Sashe 11
Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
~And now~
*🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*
🔔 📚*JARUMAI WRITERS ASSOCIATION* 📚🖋️
Page 08
Washe gari Abbu da wuri ya shirya dan zuwa court misalin 9:00am tunani ya fara yi na ko Hajiya hurairah ta na nan ko ta yi ficewarta dan jiya bayan ya shigo yaji shigowar ta bata nemi tazo taji ko yana lafiya ba ko akasin haka ba taje ta yi uzurin ta,shisa shima daya gama shirya wa ya fito be ko kalli inda dakinta yake ba yabar part din. me aiki ya gani tana kokarin shiga ta yi musu gyare_gyare nan ne ya tambaye ta ko taga Hajiya hurairah ta amsa mishi da"yau Hajiya da wuri ta fita tun asuba naga fitar ta"gyada mata kai kawai ya yi yasa kai ya wuce yana hasaso irin kwakkwaran matakin da ze dauka akan Hajiya hurairah domin abin nata yafara wuce gona da iri.
BORNO STATE HIGH COURT
" Ya me girma me Shari'a wanda nake karewa malam isah gwani ya kama abokinshi wato labaran sha'ibu yana kokarin yin lalata da matarsa Hajara , yana kokarin keta mata haddinta amatsayinta ta matar aure kuma mace , malam isah gwani yasan wannan kotu me adalci ne za'a bi musu hakkin shi ,shida matarsa Hajara shisa yakawo wannan ƙaran nan . ya me girma me Shari'a da wannan nake rokon kotu tabi musu hakkinsu , kuma labaran sha'ibu yakarbi hukunci dede da abinda ya shuka Nagode"
Lauyan na gama fadin haka cikin girmamawa dakuma sanin aikinshi yasamu guri ya zauna.
Yar rubuce rubuce alƙali Isma'il Bishara ( Abbu) ya yi idonshi manne da farin glass.
Karewa kotun kallo nayi nan na sake fahimtar babban kotu ne ga al'umma a cike maƙil da kotun kowa ya yi shuru ya ka sa kunne ana sauraran wannan shari'ar , dakuma son jin hukuncin da alƙali ze yankewa mai laifin duk sun matsu suji .
Ɗago kai alƙali ya yi bayan yagama rubuce rubuce ya ce
" Kotu ta yankewa labaran sha'ibu hukuncin bulala 100 abisa kokarin yin zina da matar aure tare da cin taransa na dubu ɗari sannan kuma ze bawa malam isah gwani da matarsa hakuri."
Yana kammala fadin haka ya buga guduma
Aka amsa da " kotuuuuuuuuu"
Mikewa ya yi polisawa da lawyer's suka bi bayanashi domin takewa babban alƙali baya har packing space din kotun bude mishi motar jami'an tsaron sukayi ya shiga , motoci goma ne suka fita a kotun don zuwa gidan Bishara .
Kowa dake cikin kotun se alhamdulillah sukeyi da hukuncin da aka yankewa labaran saboda irinsu ne maciya amana da koda anbasu amana zasuci tunda ga shi yaje yana kokarin keta haddin matar abokinsa , hakan ya zama izina ga yan baya.wa'yannan sune mutanen da zaka nemi Allah yarabaka dasu domin ba abokan zama bane .
BISHARA'S FAMILY
Motacin da suka rako alƙali suna gama shigowa motar Hajiya hurairah yashigo Packing ta yi ta fito tunda tafito Abbu yake kallonta ranshi na ƙuna saboda tafita batare da izininshi ba duk da ba yau ta fara ba , ganin yana jefa mata harara yasa ta dauke kanta kamar bata ganshi ba ta wuce ta gabansu kanta asama , mansion din ta shiga ta ƙare mishi kallo ajiyar zuciya ta sauke ganin yaranta suna zaune suna kallon Tv a main part din dan rabonta dasu tun asubahi data fita agidan part dinsu ta nufa hankalinta kwance bata damu da tambayoyin da Abbu ze mata ba domin kuwa tana dede dashi har ta yi nisa a haura steps taji an dafa kafaɗarta juyawa ta yi dan ganin waye haka .
Murmushi suka sakarwa juna lokaci da ta juyo jan hannunta Hajiya hurairah ta yi zuwa part din.
Tana shiga suka tafa hade da yin shewa zama sukayi abakin gado .
