidan ma basu san anyi haka ba.
Mikewa uncle Hameed ya yi yana magana"yanzu shalelen yan matan namu LTG ka galabaitar wayyo,ko wani hali Madam Zoya take cike oho!?"dariya suka kwashe dashi harda shi uncle Hameed din da ya yi maganar sannan ya nufi part dinsa,shide LTG ko ta kansu be bi ba cikin nutsuwa yake cin abincisa.
Sahil ya sake cewa"kuma babban abin tausayin shine harda wannan Sabriyah din da ya kawo gidan nan ya saka punishment din"zaro ido waje Ammi da anty amarya sukayi sannan suka maida kallonsu kan LTG.
"Yanzu Tajuddeen har da bakuwar mun ma baka bari ba!?,ni Wallahi har kunyarta ya kamani,ka sato ta sannan kazo kana haɗa ta da kannnenka kana musu Punishment!?"ta tambayesa tana riƙe habarta.
Ɗaukar wayarsa ya yi, ya bar musu dinning table din,ya nufi part din Abbie da baya nan.
Anty amarya da Ammi ne suka shiga part din dubasu.ga kuma fatime da ta shirya musu nasu abincin ta kai musu.
Sosai Ammi ta musu faɗa akan shiga masa part binciken da sukayi domin koda basu ɗauki komai ba ze ce sun mishi ɓarna,ga shi yanzu a banza ya sa su punishment.
Haka suka je wajen Sabriyah ma nan kam sannu sukayi mata sannan anty amarya ta zauna da ita tana bata abinci abaki tun bata karba hatta soma karba,bata barta ba se da ta tabbatar da ta koshi.lokacin har karfe 9:00 saura nan ta yi mata se da safe ta fita.kwanciya Sabriyah ta yi dan bacci takeji sosai sannan ta kwanta da ya ƙinin gobe LTG ze mayar da ita Lagos.
Sergent Khalifa ne da suke cikin dajin Kano sun yi ɗauki ba da ɗi da yan ta'addan da LTG ya tura su wajensu kuma sunyi nasara,nan ya samu ya kira LTG din a waya.
Yana dakin bincike da layin wayarsu yake bibiyar yan ta'addan da kuma su major Marry,shi yake basu direction akan inda zasu je da kuma yanda zasu yi yana daga zaune akan kujera ga hot black tea a kusa dashi.
"Hello LTG, Alhamdulillah mun gama dasu sede an harbi major Marry a hannunta na dama, sannan munyi losing din sojan mu daya!".
"Na sani na turo muku helicopter,ku dawo yanzu.and what about the girl fatan basu kasheta ba!?".
LTG ya jefawa Khalifa tambaya.
"Mun samota sede bata cikin hankalinta ina tunanin ma zeye wuya in bata haukace ba sakamakon bakar fodar ibilis din da suka dinga shaƙa mata"
Jinjina kai kawai ya yi,ya kashe wayarsa.
Bari mu leka bangaren magajiya boss lady.
Tun ranar da aka sace Sabriyah da Asmita boss lady ta tayar da hankalinta,ko ina a cikin Lagos tasa a nemo mata su tunda har ita zasu iya yaudara su gudu daga gidan ba tare da ta yanta su ba amma ba'a samesu ba, domin ita gani take yi Sabriyah da Asmita guduwa sukayi daga gidan, wa'yanda akayi abun a gabansu sun yi mata bayani dallah_dallah kan cewa sace su akayi ,amma fir boss lady ta ƙi yarda da hakan, ta kudiri niyar duk sanda ta yi tozali dasu ko kuma tasa aka kamo mata su seta sa sun dandana guɗarsu.
Cele kullum se ya shigo afafa da sa ran ko ze ga Sabriyah da Asmita sun dawo,amma haka ze jisu shuru,ga anty Teema da ciwonta yanzu ya fara tashi gadan_gadan babu wanda yake zuwa dubata da taimaka mata se Nabiha da Cele,su suke kawo mata abinci da kuma magani.
Katsina state
Gidan mom Rumanatu Bishara yau zamu leka.
Babban gida ne kerarren gida wanda ya gaji da haɗuwa wato gidan minister Abu Sufyan Ubaid. Abu Sufyan ministan harkokin jiga da ficen kuɗaɗe ne,suna rayuwar farin ciki shida matarsa ɗaya se ya'yan su hudu biyu maza biyu mata.
Babban dan su shine Ashman da ya kasance babban manager a company babanshi Abu Sufyan,se Dawood shi kuma engineer ne.
Se ƙannen su mata,wanda suke saƙo da saƙo, Iftisan ce babba se yar autar su Jaleelah me shekara sha shida.
Tunda na shigo gidan na soma jin hayaniya kamar ana dambe a falo,leka kaina ciki nayi na hango wasu kyawawan yan mata guda biyu wanda kan su ɗaya kayan jikinsu kuwa dayar na sanye da jeans din wando baƙi da riga,dayar kuma doguwar riga take sanye dashi.
Dambe suke yi kamar zasu kashe junansu kuma badan komai ba se akan remote,da gudu na hango mom Rumanatu ta sauka daga downstairs tana ihun.
