← Book details Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 60

Sashe 34

Ashe Zamuga Juna Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Dariya sukayi banda Zoya da ko kallonta batayi ba, hasalima haushi ta ji da taga yanda Umaisha suke janta da zolaya.
Parsa ne ta miƙe ta bisu a baya ta ce"nide Wallahi sena biku". kallonta kawai Sabriyah ta yi taga tana mata murmushi, itama murmushin ta mayar mata.
Sannan suka fice garden suka nufa tun daga nesa suka hango LTG zaune akan kujerun da suke cikin garden din yana sanye da army trouser se rigar t-shirt me budeden gaba, sojoji kuma na zagaye dashi ta ko ina,ga wasu maza guda biyu da aka musu daurin huhun goro da igiya zaune akasa.
Karasowa wajan sukayi major Marry ta jawa Sabriyah kujera ta zauna.

"Ya Taj ashe kana nan dazun muka ta neman ka bamu ganka ba"ta yi maganar tana shagwabe fuska.

Wayarsa yake dannawa cikin kwanciyar hankali tunda suka iso wajen be ko daga kai ba.

With his sexy voice ya ce"yeap am here do you need anything?"
Cikin jin dadi Parsa ta ce "yes!Muna son muje mu siya ice cream, chocolate and some yogurt".
Yanda take lissafin ne ya bawa major Marry dariya...ita de Sabriyah da ido kawai take binsu.

"Give her the ATM"cewar LTG,fito da ATM da suka kusa takwas major Marry ta yi ta mikawa Parsa guda daya.

Tsalle ta yi tana"thank you sweet bro".da gudu tabar garden din,dan taje ta bawa su Umaisha labari.yau ai tunda ATM ya shiga hannunsu se abinda hali ya yi.

Ajiye wayar hannunsa ya yi,ya ɗan kalli wa'yannan mazan da suke daure da igiya, "kun san wannan!?"ya faɗa yana nuna musu Sabriyah da ido,a galabaice daya daga cikinsu ya ce "ah ah Wallahi bamu santa ba".

Gyada kai ya yi "ke kin san su?"harara ta watsu musu ta ce "Ni ban san su ba."

"Shikenan!amma shi ogansu ai kin sanshi tunda har kukayi kwanaki goma a hotel,yanzu ina so ki sanar dani aina zan sameshi!?"tunda ta ji ya ambaci tayi kwanaki goma a Hotel da wani ta gane magana yake yi akan Fu'ad.

baƙi ta buɗe da niyar zata yi magana ta ji ana mata rada a kunne,kuma ba muryar kowa bane, fa ce na Fu'ad"my Sabriyah dan Allah karki nuna musu kan cewa kin san ni,nemana suke yi,ruwa a jallo,saboda su kasheni,babu abinda na musu kawai zalunci ne irin na soja.ki taimaki rayuwata dan Allah Sabriyah"
Shuru ne ya biyo baya hankalinta ya yi gaba wajen sauraran abinda Fu'ad yake ce mata,a dayan bangaren kuwa tana mamakin taya hakan ya kasance amma wannan ba shi bane damuwarta,abinda yafi damunta jin wai nemansa suke yi su kasheshi,hakan ne ya tayar mata da hankali, tambayar kanta takeyi,shin menene abinda Fu'ad ya musu,bawan Allah da Babu ruwansa,kamilin mutum me kyautatawa mutane.
Wannan dalilin ne yasa tasa aranta ko da kasheta zasu yi ba zasu taɓa jin wani abu dangane da Fu'ad a bakinta ba.

Ganin ta yi shuru ta faɗa duniyar tunani ne yasa LTG ya da ki table din gabansun da karfi,har seda ta firgita tana kokarin mikewa.

"Zauna"
Ya yi maganar fuskarsa kamar hadari.
"Inajinki"
Cikin inda_inda ta soma magana"ni ban san akan waye kake wa'yannan maganganun ba,ka kyaleni in je in nemo yar uwata'".ta karisa maganar idonta na ciki da hawaye.
LTG dama yasan za'a rina saboda shugaban kungiyar Italian Mafia ba karamin shu'umin mutum bane zeyi fiye da haka ma.yasan ko shekara daya zasu yi yana tambayarta game da shi bazata taɓa faɗa masa komai akan sa ba,kamar yadda shugaban Italian Mafia ya yi blackmailing din ta shima dole ne ya yi blackmailing dinta saboda ta wannan hanyar ne kawai ze samu ta yi magana, saboda shugaban Italian Mafia yana kokarin juya mata tunaninta ne da karfin sihirinsa..

Kallon major Marry ya yi ya mata alamar da ta komar da ita ciki.