Hajiya khareema ta ce " aminiyata faɗamin ya ake ciki ya kukayi da boka mauzau , shafamin inji nakosa "
Dariya Hajiya hurairah ta yi ta bude hadadden handbag dinta tafara fito da kayan tsubbun da boka mauzau yabatasu masu yawa sosai daga kan layoyi dakuma wasu abubuwa akulle a ledoji.
Wata bak'ar leda ta dauko yana ƙunshe da wani maganin tsubbun aciki. ta kalli Hajiya khareema ta kashe mata ido ta ce
" Yau din nan jinakeyi nafi kowa farin ciki , kinga nan da gobe zuwa jibi ? to labarin yarinyar da take kokarin bata miki aiki yakare batt zasu nemeta su rasa na tsawon har abada"
" Heeeee kai kawata inaji dake wallahi shisa nadauki ragamar wannan aikin nabaki shi a hannun ki kafin a zo mataki na biyu" cewar Hajiya khareema tana bata hannu suka tafa , ci gaba da magana Hajiya hurairah ta yi.
" Wannan maganin da kike gani acikin bakin ledar nan shine za ki san hanyar da za'ayi asashi a abincin gidan nan gabaki daya kowa yaci harta masu aiki, jami'ai, masu gadi da kuma mutanen gidan! daga zaran sunci abincin nan dake dauke da wannan maganin tofa sufa labarin su yakai monday domin bacci zasuyi sosai yanda har a shigo adauke Asrah aje akasheta ma bazasu taba sani ba se safiyar washe gari .
Maganin zesasu ne suyi dogon bacci me nauyin gaske , rikeshi a hannunki"
Ta faɗa tana miƙa mata sa hannu Hajiya khareema ta yi ta karbe shi tana jinjina kai cike da farin ciki.
" sekuma wannan layar kinganshi nan ? acikin gidan nan za ki binne shi , tayanda ze hanasu yunkurin neman yarinyar sannan kuma zasu manta da ita na har abada ke in taƙaice miki ma babu wanda ze sake koda ambatan sunan Asrah "
Jinjina mata ta yi da babban yatsar hannunta kafin Hajiya khareema ta ce..
" gaskiya hurairah kedin fa bata wasa bace , shin boka mauzau yabaki wanda yarinyar zata manta komai nata harta sunanta ?" " Eh yabani ga shi nan ma " tafada tana fito dashi acikin jaka, kamar ruwan turare yake ɗan kaɗan a kwalba gyara zama Hajiya hurairah ta yi ta soma magana " kinga wannan kuma kadan za'a saka acikin hanky se a shaƙa mata a hancinta daga zaran ta shakeshi tofa ko kanta bazata sake tunawa ba daga nan ma mutuwa zatayi saboda duk wanda ya shaƙi wannan turaren shida sake rayuwa kuma se wani ikon Allah"
Ajiyar zuciya Hajiya khareema ta sauke sannan ta sa hannu ta kwashi kayan tsubbun nasu ta saka acikin yar handbag dinta ta kalli Hajiya hurairah ɗakyau ta ce" kinyi mini kokari sosai kawata , kuma in sha Allah zan cika miki burinki na mallakar dukiyar wannan ahalin gaba daya , yanzu bari in wuce in tafi in samu in adana wa'yannan kayan kar mijinki Abbu ya shigo yasamemu " tana magana tana tafiya da sauri_sauri dan batason su hadu da Abbu a hanya saboda ta lura kamar yafara zarginsu , bin bayanta ta yi saboda tarakata , sosai suke murna yau ce rana ta farko da zasu fara cin nasara akan wannan family din.
Bata koma ciki ba har se da taga Hajiya khareema ta bace mata da kallo kokarin komawa takeyi idonta yasauka akan Abbu da yake daff da shigowa daure fuska ta yi itama sannan takoma ciki ta tsaya , yana shigowa babu abinda ya ce mata fa ce zaman da ya yi akan manya_manyan kujerun da suka zagaye falon nasu , ganin bece mata komai bane yasa ta shiga kitchen ta dauko mishi ruwa me sanyi ta kawo mishi sannan ta tsiyaya a glass cup.
Abbu de da ido kawai yake binta takaicinta ma ya hanashi magana saboda Hajiya hurairah kamar ba zaman aure sukeyi dashi ba duk sanda ta yi niyar fita ,fita takeyi abinta ako wani irin lokaci kuma tadawo aduk sanda ta yi niya abin na matukar kona mishi rai , aduk sanda ta fita se ya mata faɗa daga karshe yakara mata da nasiha kullum cikin cewa take bazata karaba.
Daukan glass cup din ruwan Abbu ya yi yasha ya ajiye duk tana zaune a kujera me zaman banza tana kallonshi.
