← Book details Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 60

Sashe 53

Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan wata daya, abubuwa da dama sun faru,mom Rumanatu ita da yaranta sun koma katsina.an sallamo Asmita daga asibiti jikinta ya yi sauki,har ta fara maida kibanta,sunci gaba da zuwa makaranta tare da Sabriyah sun yi kyau sosai sunyi fresh sun zama yan gida su ma,duk abinda za'a yiwa su Rameesa tare ake yi musu.kullum se ta yi waya da Fu'ad idan ta tabbatar da kowa ya yi bacci,duk da ta rage alwashin da ta dauka akan LTG domin taga duk tunaninta, LTG ya take ta ya shanye,ita yanzu tsoro ma yake bata,wani abun kamar akan idonshi takeyi hakan yasa ta watsar da mukaman ta,duk da haka Fu'ad be dena in gizata ba.duk da yaga yanzu ita ta karaya.wannan dalilin yasa ya sake sabon mugun shiri.
Daga LTG, Sudais, ACP Jawan duk busy ya musu yawa kullum karfe shida na safiya suke fita,su dawo tara ko goma LTG kam yana kaiwa har karfe daya wata rana ma baya kwana a gidan.aiki ya sha musu kai suna nan suna dakon shugaban kungiyar Italian Mafia,domin any moment ze iya yin abinda yace ze aikata.

Wannan dalilin ne yasa rabon da Sabriyah tasa LTG a idonta hatta manta domin yakai kusan sati biyu rabon da taga ko da gilmawarsa,sede tana yawan ganin major Marry.

Yau Friday tun 12:00 aka tashe su daga makaranta driver yazo ya maida su gida.suna shiga suka ga samarin gidan gaba daya cikin fararen shadda ɗinkin half jumfa bakaramin kyau sukayi ba,sun shirya zuwa masallaci tare da su Abbie da Abbu, uncle Hameed,suna zaune da alama akwai wanda suke jira ya fito.
Tunda suka shigo cikin falon Saghar da Asmita suke satan kallon junansu.uniform din jikinta da ta saka ne yau yasa ya ji kishi yakamasa ransa ya ɓaci ya rasa dalilin da yasa ranshi yabaci dan yaga Asmita da uniform din bayan kuma Sabriyah ma shine a jikinta amma be ji hakan ba,kuma su Rameesa ma makarantar sukayi amma be taɓa jin akwai wani abu dangane da uniform din ba se yau da ya gani a jikin Asmita.
Riga da wandon spot Wear ne wandon yana da fa ɗi,haka rigar ma yana da girma kadan da kauri,irin kayan yan kwallo,sun saka baby hijab.ga school back din su dake rataye a kafadarsu.
Kauda idonsa ya yi daga kanta ya fuske kamar be ganta ba.

Shigowa sukayi wajen su, suka gaishe su cikin girmamawa.

Murmushi Abbie ya yi "sannunku da dawuwa yan boko,kun sha gajiya kam"su ma murmushin suka yi, Asmita ta ce "Abbie ai ba wahala,kawai de zama"dariya sukayi.
ACP Jawan ya ce "to ai babu maraban dambe da faɗa" "tom wannan waya gaya maka Hausa ya ishe ta ɓalle ta san me kake nufi"cikin zolaya Sudais ya faɗi haka.

Shagwabe fuska ta yi "Abbie ka ga ya Sudais ko!?" "Kyaleshi kishi yake yi dan kina zuwa makaranta shi baya zuwa".dariya Sabriyah ta yi jin shirmen Asmita.ga Abbie ma da ya biye mata.

Duk yanda tasan zata yi Saghar ya kalleta ko za ta samu nutsuwa amma abun ya ƙi,tunda ya sunkuyar da kansa kasa yafara danna wayarsa be sa'ke dagowa ba.

Fitowa ya yi falon yana sanye cikin farar danyen shadda half jumfa ,me tsadar gaske,an yi mishi aiki na alfarma,yana sanye da bak'ar takalmi,ga Rolex wrist watch daure a hannunsa.kan sa babu hula se gyararren bakin sumar kanshi da yasha gyara yana sheki da daukar ido.ga baƙin tsadadden sun glass manne a fuskarsa,ya ƙara ƙawatar da fuskar.
Ya yi kyau sosai me matukar nutsuwa da daukan hankali,duk yanda ka kai ga kamewa,idan ka masa kallo ɗaya se ka ji sha'awar sa'ke daura ido a kan sa,ga daddadar Kamshin turaren dake tashi a jikinsa.
Tunda ya shigo falon Sabriyah ta kasa dauke ido akansa,bata taɓa ganin sa da manyan kaya ba se yau,se ta ga manyan kayan ma sunfi mishi kyau da karban sa.

"Tajuddeen manyan kaya suna maka kyau sede bakason sawa"Abbie ya faɗa yana dafa shi.
Kallon Abbie ya yi be ce komai.

Haɗa ido ya yi da Sabriyah dake satan kallon sa, harara ya watsa mata.
Tabe baki ta yi,magana kawai ta yi.ba tare da kowa ya ji ba iya labban bakinta ne yake motsawa yanda iya LTG ne ze ganta ta ce.
"Ko kyau bakayi ba,ka dena wani yanga,kanajin kanka na wani girma".

Hannunsa yasaka a wuyansa ya mata alamar se na yanka ki.

Dariya ma yabata.yanda ya mata alama da ze yankata ne abin yasata dariya.

Tana dariya ta ce"to se kun dawo Allah ya kiyaye hanya, Abbie, Abbu, daddy,amana addu'a " "in sha Allah "suna bata amsa ta haura part din su Asmita ma tabi bayan ta.