"Iftisan da Jaleelah bazaku bar wannan faɗan ba ko!?"karasowa cikin falon ta yi ta samu ta shiga tsakanin su ta raba faɗan, dukkansu biyu se haki suke yi suna hararan junansu.
"Mommy kin ga yanda Jaleelah take hararata ko!?, gaba-daya ta gama rena ni"Iftisan ta yi maganar tana nuna Jaleelah da yar yatsa.
"Yanzu wannan damben da ku ka za ge Kunayi kamar wasu makiyan juna duk akan menene!?"mom Rumanatu ta tambayesu tana bin ko wacce da kallo.
Cikin shagwaba Jaleelah ta ce "mommy ina zaune ne fa ina kallon cartoon shine Iftisan tazo wai sede in bata remote ta kamo mbc Bollywood shine na ƙi bata remote din,shine fa...shine fa ta fara dukana".
Kallon Iftisan din mom Rumanatu ta yi"yanzu akan wannan abin kuka tsaya faɗa,ina ce ta kan hakane ko waccen ku aka sa mata Tv a bedroom dinta!?,amma hakan be muku ba se kunzo falon downstairs kun yi mini faɗa ko!?,to bari yayanku ya dawo sena saka ya muku dan banzan duka.kuma daga yau kar wacce na sa'ke kallo a falo, da sunan tazo kallo tunda ku kamar wasu mayu kullum kuna cikin faɗa,jini daya uwarku daya ubanku ɗaya amma ko da yaushe kuna cikin faɗa kamar wasu ka ji".
"Mommy kiyi hakuri bazamu sa'ke ba!,and kiyiwa wannan fitsararriya magana ta dena mini rashin kunya na girmeta da shekara daya so am not her mate". Iftisan ta yi magana tana zazzagawa Jaleelah buhun harara kai kace idanunta zasu faɗo kasa.
Girgiza kai mom Rumanatu ta yi dan ita rikicin Iftisan da Jaleelah ya fara isarta,jira take yi Ashman ko Dawood wani ya dawo tasa su zane mata su.
Ta ce"ku bani guri ko in gwara kanku da kujerar nan"turo baki Jaleelah ta yi ido cike da hawaye ta ce"sorry mom! please karki faɗawa su ya Ashman". hararanta mom Rumanatu ta yi, sannan ta sake daka musu tsawa da gudu ko wacce ta nufi bedroom dinta.
Zama ta yi a palour tana girgiza kanta,kallon agogon dake manne a falon ta yi taga 9:50pm na dare ga shi basu dawo ba,jiransu takeyi dan tasan daga su har daddyn nasu suna tare.
Da sauri me aikinta ta shigo falon riƙe da wayar mom Rumanatu da ta barshi a bedroom dinta.
"Anty! Hajjatiye ce ke kiranki"ta faɗa tana me miƙa mata wayar,da sauri mom Rumanatu ta karba jin an ce mahaifiyar su ce kiranta.
Tana sa wayar a kunne ta ji Hajjatiye ta fashe da kuka.
Gabanta ne ya faɗi aranta ta ce "yau kuma laifin me nayiwa Hajjatiye ni Rumanatu".
Murya a sanyaye ta yi magana"assalamualaikum! Hajjatiye na Barka da wannan lokacin".
A bangaren Hajjatiye kuwa jan majina ta yi,ta ce "munafukar banza da wofi babu tsiyar tsinantakar da gaisuwar ki zata mini!ku kasheni kawai ku huta,nagaji da tsiyar tsinantakar ku bazan iya ba,baze yu ba".
Daura hannu aka mom Rumanatu ta yi jin yanda Hajjatiye ke surfa mata ruwan masifa.
Ta ce"haba Hajjatiye na, faɗamin laifin me mukayi nida su ya Mubarak din!?".
Cikin masifa Hajjatiye ta sa'ke hayayyaƙowa mom Rumanatu"bansaniba!, ni zaku mayar tsohuwar banza ko,ku ce zaku turo anlikonta ya ɗauke ni inzo Nijeriya shine zaku watsa mini ƙasa a ido ko!to duk sena yi maganin tsinantakar dake damunku!su kam ma da suka saka yaransu da matan su suka rena ni ina zasu ga girmana kowa yana tsula tsiyar da yake so,to bazaku kasheni ba se lokacin mutuwata ya yi ".magana take yi amma mom Rumanatu tana jiyo hucin da takeyi ta waya.
Dariya ne yaso kufcewa mom Rumanatu jin yanda Hajjatiye ta kira helicopter da anlikonta,ga kuma maganar dawuwarta da takeyi wai anki turawa a ɗaukota.bayan yau da safe aka gama waya da ita ana sanar mata kan cewa gobe jirgi zezo ya dauketa.duk yanda su Ammi suke mata ladabi da biyayya amma yanzu rikicin tsufa yasa tana cewa wai duk sun renata basa ganin girmanta.
Gyaran murya mom Rumanatu ta yi cikin kwantar da murya da ya,lallashi haɗe da girmamawa ta fara bawa Hajjatiye hakuri da kuma rarrashinta har ta samu ta shawo kanta.da kuma yi mata alkawarin gobe za'a zo a dauketa.