Rike haɓa Abbu ya yi ya ce" Hurairah Ina kikaje yau tunda asuba kika fita ?"
Ɗan nisawa ta yi tana tuno me za ta faɗa mishi can wani tunani ya faɗo mata a rai . " Abbu ina wannan ƙawar tawa rukayya? to ita ce mamar ta ba lafiya shine ta ƙirani mukaita asibiti" girgiza kai Abbu ya yi saboda ko kaɗan be yarda da wannan maganar na taba ,dama ita inde tafita bata rasa abin faɗa uzuri kala_kala kullum da irin karyar da take mishi , mikewa ya yi yana cire babbar rigar jikinshi yarike a hannu ya ce " nasha faɗa miki na tsani irin wannan fitan hurairah ko kadan banaso amma , bazakisan banaso ba sena dau mataki akai " yawuce yabarta awajen zaune. tabe baki ta yi sannan ta fito daga part din nasu zuwa can main part din gidan ta nufa saboda kiran yaranta Sudais da Saghar da kuma yara matan ta.
(wlh mata da yawa ba su dauki irin wannan fitan abakin komai ba zakaga mace ta fita aduk lokacin da take so batare da izinin mijinta ba.wata kam ma jira take yi yasa ƙafa ya fita yana sa kafa ya fita itama zata bazama nata wajen,bayan kuma hakan da mata keyi kwasarwa kanmu zunubi mukeyi duk taku daya da za ki taka Mala'ikun Allah na tsinuwa ne gareki.shin menene ribar haka kina saɓawa mahaliccinki, babban abinda yake kashe aure kenan saboda babu abinda maza suka tsana sama da irin haka musamman ma su dawo gida suna tsammanin zasu tarar da matan su agida amma ah ah bakya nan kuma fitan naki bawai da izinin shi ba hakan ne ze tunzurshi yasa ku fara samun saɓani,ba ma wannan ba wasu matan basa tunanin tsautsayi kin fita batare da sanin mijinki ba ƙila ma yace miki karki fita kika ƙi jin maganar shi wani tsautsayin ya rifta wa gari ya waya?Allah yasa mu dace ya bamu ikon gyarawa Allah yasa a fahimci wannan kuskure ne.)
*🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*
🔔 📚*JARUMAI WRITERS ASSOCIATION* 📚🖋️
Page 08
Washe gari Abbu da wuri ya shirya dan zuwa court misalin 9:00am tunani ya fara yi na ko Hajiya hurairah ta na nan ko ta yi ficewarta dan jiya bayan ya shigo yaji shigowar ta bata nemi tazo taji ko yana lafiya ba ko akasin haka ba taje ta yi uzurin ta,shisa shima daya gama shirya wa ya fito be ko kalli inda dakinta yake ba yabar part din. me aiki ya gani tana kokarin shiga ta yi musu gyare_gyare nan ne ya tambaye ta ko taga Hajiya hurairah ta amsa mishi da"yau Hajiya da wuri ta fita tun asuba naga fitar ta"gyada mata kai kawai ya yi yasa kai ya wuce yana hasaso irin kwakkwaran matakin da ze dauka akan Hajiya hurairah domin abin nata yafara wuce gona da iri.
BORNO STATE HIGH COURT
" Ya me girma me Shari'a wanda nake karewa malam isah gwani ya kama abokinshi wato labaran sha'ibu yana kokarin yin lalata da matarsa Hajara , yana kokarin keta mata haddinta amatsayinta ta matar aure kuma mace , malam isah gwani yasan wannan kotu me adalci ne za'a bi musu hakkin shi ,shida matarsa Hajara shisa yakawo wannan ƙaran nan . ya me girma me Shari'a da wannan nake rokon kotu tabi musu hakkinsu , kuma labaran sha'ibu yakarbi hukunci dede da abinda ya shuka Nagode"
Lauyan na gama fadin haka cikin girmamawa dakuma sanin aikinshi yasamu guri ya zauna.
Yar rubuce rubuce alƙali Isma'il Bishara ( Abbu) ya yi idonshi manne da farin glass.
Karewa kotun kallo nayi nan na sake fahimtar babban kotu ne ga al'umma a cike maƙil da kotun kowa ya yi shuru ya ka sa kunne ana sauraran wannan shari'ar , dakuma son jin hukuncin da alƙali ze yankewa mai laifin duk sun matsu suji .