"Okay"

marairace fuska Sabriyah ta yi "dan Allah ka taimakeni ka mayar dani inda ka dauko ni,sun sace mini yar uwata' akan wani abun da baya wajen ta yana wajena,sun saceta bansan a wani hali take ba".tana magana hawaye na zubowa daga idanunta.

maida kallonsa kanta yayi,jin abinda ta faɗa. yana me son gasgatar da hasashen da ya keyi game da abinda Sabriyah ta ke magana yana wajenta,fatan shi ɗaya shine Allah yasa wannan ma'adanar memory card din ne a wajenta.

"Akan me kike magana meye a wajen naki!?"ya faɗa yana tsare ta da mayun idanunsa,ka war da kanta gefe tayi saboda bazata iya kallon cikin kwayar idanunsa ba,ji ta keyi kamar akwai guba me zautar da mutum acikin idanun nasa.wannan dalilin yasa ko da yaushe take avoiding din haɗa ido dashi.

"Am......amm......dama wani Barrister Lameer ne ya bawa Asmita ma'adanar memory kan cewa ko ta wani hali mu tabbatar da mun miƙa wannan abun wajen hukuma,ita kuma ta bani.shine suka kashe Barrister Lameer din,suka biyo mu har gida aka sace Asmita".

Zuba mata ido kawai ya yi,yana sauraranta,lumshe kyawawan idonsa ya yi ganin ya samo abinda suke nema har gida,domin lokacin da suka jefo da Barrister Lameer kan titi yayi dede da i sowarsu wajan nan suka fara ɓarin wuta har suka samu suka kashe wasun su wasu kuma suka kama su,anan ne Barrister Lameer ya sanar dashi kan cewa ya bawa wasu yan mata ajiyar memory din.kiran ambulance sukayi aka dauki Barrister Lameer zuwa asibiti domin a bashi taimakon gaggawa.

Ashe wa'yanda yake nema tana tare dasu.

Idonsa a lumshe kamar me bacci ya furta, "bani memory card din!"
Mikewa Sabriyah ta yi, "ban yarda dakai ba,babu dalilin da zesa in baka wannan memory ko da kuwa kasheni zakayi"tana gama maganar ta fara tafiya,zata bar garden din.cizan libs din sa na kasa ya yi,ya ce "in dan kika bani,nikuma na yi miki alkawarin nemo miki yar uwarki a duk duniyar da take".

Cak ta dakata da tafiyar da takeyi jin ya ambaci ze nemo mata Asmita,da sauri ta juyo ta dawo inda yake zaune ta ce "ni kuma muddin ka nemo mini ita zan baka wannan memory card din".tana ga fadin hakan ta sa kanta ta wuce cikin gidan,ta barsa zaune a wajen murmushi ya yi.
kawai yana binta ne cikin ruwan sanyi ta ba shi,amma in ya gadama a yanzu ze ƙarbi memory a wajanta,domin duk wani motsin mutanen gidan nan yana sane dashi,amma ze barta ya ga iya gudun ruwanta.
"Find the other girl,and kill this bastards"abinda ya ce kenan sannan ya mike,a tare sojojin dake wajen suka sara mishi.barin garden din ya yi wasu daga cikin sojojin suka bi bayan sa.

Kallon wani soja major Marry ta yi, ta ce "Khalifa! hand me the gun"miko mata bindiga ya yi,.nan take tsoro ya dira akan fuskokin wa'yanda za'a kashen suka fara neman afuwa.

Ko ajikinta ta seta kansu ta ɗa na kunamar bindigar sannan ta sake shi akan goshin na farko nan take ya fadi awajen matacce,haka dayan ma ta harbeshi a goshi.

Bindigar da ta yi amfani dashi,bayi da ƙara hakan yasa mutanen gidan basu ji kar'ar ba, ficewa ta yi itama taname basu umarnin su kwashe gawan nasu a wajen.

Birkita dakin ta yi kamar wata mahaukaciya tana neman breziyar ta,amma bata gani ba hakan ya daga mata hankali sosai,wanda yasa ta fara zargin ko wani ya shigo ya dauke ne musamman inta tuna da yanda sukayi da LTG,leƙawa kasan gado ta yi nan ta gansa yashe awajen. ashe da ta fito daga wanka ne ta yi wurgi dashi kan gado se ya faɗa bayan gadon.

Da hanzari ta shige kasar gadon kamar wata bera,daukowa ta yi ya,ta na kokarin fitowa ta ji muryoyinsu a dakin suna "to ina kuma taje?"

Fitowa ta yi hannunta riƙe da breziyar nata ta gansu dan tsuke fuska ta yi,bata ce musu komai ba.

Kallonta sukayi suna mamakin ita kuma me yasa ta shiga ƙasan gado.Rameesa ta ce"Sabriyah me kikeyi a kasan gado kuma".
Ajiyar zuciya ta yi "breziya ta na dauko" "okay!dama zamuje shan ice cream ne mukace bari muzo muce ki shirya muje".

Yatsina fuska ta yi ta ce"ku je kawai bazan samu zuwa ba".
Chapter 34 · 0% Book details