Abbie da Sudais su kadai ne suka lura da abinda LTG da Sabriyah sukayi,su kansu abin nasu ma dariya ya basu, wato tsakanin LTG da Sabriyah babu shiri.
Ko wannensu motarsa ya shiga driver yaja su , sojoji da kuma da polisawa da securities ne suka musu taki har masallacin.

Suna shiga dakinsu suka tarar da su parsa a ciki,suna taɗi, hiran wani saurayin da Zoya ta yi jiya sukeyi,suna dariya.

Ɗago kai sukayi dukkansu, dama zaman jiran dawuwar su, sukeyi su basu labari.

Cikin dariyar mugunta Rameesa ta soma cewa "gwara da Allah yasa kuka dawo yanzu" cire hijab din kanta Sabriyah ta yi,dama bata saka hula ta ciki ba gashin kanta baki wuluk na daure da ribbom babba ja.
Ta ce"ai ke Rameesa in an ga kina irin wannan yar iskar dariyar taki tofa abun mugunta ne ya samu"sa'ke tuntsirewa ta yi da dariya.
"Dadina da ke Sabriyah akwai ki da gane abu.kinsan jiya Zoya da iklas sun je gidan ya Abbas,to wai su iyayen kinibibi suka fita siyan abu waje,a hanyar dawuwar su ne suka haɗu da wani wai yana son Zoya.nan ya fara cika su da surutu kamar wani aku.Sau uku suna ce mishi zasu tafi amma yana dakatar dasu,har ya kure hakurin Zoya,kin san mutumiyar taki,nan fa ta mishi tas bata raga masa ba!"dariya Asmita da Sabriyah suka kwashe harda tafawa.

Asmita dake cire safar ƙafarta ta ce"haba ke kuwa Zoya,kin yi saurayi amma shine zaki kora shi da masifarki".galla mata harara ta yi,"ku fa baku da hankali. dan de baku gansa bane Wallahi kamar wani ɗan shaye_shaye".

Haka suka ta hirarsu,suna shan dariya, Zoya har kwatanta musu yanda saurayin yake magana yana wani buɗe ƙafadata kamar wani boss take yi,su kuma suna kallonta kamar sun samu Tv suna dariya.

Daga masallaci ACP Jawan station ya wuce saboda kiran da DPO yake masa ya wuce misali.jikinsa ne ya bashi akwai abinda yake faruwa,shisa ana idar da sallah ya wuce direct station.
Yana shiga yaga yan sanda se shige da fice suke yi.
Yana shigowa suka sara mishi.
Office dinsa ya wuce ya samu waje ya zauna.shigowa DPO ya yi da tarin files a hannunsa da a ƙalla zasu kai guda goma zuwa sha wani abu.

Sara mishi DPO ya yi kafin ya fara magana "ACP!yau tunda garin Allah ya waye muke ta karban cases din kidnapping,i zuwa yanzu an yi kidnapping mutane sama da goma.shisa nake ta kiran ka,this is getting out of hand ACP".Shuru Jawan ya yi yana wani tunani,inde tunanin sa ya bashi dede to wannan aikin Italian Mafia ne.

Kallon DPO,ACP Jawan ya yi kafin ya ce"have a sit"zama ya yi yana"thank you sir ".

Danna kira ACP Jawan ya yi ya kira, commissioner a waya suka yi magana ya sanar dashi halin da ake ciki.

Suna cikin yin magana,wata mata ta shigo station din tana kuka haɗe da kururuwa.ta cika station din da kuka.

Tambayarta kurtun yan sandan sukayi nan take sanar musu da yaranta mata guda biyu da ta mallaka a duniya an yi garkuwa dasu.

Da sauri wani dan sanda ya shigo office din ya sanar dasu.

Fitowa suka yi ACP Jawan ya taimakawa yar dattijuwar ta mike ya zaunar da ita akan kujera yana lallashinta,da bata karfin guiwar cewa da yardar Ubangiji za'a ga yaranta.

*🌹🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹🌹*

Page 28,29,&30

*_Story & written_*

By

*MRS🌹ISHAM🌹*
( Yar lelen Jarumai)

📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️

Three in one
Page 28,29&30

Rubuta report matar ta yi sannan ACP Jawan ya bada umarni aka mayar da ita har gidan ta.

Da haka shima ya koma gida bayan yasa yan sanda sun fara binciken yaran da aka sace.
Karfe 5:00 dede ya iso gida polisawa suka bude masa kofa,yana fitowa suka sara mishi fara tafiya ya yi suka yi kokarin mara masa baya hannu kawai ya daga musu, dakatawa sukayi suna "Yes sir".

Ko part din sa be shiga ba ya wuce na LTG nan ya samu baya nan,ga shi tun yana office ya ke kiransa be yi picking ba,dama LTG haka yake in ba wai shi ya kiraka ba tofa in ka kirasa ma,abanza domin baya daga kira se in ya zama urgent and important.

Koma wa nashi part din ya yi,wanka ya fara yi sannan ya sauya zuwa ƙananan kaya. ACP Jawan da LTG suna tsananin kama da juna sede abinda ya bambanta su shine, kwayar idonsu ya sha bambam dana juna LTG nasa golding eye balls wato Hazel eye balls,which is the combination of green, brown,gold.yake dashi wanda ya gado a wajen kakar su Ammi da anty amarya,hatta farinsa ma irin na turawa ne da kuma sumar kanshi,while ACP Jawan nashi kwarya idon sa brown ne shida Umaisha.
Chapter 53 · 0% Book details