Ɗago kai alƙali ya yi bayan yagama rubuce rubuce ya ce
" Kotu ta yankewa labaran sha'ibu hukuncin bulala 100 abisa kokarin yin zina da matar aure tare da cin taransa na dubu ɗari sannan kuma ze bawa malam isah gwani da matarsa hakuri."
Yana kammala fadin haka ya buga guduma
Aka amsa da " kotuuuuuuuuu"
Mikewa ya yi polisawa da lawyer's suka bi bayanashi domin takewa babban alƙali baya har packing space din kotun bude mishi motar jami'an tsaron sukayi ya shiga , motoci goma ne suka fita a kotun don zuwa gidan Bishara .
Kowa dake cikin kotun se alhamdulillah sukeyi da hukuncin da aka yankewa labaran saboda irinsu ne maciya amana da koda anbasu amana zasuci tunda ga shi yaje yana kokarin keta haddin matar abokinsa , hakan ya zama izina ga yan baya.wa'yannan sune mutanen da zaka nemi Allah yarabaka dasu domin ba abokan zama bane .
BISHARA'S FAMILY
Motacin da suka rako alƙali suna gama shigowa motar Hajiya hurairah yashigo Packing ta yi ta fito tunda tafito Abbu yake kallonta ranshi na ƙuna saboda tafita batare da izininshi ba duk da ba yau ta fara ba , ganin yana jefa mata harara yasa ta dauke kanta kamar bata ganshi ba ta wuce ta gabansu kanta asama , mansion din ta shiga ta ƙare mishi kallo ajiyar zuciya ta sauke ganin yaranta suna zaune suna kallon Tv a main part din dan rabonta dasu tun asubahi data fita agidan part dinsu ta nufa hankalinta kwance bata damu da tambayoyin da Abbu ze mata ba domin kuwa tana dede dashi har ta yi nisa a haura steps taji an dafa kafaɗarta juyawa ta yi dan ganin waye haka .
Murmushi suka sakarwa juna lokaci da ta juyo jan hannunta Hajiya hurairah ta yi zuwa part din.
Tana shiga suka tafa hade da yin shewa zama sukayi abakin gado .
Hajiya khareema ta ce " aminiyata faɗamin ya ake ciki ya kukayi da boka mauzau , shafamin inji nakosa "
Dariya Hajiya hurairah ta yi ta bude hadadden handbag dinta tafara fito da kayan tsubbun da boka mauzau yabatasu masu yawa sosai daga kan layoyi dakuma wasu abubuwa akulle a ledoji.
Wata bak'ar leda ta dauko yana ƙunshe da wani maganin tsubbun aciki. ta kalli Hajiya khareema ta kashe mata ido ta ce
" Yau din nan jinakeyi nafi kowa farin ciki , kinga nan da gobe zuwa jibi ? to labarin yarinyar da take kokarin bata miki aiki yakare batt zasu nemeta su rasa na tsawon har abada"
" Heeeee kai kawata inaji dake wallahi shisa nadauki ragamar wannan aikin nabaki shi a hannun ki kafin a zo mataki na biyu" cewar Hajiya khareema tana bata hannu suka tafa , ci gaba da magana Hajiya hurairah ta yi.
" Wannan maganin da kike gani acikin bakin ledar nan shine za ki san hanyar da za'ayi asashi a abincin gidan nan gabaki daya kowa yaci harta masu aiki, jami'ai, masu gadi da kuma mutanen gidan! daga zaran sunci abincin nan dake dauke da wannan maganin tofa sufa labarin su yakai monday domin bacci zasuyi sosai yanda har a shigo adauke Asrah aje akasheta ma bazasu taba sani ba se safiyar washe gari .
Maganin zesasu ne suyi dogon bacci me nauyin gaske , rikeshi a hannunki"
Ta faɗa tana miƙa mata sa hannu Hajiya khareema ta yi ta karbe shi tana jinjina kai cike da farin ciki.
" sekuma wannan layar kinganshi nan ? acikin gidan nan za ki binne shi , tayanda ze hanasu yunkurin neman yarinyar sannan kuma zasu manta da ita na har abada ke in taƙaice miki ma babu wanda ze sake koda ambatan sunan Asrah "
Jinjina mata ta yi da babban yatsar hannunta kafin Hajiya khareema ta ce..
" gaskiya hurairah kedin fa bata wasa bace , shin boka mauzau yabaki wanda yarinyar zata manta komai nata harta sunanta ?" " Eh yabani ga shi nan ma " tafada tana fito dashi acikin jaka, kamar ruwan turare yake ɗan kaɗan a kwalba gyara zama Hajiya hurairah ta yi ta soma magana " kinga wannan kuma kadan za'a saka acikin hanky se a shaƙa mata a hancinta daga zaran ta shakeshi tofa ko kanta bazata sake tunawa ba daga nan ma mutuwa zatayi saboda duk wanda ya shaƙi wannan turaren shida sake rayuwa kuma se wani ikon Allah"
Ajiyar zuciya Hajiya khareema ta sauke sannan ta sa hannu ta kwashi kayan tsubbun nasu ta saka acikin yar handbag dinta ta kalli Hajiya hurairah ɗakyau ta ce" kinyi mini kokari sosai kawata , kuma in sha Allah zan cika miki burinki na mallakar dukiyar wannan ahalin gaba daya , yanzu bari in wuce in tafi in samu in adana wa'yannan kayan kar mijinki Abbu ya shigo yasamemu " tana magana tana tafiya da sauri_sauri dan batason su hadu da Abbu a hanya saboda ta lura kamar yafara zarginsu , bin bayanta ta yi saboda tarakata , sosai suke murna yau ce rana ta farko da zasu fara cin nasara akan wannan family din.
Bata koma ciki ba har se da taga Hajiya khareema ta bace mata da kallo kokarin komawa takeyi idonta yasauka akan Abbu da yake daff da shigowa daure fuska ta yi itama sannan takoma ciki ta tsaya , yana shigowa babu abinda ya ce mata fa ce zaman da ya yi akan manya_manyan kujerun da suka zagaye falon nasu , ganin bece mata komai bane yasa ta shiga kitchen ta dauko mishi ruwa me sanyi ta kawo mishi sannan ta tsiyaya a glass cup.
Abbu de da ido kawai yake binta takaicinta ma ya hanashi magana saboda Hajiya hurairah kamar ba zaman aure sukeyi dashi ba duk sanda ta yi niyar fita ,fita takeyi abinta ako wani irin lokaci kuma tadawo aduk sanda ta yi niya abin na matukar kona mishi rai , aduk sanda ta fita se ya mata faɗa daga karshe yakara mata da nasiha kullum cikin cewa take bazata karaba.
Daukan glass cup din ruwan Abbu ya yi yasha ya ajiye duk tana zaune a kujera me zaman banza tana kallonshi.
Rike haɓa Abbu ya yi ya ce" Hurairah Ina kikaje yau tunda asuba kika fita ?"
Ɗan nisawa ta yi tana tuno me za ta faɗa mishi can wani tunani ya faɗo mata a rai . " Abbu ina wannan ƙawar tawa rukayya? to ita ce mamar ta ba lafiya shine ta ƙirani mukaita asibiti" girgiza kai Abbu ya yi saboda ko kaɗan be yarda da wannan maganar na taba ,dama ita inde tafita bata rasa abin faɗa uzuri kala_kala kullum da irin karyar da take mishi , mikewa ya yi yana cire babbar rigar jikinshi yarike a hannu ya ce " nasha faɗa miki na tsani irin wannan fitan hurairah ko kadan banaso amma , bazakisan banaso ba sena dau mataki akai " yawuce yabarta awajen zaune. tabe baki ta yi sannan ta fito daga part din nasu zuwa can main part din gidan ta nufa saboda kiran yaranta Sudais da Saghar da kuma yara matan ta.
(wlh mata da yawa ba su dauki irin wannan fitan abakin komai ba zakaga mace ta fita aduk lokacin da take so batare da izinin mijinta ba.wata kam ma jira take yi yasa ƙafa ya fita yana sa kafa ya fita itama zata bazama nata wajen,bayan kuma hakan da mata keyi kwasarwa kanmu zunubi mukeyi duk taku daya da za ki taka Mala'ikun Allah na tsinuwa ne gareki.shin menene ribar haka kina saɓawa mahaliccinki, babban abinda yake kashe aure kenan saboda babu abinda maza suka tsana sama da irin haka musamman ma su dawo gida suna tsammanin zasu tarar da matan su agida amma ah ah bakya nan kuma fitan naki bawai da izinin shi ba hakan ne ze tunzurshi yasa ku fara samun saɓani,ba ma wannan ba wasu matan basa tunanin tsautsayi kin fita batare da sanin mijinki ba ƙila ma yace miki karki fita kika ƙi jin maganar shi wani tsautsayin ya rifta wa gari ya waya?Allah yasa mu dace ya bamu ikon gyarawa Allah yasa a fahimci wannan kuskure ne.)